ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Hakar Ma’adinai Ba Bisa Ka’ida Ba Na Barazana Ga Tsaro – AbdulRazak

by Khalid Idris Doya
2 years ago
Barazana

Gwamnan Jihar Kwara, AbdulRahman AbdulRazak, ya bukaci kwararrun masana tattalin arzikin kasa da su taimaka wajen lalubo hanyoyin da za a dakike hakar ma’adinai ba bisa ba da ke kara dagula lamuran tsaro a fadin kasar nan.

Gwamnan ya yi rokon ne a wajen bude babban taron kwararrun masana tattalin arzikin kasa karo na uku da ya gudana a dakin taron jami’ar Al-Hikmah da ke Ilorin, babban birnin jihar.

  • Ba Zan Goyi Bayan Ƙudirin Ƙarin Haraji Ga Talakawa Ba – Sanata Ndume
  • Sin Ta Zargi EU Da Bayar Da Kariyar Cinikayya Bayan Da Kungiyar Ta Kakaba Karin Haraji Kan Motoci Masu Aiki Da Lantarki Kirar Sin

AbdulRazak, wanda ya samu wakilcin kwamishinan ma’adinai da albarkatun kasa na jihar, Dakta Afees Abolore, ya misalta halin da ake ciki na yawaitar masu hakar ma’adinai ta barauniyar hanya da cewa akwai bukatar daukan matakin gaggawa.

ADVERTISEMENT

Kazalika, gwamnan ya nemi masanan da su yi amfani da taron wajen ganin sun bullo da tattauna yadda za a samu kyautata harkokin hakar ma’adinai da kuma shawo kan matsalolin da suke bangaren.

“Albarkatun kasa na kan gaba wajen farfado da tattalin arzikin kasa nan.”

LABARAI MASU NASABA

’Yan Takarar ADC A Arewa Maso Yamma Sun Yi Alƙawarin Biyan N110,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi

Na Sayar Da ’Ya’yana, Na Sace Wasu 19 – Wata Da Ake Zargi Da Safarar Yara

AbdulRazak.Ya ce gwamnatin tarayya za ta iya sanya bangaren albarkatun kasa a matsayin hanya na gaba-gaba wajen samar da kudaden shiga da kuma samar wa matasa ayyukan yi, sai dai abun takaici masu hakar ma’adinai ta barauniyar hanyoyi sun mamaye sashin da kuma kara janyo barazanar tsaro.

Gwamnan ya ce, gwamnatin Kwara a shirye take wajen hada hannu da masu zuba jari a ciki da waje kan wannan bangaren da ma sauran bangarorin kyautata tattalin arziki. Ya kuma ce Kwara ta kasance jiha mai saukin hulda da masu zuba hannun jari a bangaren gudanar da kasuwanci.

Tun da farko, shugaban NSEG, Dakta AbdulRazak Garba, ya ce, lokacin ya yi da Nijeriya za ta maida wajen kula da albarkatun kasarsa da kyautata muhalli.

Garba, wanda ya ce bangaren albarkatun kasa na da gagarumar rawar takawa a cikin kasar nan, ya lura da cewa bangaren na bukatar jerin kalubale.

Ya jero wasu daga cikin kalubalen da suka hada da rikitattun tsarin mulki, gazawar ababen morewa, gibin kudi, bukatar daidaita cigaban fasaha da dai sauransu.

Barazana
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Yaro Ya Harbe Kansa Har Lahira Bayan Mafarauci Ya Yi Sakaci Da Bindigarsa A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    An Kama Mutane 5 Da Sassan Jikin Ɗan’Adam Za Su Yi Tsafi A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Tsohon Mai Neman Takarar Gwamnan Bauchi, Bala Jibrin, Ya Fice Daga APC Kan Zargin Ɗoki-ɗora

MASU ALAKA

’Yan Takarar ADC A Arewa Maso Yamma Sun Yi Alƙawarin Biyan N110,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi
Manyan Labarai

’Yan Takarar ADC A Arewa Maso Yamma Sun Yi Alƙawarin Biyan N110,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi

September 9, 2026
Yadda Jami’an ‘Yansanda Suka Yi Garkuwa Da Wani Mazaunin Abuja, Sun Kwashe Fiye Da Naira Miliyan 20 A Asusunsa
Labarai

Na Sayar Da ’Ya’yana, Na Sace Wasu 19 – Wata Da Ake Zargi Da Safarar Yara

September 9, 2026
Iran Ta Musanta Ikirarin Trump Tare Da Zafafa Hare-hare Kan Isra’ila
Manyan Labarai

Hormuz: Iran Ta Kai Muggan Hare-hare Kan Sansanin Amurka A Jordan

September 9, 2026
Next Post
Mutane Miliyan 33.1 Zasu Fuskanci Ƙarancin Abinci A Nijeriya A 2025

Mutane Miliyan 33.1 Zasu Fuskanci Ƙarancin Abinci A Nijeriya A 2025

LABARAI MASU NASABA

Yaya Toure Na Dab Da Kafa Tarihi A Gasar Zakarun Turai

Yaya Toure Na Dab Da Kafa Tarihi A Gasar Zakarun Turai

September 9, 2026
’Yan Takarar ADC A Arewa Maso Yamma Sun Yi Alƙawarin Biyan N110,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi

’Yan Takarar ADC A Arewa Maso Yamma Sun Yi Alƙawarin Biyan N110,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi

September 9, 2026
Yadda Jami’an ‘Yansanda Suka Yi Garkuwa Da Wani Mazaunin Abuja, Sun Kwashe Fiye Da Naira Miliyan 20 A Asusunsa

Na Sayar Da ’Ya’yana, Na Sace Wasu 19 – Wata Da Ake Zargi Da Safarar Yara

September 9, 2026
Iran Ta Musanta Ikirarin Trump Tare Da Zafafa Hare-hare Kan Isra’ila

Hormuz: Iran Ta Kai Muggan Hare-hare Kan Sansanin Amurka A Jordan

September 9, 2026
ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

September 9, 2026
Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.