• English
  • Business News
Saturday, October 25, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Hanyar Gaskiya Ba Kaya

by CGTN Hausa and Sulaiman
10 months ago
Gaskiya

Paul Kagame, shugaban kasar Rwanda, ya yaba wa kasar Sin, a taron dandalin tattaunawa na Doha, da ya gudana a kasar Qatar, a farkon watan nan da muke ciki. Inda shugaban ya ce, tasowar kasar Sin a duniya dama ce mai kyau ga kasashe masu tasowa, ganin yadda hadin gwiwar da suke yi tare da Sin ke haifar da alfanu ga dukkan bangarori masu ruwa da tsaki.

Sai dai kafin na ga rubutaccen bayani na jawabin shugaban, na ga labari mai alaka da batun, da kafar watsa labarai ta VOA ta kasar Amurka ta gabatar. Inda a kan shafin yanar gizo na VOA, an rubuta maganar da shugaba Kagame ya fada, kana a dab da zancen, an sanya alamar sokewa mai launin ja, gami da rubuta cewa “Kuskure ne”. Sa’an nan a cikin bayanin da ta wallafa, VOA ta zargi shugaba Kagame da “murde gaskiya”, kana ta ambaci dimbin laifuka na wai “tarkon bashi”, da “kwace damar yin aiki na ‘yan Afirka”, da “keta hakkin dan Adam”, da dai sauransu, wadanda kafofin yada labaru na kasashen yamma su kan dora wa kasar Sin.

  • Noman Zamani: Jigawa Ta Rattaba Hannu Kan Yarjejeniya Da Kamfanin CAMCE A Birnin Beijing 
  • ‘Yan Bindiga Sun Ƙwace Kayan Abincin Kirsimeti A Kaduna

Amma a hakika, wani abu da VOA din ba ta ambata shi ne, yayin da shugaba Kagame ke jawabi a wajen wani taro a karkashin dandalin Doha, wani shugaba na daban daga nahiyar Afirka na tare da shi, wato shugaban kasar Namibia Nangolo Mbumba. Sa’an nan a cikin jawabinsa, shugaba Mbumba shi ma ya yi wa kasar Sin yabo, kan yadda ta yi kokarin tabbatar da amfanawa dukkan bangarori, yayin da take hadin kai da sauran kasashe. To, watakila a ganin VOA, wannan shugaba na Afirka shi ma yana “murde gaskiya”? Watakila VOA din za ta sanya karin wata alamar sokewa mai launin ja a shafinta na yanar gizo?

Sai dai wani rahoton da cibiyar nazarin manufofi ta kungiyar Asiya, dake birnin New York na kasar Amurka, ta gabatar a farkon watan nan, ya nuna cewa, kasar Sin tana samu karbuwa a tsakanin al’ummun kasashen Afirka, saboda a ganinsu kasar Sin ta samar da damammaki na raya tattalin arziki ga nahiyar Afirka. An ce ko a kasar Eswatini, wata kasar da ba ta kulla huldar diplomasiyya tare da Jamhuriyar Jama’ar kasar Sin ba tukuna, al’ummarta su ma suna amincewa da kasar Sin sosai, inda kaso 73% cikin jama’ar kasar ke ganin cewa, ayyuka masu alaka da tattalin arziki da kasar Sin ke aiwatarwa na haifar da tasiri mai yakini kan ci gaban tattalin arzikin kasarsu.

To, idan ka tambayi ra’ayina dangane da batun, zan ce, sam ban yi mamaki ba, kan goyon bayan da al’ummun kasashen Afirka ke nunawa kasar Sin. Saboda na san ka’idar tushe ta gwamnatin kasar Sin a fannin hulda da kasashen Afirka ita ce, nuna gaskiya, da kauna, da sahihanci, da samar da takamaiman alfanu ga jama’ar kasashen Afirka.

LABARAI MASU NASABA

Harkokin Ciniki Da Zuba Jari Tsakanin Sin Da Afirka Sun Samu Ci Gaba Mafi Girma a Shekaru 5 Da Suka Gabata

Sanarwar Bayan Taron Jks: Mene Ne Sirrin Kwarin Gwiwar Kasar Sin?

