• English
  • Business News
Sunday, June 1, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Halittar Mata Na Canzawa Bayan Aure

by Amina Usman
2 years ago
in Nazari
0
Halittar Mata Na Canzawa Bayan Aure
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kamar yadda aka sani cewa kowace mace da irin kirar halittar da Ubangiji ya yi mata, amma tambayar a nan ita ce me ya sa mata ke murjewa su yi kiba bayan sun yi aure.

Wannan lamari ba bako ba ne ga dukkan al’ummar kasar Hausa. In muka duba za mu ga cewa da yawa daga cikin matan Nijeriya musammam yankin Arewa da zarar mace ta yi aure ba jimawa sai ka ga halittar jikinta ya fara sauyawa ta yi kiba ta murmure duk taya ni muni sun bace. A al’adance al’ummar kasar Hausa suna kallon wannan lamari a matsayin ci gaba ga mace saboda ana ganin cewar tana samun matukar kulawa a wurin mijinta.

  • Za Mu Tabbatar An Hukunta Masu Zaluntar Kananan Yara Da Mata – Kwamishina Rabi Salisu
  • Gwamna Dauda Lawal Ya Yi Wa Matar Da ‘Yan Bindiga Suka Raba Da Muhallinta Shatara Ta Arziki

Amma sai dai abin tambaya a nan shi ne kulawar miji ita ce babbar magana da ke sa jikin mace ya canza ko kuwa akwai wasu abubuwa?

Tabbas kulawar miji na janyo sauyi ga halittar mace amma hakan bai isa dalili daya da za a ce shi ne ke janyo wannan sauyi ba.

Ga kadan daga cikin dalilan da ke sa mace samun sauyin halitta a gidan miji;

Labarai Masu Nasaba

Masana Sun Bayyana Yadda Yakin Neman Zaben 2027 Ke Barazana Ga Harkokin Tafiyar Da Gwamnati

Shirin Fim Kan Cikar Nijeriya Shekaru 25 A Kan Turbar Dimokuradiyya: Tasiri Da Muhimmanci

Samin kwanciyar hankali

A lokacin da mace ta yi aure za a ga cewa akwai wata kwanciyar hankali na musamman da za ta fuskanta wanda duk inda ta je ba za ta same ta ba sai a gidan miji ire-iren wannan sauyi sun hada da amarci, soyayya, sannan kuma cima mai kyau, wadannan abubuwa suna da matukar tasiri a canjin halittar mace, cikin kankanin lokaci za a ga mace ta murmure ta murje.

Sabuwar Rayuwa da kuma samun ‘yancin kai

Bayan soyayya a aure akwai kuma wasu tarin nauyi da zai hau kan mace wanda hakan kansa ta fahimci cewar girma da kulawar wasu mutane ya hau kanta kamar su rainon ciki, haihuwa da kuma renon yaron da za ta haifa. Wannan sauyin da kwanciyar hankali suma suna kara taimaka wa mace wajen zama babbar mata. Sai a ga cikin kankanin lokaci mace ta murje ta yi jiki duk wasu jijiyoyi, kasusuwa, da kuma kwayar halittunta sun sami sauyi sun bude wanda hakan zai sa alamar kiba ta bayyana.

Rainon Ciki

Bayan hidimar aure akwai babbar hidima a gaban ma’aurata, wannan hidima ita ce daukar ciki. Haihuwa da aba ce mai matukar dadi da sa farin ciki kuma tana daga cikin abubuwa mafi sauki da ke kara wa mata budewar jiki ka ga sun yi kiba.

Daga lokacin da mace ta sami ciki to tabbas cin abincinta zai karu fiye da na da, za a ga idan a da tana cin karamin kwano to daga ta sami ciki sai ka ga abin ya canza, dole a nemo babban mazubi.

