ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, November 12, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Hakar Ma’adinai Ba Bisa Ka’ida Ba Na Barazana Ga Tsaro – AbdulRazak

by Khalid Idris Doya
1 year ago
Barazana

Gwamnan Jihar Kwara, AbdulRahman AbdulRazak, ya bukaci kwararrun masana tattalin arzikin kasa da su taimaka wajen lalubo hanyoyin da za a dakike hakar ma’adinai ba bisa ba da ke kara dagula lamuran tsaro a fadin kasar nan.

Gwamnan ya yi rokon ne a wajen bude babban taron kwararrun masana tattalin arzikin kasa karo na uku da ya gudana a dakin taron jami’ar Al-Hikmah da ke Ilorin, babban birnin jihar.

  • Ba Zan Goyi Bayan Ƙudirin Ƙarin Haraji Ga Talakawa Ba – Sanata Ndume
  • Sin Ta Zargi EU Da Bayar Da Kariyar Cinikayya Bayan Da Kungiyar Ta Kakaba Karin Haraji Kan Motoci Masu Aiki Da Lantarki Kirar Sin

AbdulRazak, wanda ya samu wakilcin kwamishinan ma’adinai da albarkatun kasa na jihar, Dakta Afees Abolore, ya misalta halin da ake ciki na yawaitar masu hakar ma’adinai ta barauniyar hanya da cewa akwai bukatar daukan matakin gaggawa.

ADVERTISEMENT

Kazalika, gwamnan ya nemi masanan da su yi amfani da taron wajen ganin sun bullo da tattauna yadda za a samu kyautata harkokin hakar ma’adinai da kuma shawo kan matsalolin da suke bangaren.

“Albarkatun kasa na kan gaba wajen farfado da tattalin arzikin kasa nan.”

LABARAI MASU NASABA

Bayan Ganawa Da Tinubu, COAS Ya Tabbatar Wa ‘Yan Nijeriya Samun Ingantaccen Tsaro

Za Mu Ci Gaba Da Tallafa Wa ’Yansanda Domin Inganta Ayyukan Su A Zamfara – Gwamna Lawal

AbdulRazak.Ya ce gwamnatin tarayya za ta iya sanya bangaren albarkatun kasa a matsayin hanya na gaba-gaba wajen samar da kudaden shiga da kuma samar wa matasa ayyukan yi, sai dai abun takaici masu hakar ma’adinai ta barauniyar hanyoyi sun mamaye sashin da kuma kara janyo barazanar tsaro.

Gwamnan ya ce, gwamnatin Kwara a shirye take wajen hada hannu da masu zuba jari a ciki da waje kan wannan bangaren da ma sauran bangarorin kyautata tattalin arziki. Ya kuma ce Kwara ta kasance jiha mai saukin hulda da masu zuba hannun jari a bangaren gudanar da kasuwanci.

Tun da farko, shugaban NSEG, Dakta AbdulRazak Garba, ya ce, lokacin ya yi da Nijeriya za ta maida wajen kula da albarkatun kasarsa da kyautata muhalli.

Garba, wanda ya ce bangaren albarkatun kasa na da gagarumar rawar takawa a cikin kasar nan, ya lura da cewa bangaren na bukatar jerin kalubale.

Ya jero wasu daga cikin kalubalen da suka hada da rikitattun tsarin mulki, gazawar ababen morewa, gibin kudi, bukatar daidaita cigaban fasaha da dai sauransu.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Coas
Manyan Labarai

Bayan Ganawa Da Tinubu, COAS Ya Tabbatar Wa ‘Yan Nijeriya Samun Ingantaccen Tsaro

November 11, 2025
Za Mu Ci Gaba Da Tallafa Wa ’Yansanda Domin Inganta Ayyukan Su A Zamfara – Gwamna Lawal
Labarai

Za Mu Ci Gaba Da Tallafa Wa ’Yansanda Domin Inganta Ayyukan Su A Zamfara – Gwamna Lawal

November 11, 2025
‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutum 3 A Nasarawa
Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutum 3 A Nasarawa

November 11, 2025
Next Post
Mutane Miliyan 33.1 Zasu Fuskanci Ƙarancin Abinci A Nijeriya A 2025

Mutane Miliyan 33.1 Zasu Fuskanci Ƙarancin Abinci A Nijeriya A 2025

LABARAI MASU NASABA

Coas

Bayan Ganawa Da Tinubu, COAS Ya Tabbatar Wa ‘Yan Nijeriya Samun Ingantaccen Tsaro

November 11, 2025
Sin: Amurka Ba Ta Sa Lura Ga Kare Hakkin Dan Adam

Sin: Amurka Ba Ta Sa Lura Ga Kare Hakkin Dan Adam

November 11, 2025
Bikin CIIE Ya Nuna Yadda Sin Ke Ba Da Jagora Kan Harkokin Bude Kofa

Bikin CIIE Ya Nuna Yadda Sin Ke Ba Da Jagora Kan Harkokin Bude Kofa

November 11, 2025
Za Mu Ci Gaba Da Tallafa Wa ’Yansanda Domin Inganta Ayyukan Su A Zamfara – Gwamna Lawal

Za Mu Ci Gaba Da Tallafa Wa ’Yansanda Domin Inganta Ayyukan Su A Zamfara – Gwamna Lawal

November 11, 2025
CIIE Ya Kasance Gadar Sada Tattalin Arzikin Kasar Sin Da Na Duniya

CIIE Ya Kasance Gadar Sada Tattalin Arzikin Kasar Sin Da Na Duniya

November 11, 2025
CMG Ya Gabatar Da Sabbin Manhajoji 10 Da Ya Kirkiro Don Watsa Gasar Wasannin Motsa Jiki Ta Kasar Sin Karo Na 15

CMG Ya Gabatar Da Sabbin Manhajoji 10 Da Ya Kirkiro Don Watsa Gasar Wasannin Motsa Jiki Ta Kasar Sin Karo Na 15

November 11, 2025
‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutum 3 A Nasarawa

‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutum 3 A Nasarawa

November 11, 2025
Cikin Wata Ɗaya, ‘Yansanda Sun Kama Mutane 200 Da Ake Zargi Da Laifuka A Katsina

Cikin Wata Ɗaya, ‘Yansanda Sun Kama Mutane 200 Da Ake Zargi Da Laifuka A Katsina

November 11, 2025
CIIE Ya Ba ‘Yan Kasuwar Afirka Damar Habaka Cinikinsu Da Sin 

CIIE Ya Ba ‘Yan Kasuwar Afirka Damar Habaka Cinikinsu Da Sin 

November 11, 2025
Me Sabon Tarihin Da Aka Kafa A Baje Kolin CIIE Ke Nunawa?

Me Sabon Tarihin Da Aka Kafa A Baje Kolin CIIE Ke Nunawa?

November 11, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.