A ganina, bai kamata kafofin watsa labarai na kasashen yamma su wuce gona da iri a yunkurinsu na shafa wa kasar Sin kashin kaza ba, har ma sun dora wa shugaban wata kasa laifi, da sanya alamar sokewa mai launin ja a dab da maganarsa, cikin matukar fushi. Kana zan ba su karin magana guda 2 a matsayin abun tunasarwa, wato: “Hanyar gaskiya ba kaya.” Kana, “kowa ya yi karyar dare, gari ya waye.” (Bello Wang)

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Harkokin Ciniki Da Zuba Jari Tsakanin Sin Da Afirka Sun Samu Ci Gaba Mafi Girma a Shekaru 5 Da Suka Gabata
Ra'ayi Riga

Harkokin Ciniki Da Zuba Jari Tsakanin Sin Da Afirka Sun Samu Ci Gaba Mafi Girma a Shekaru 5 Da Suka Gabata

October 23, 2025
Sanarwar Bayan Taron Jks: Mene Ne Sirrin Kwarin Gwiwar Kasar Sin?
Ra'ayi Riga

Sanarwar Bayan Taron Jks: Mene Ne Sirrin Kwarin Gwiwar Kasar Sin?

October 23, 2025
Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar Biyar: Sirrin Kasar Sin Na Saurin Bunkasa
Ra'ayi Riga

Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar Biyar: Sirrin Kasar Sin Na Saurin Bunkasa

October 21, 2025
Next Post
Ganduje Ya Zargi Gwamna Yusuf Da Ɗaukar Nauyin Zanga-zanga A Kano

Sanata Barau Ya Roƙi Ganduje Ya Ƙwato Jihohin Da Suka Yi Wa Jam'iyyar APC Tutsu

LABARAI MASU NASABA

Kasar Sin Ta Nemi Amurka Ta Dakatar Da Hare-haren Shafin Intanet Kan Muhimman Kayayyakinta Nan Take

Kasar Sin Ta Nemi Amurka Ta Dakatar Da Hare-haren Shafin Intanet Kan Muhimman Kayayyakinta Nan Take

October 24, 2025
Ba Zan Kwatanta Matsayina Da Na Sarkin Bauchi Ba – Sabon Sarkin Duguri

Ba Zan Kwatanta Matsayina Da Na Sarkin Bauchi Ba – Sabon Sarkin Duguri

October 24, 2025
Gwamnatin Kaduna Ta Gano Ma’adanin Zinari Da Tagulla Da Za Su Haɓaka Tattalin Arziƙin Jihar

Gwamnatin Kaduna Ta Gano Ma’adanin Zinari Da Tagulla Da Za Su Haɓaka Tattalin Arziƙin Jihar

October 24, 2025
An Kebe Ranar 25 Ga Oktoba A Matsayin Ranar Tunawa Da Kawo Karshen Mulkin Mallakar Japan A Yankin Taiwan

An Kebe Ranar 25 Ga Oktoba A Matsayin Ranar Tunawa Da Kawo Karshen Mulkin Mallakar Japan A Yankin Taiwan

October 24, 2025

Gwamnatin Katsina Ta Ƙara Samar Da Dakarun Tsaro 200 Domin Maganace Ta’addanci

October 24, 2025
Sin Ta Saka Burikan Da Za Ta Cika A Shekaru 5 Masu Zuwa

Sin Ta Saka Burikan Da Za Ta Cika A Shekaru 5 Masu Zuwa

October 24, 2025
Jam’iyyar NNPP A Kaduna Ta Ƙaryata Batun Tsige Shugabanta

Jam’iyyar NNPP A Kaduna Ta Ƙaryata Batun Tsige Shugabanta

October 24, 2025
An Shirya Harba Kumbon Shenzhou-21 A Kwanan Nan

An Shirya Harba Kumbon Shenzhou-21 A Kwanan Nan

October 24, 2025
Shugaba Xi Ya Jagoranci Zaman Jin Ra’ayoyin Wadanda Ba ‘Yan JKS Ba Game Da Tsara Shirin Raya Kasa Karo Na 15 

Shugaba Xi Ya Jagoranci Zaman Jin Ra’ayoyin Wadanda Ba ‘Yan JKS Ba Game Da Tsara Shirin Raya Kasa Karo Na 15 

October 24, 2025
Gwamnan Bauchi Ya Tabbatar Wa Sarakuna Ba Zai Rage Musu Iko Ba A Shirinsa Na Ƙirƙirar Sabbin Masarautu

Gwamnan Bauchi Ya Naɗa Yayansa A Matsayin Sabon Sarkin Duguri

October 24, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.