Mata yayin da suke da ciki suna matukar yin ciye-ciye sosai musamman abubuwa masu maiko wanda hakan ke sa jikin mace ya bude har ta yi jiki ta murmure.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

2034: Nijeriya Na Goyon Bayan Saudiyya Ta Dauki Nauyin Kofin Duniya

Next Post

Sin Za Ta Fadada Girman Tashar Binciken Samaniyarta

Related

haraji
Nazari

Masana Sun Bayyana Yadda Yakin Neman Zaben 2027 Ke Barazana Ga Harkokin Tafiyar Da Gwamnati

4 weeks ago
Mata
Nazari

Shirin Fim Kan Cikar Nijeriya Shekaru 25 A Kan Turbar Dimokuradiyya: Tasiri Da Muhimmanci

2 months ago
Asalin Tushen Matsalolinmu A Nijeriya
Nazari

Asalin Tushen Matsalolinmu A Nijeriya

8 months ago
Sinadarin Ƙara Kuzari Lokacin Jima’i
Nazari

Sinadarin Ƙara Kuzari Lokacin Jima’i

12 months ago
Mata
Labarai

Farashin Shinkafa, Tumatir Da Gari Ya Qaru Da Kashi 141 Cikin Shekara Guda – NBS

12 months ago
Kwarewar Sabon Shugaban Babban Bankin Nijeriya (CBN)
Nazari

Kwarewar Sabon Shugaban Babban Bankin Nijeriya (CBN)

2 years ago
Next Post
Sin

Sin Za Ta Fadada Girman Tashar Binciken Samaniyarta

LABARAI MASU NASABA

Binciken CGTN Ya Nuna Kaso Kusan 90 Bisa Dari Na Masu Bayyana Ra’ayoyi Na Kokawa Da Makomar “Mafarkin Amurka”

Binciken CGTN Ya Nuna Kaso Kusan 90 Bisa Dari Na Masu Bayyana Ra’ayoyi Na Kokawa Da Makomar “Mafarkin Amurka”

June 1, 2025
Gwamnatin Kano Ta Ba Da Hutun Makaranta Domin Bukukuwan Sallah

Gwamnatin Kano Ta Ba Da Hutun Makaranta Domin Bukukuwan Sallah

June 1, 2025
bakin wake

Bam Ya Kashe Mutane 9 A Wata Tashar Motoci Da Ke Borno 

June 1, 2025
‘Yan Wasan Da Tauraruwar Ronaldo Da Messi Ta Hana Su Haskawa

‘Yan Wasan Da Tauraruwar Ronaldo Da Messi Ta Hana Su Haskawa

June 1, 2025
NDLEA Ta Cafke Masu Tura Alhazai Saudiyya Domin Safarar Hodar Iblis Zuwa Kasar

NDLEA Ta Cafke Masu Tura Alhazai Saudiyya Domin Safarar Hodar Iblis Zuwa Kasar

June 1, 2025
SULEJA – An Ci Moriyar Ganga (3)

SULEJA – An Ci Moriyar Ganga (3)

June 1, 2025
Gwamnan kano

Gwamna Yusuf Ya Bada Hutu A Ranar Litinin Domin Addu’o’i Ga ‘Yan Wasan Kano 22

June 1, 2025
Gwamna Dikko Zai Sake Tsarin Babbar Kasuwar Jihar Katsina

Majalisar Dokokin Katsina Ta Ayyana Gwamna Radda A Matsayin Dan Takara Daya Tilo A 2027

June 1, 2025
An Karrama Dalibar Kaduna Da Ta Zo Ta Biyu A Gasar Karatun Alkur’ani Ta Duniya

An Karrama Dalibar Kaduna Da Ta Zo Ta Biyu A Gasar Karatun Alkur’ani Ta Duniya

June 1, 2025
Yadda Jarumai A Masana’antar Kannywood Ke Auren Junansu

Yadda Jarumai A Masana’antar Kannywood Ke Auren Junansu

June 1, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.