• English
  • Business News
Saturday, September 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Hanyar Gaskiya Ba Kaya

by CGTN Hausa and Sulaiman
8 months ago
in Ra'ayi Riga
0
Hanyar Gaskiya Ba Kaya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Paul Kagame, shugaban kasar Rwanda, ya yaba wa kasar Sin, a taron dandalin tattaunawa na Doha, da ya gudana a kasar Qatar, a farkon watan nan da muke ciki. Inda shugaban ya ce, tasowar kasar Sin a duniya dama ce mai kyau ga kasashe masu tasowa, ganin yadda hadin gwiwar da suke yi tare da Sin ke haifar da alfanu ga dukkan bangarori masu ruwa da tsaki.

Sai dai kafin na ga rubutaccen bayani na jawabin shugaban, na ga labari mai alaka da batun, da kafar watsa labarai ta VOA ta kasar Amurka ta gabatar. Inda a kan shafin yanar gizo na VOA, an rubuta maganar da shugaba Kagame ya fada, kana a dab da zancen, an sanya alamar sokewa mai launin ja, gami da rubuta cewa “Kuskure ne”. Sa’an nan a cikin bayanin da ta wallafa, VOA ta zargi shugaba Kagame da “murde gaskiya”, kana ta ambaci dimbin laifuka na wai “tarkon bashi”, da “kwace damar yin aiki na ‘yan Afirka”, da “keta hakkin dan Adam”, da dai sauransu, wadanda kafofin yada labaru na kasashen yamma su kan dora wa kasar Sin.

  • Noman Zamani: Jigawa Ta Rattaba Hannu Kan Yarjejeniya Da Kamfanin CAMCE A Birnin Beijing 
  • ‘Yan Bindiga Sun Ƙwace Kayan Abincin Kirsimeti A Kaduna

Amma a hakika, wani abu da VOA din ba ta ambata shi ne, yayin da shugaba Kagame ke jawabi a wajen wani taro a karkashin dandalin Doha, wani shugaba na daban daga nahiyar Afirka na tare da shi, wato shugaban kasar Namibia Nangolo Mbumba. Sa’an nan a cikin jawabinsa, shugaba Mbumba shi ma ya yi wa kasar Sin yabo, kan yadda ta yi kokarin tabbatar da amfanawa dukkan bangarori, yayin da take hadin kai da sauran kasashe. To, watakila a ganin VOA, wannan shugaba na Afirka shi ma yana “murde gaskiya”? Watakila VOA din za ta sanya karin wata alamar sokewa mai launin ja a shafinta na yanar gizo?

Sai dai wani rahoton da cibiyar nazarin manufofi ta kungiyar Asiya, dake birnin New York na kasar Amurka, ta gabatar a farkon watan nan, ya nuna cewa, kasar Sin tana samu karbuwa a tsakanin al’ummun kasashen Afirka, saboda a ganinsu kasar Sin ta samar da damammaki na raya tattalin arziki ga nahiyar Afirka. An ce ko a kasar Eswatini, wata kasar da ba ta kulla huldar diplomasiyya tare da Jamhuriyar Jama’ar kasar Sin ba tukuna, al’ummarta su ma suna amincewa da kasar Sin sosai, inda kaso 73% cikin jama’ar kasar ke ganin cewa, ayyuka masu alaka da tattalin arziki da kasar Sin ke aiwatarwa na haifar da tasiri mai yakini kan ci gaban tattalin arzikin kasarsu.

To, idan ka tambayi ra’ayina dangane da batun, zan ce, sam ban yi mamaki ba, kan goyon bayan da al’ummun kasashen Afirka ke nunawa kasar Sin. Saboda na san ka’idar tushe ta gwamnatin kasar Sin a fannin hulda da kasashen Afirka ita ce, nuna gaskiya, da kauna, da sahihanci, da samar da takamaiman alfanu ga jama’ar kasashen Afirka.

Labarai Masu Nasaba

Ci Gaban Sojojin Sin Yana Hidimar Manufar Zaman Lafiya A Ko Da Yaushe

Kowa Ya Ci Zomo Ya Ci Gudu: Shekaru 80 Da Nasarar Sinawa A Kan Zalunci Da Danniyar Japanawa

A ganina, bai kamata kafofin watsa labarai na kasashen yamma su wuce gona da iri a yunkurinsu na shafa wa kasar Sin kashin kaza ba, har ma sun dora wa shugaban wata kasa laifi, da sanya alamar sokewa mai launin ja a dab da maganarsa, cikin matukar fushi. Kana zan ba su karin magana guda 2 a matsayin abun tunasarwa, wato: “Hanyar gaskiya ba kaya.” Kana, “kowa ya yi karyar dare, gari ya waye.” (Bello Wang)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Kotu Ta Umarci Ministan Shari’a Da DSS Su Gabatar Da Bodejo A Gabanta

Next Post

Sanata Barau Ya Roƙi Ganduje Ya Ƙwato Jihohin Da Suka Yi Wa Jam’iyyar APC Tutsu

Related

Ci Gaban Sojojin Sin Yana Hidimar Manufar Zaman Lafiya A Ko Da Yaushe
Ra'ayi Riga

Ci Gaban Sojojin Sin Yana Hidimar Manufar Zaman Lafiya A Ko Da Yaushe

17 hours ago
Kowa Ya Ci Zomo Ya Ci Gudu: Shekaru 80 Da Nasarar Sinawa A Kan Zalunci Da Danniyar Japanawa
Ra'ayi Riga

Kowa Ya Ci Zomo Ya Ci Gudu: Shekaru 80 Da Nasarar Sinawa A Kan Zalunci Da Danniyar Japanawa

19 hours ago
Kasar Sin Za Ta Ci Gaba Da Ba Da Gudummawarta Wajen Kiyaye Zaman Lafiya Da Ci Gaban Duniya 
Ra'ayi Riga

Kasar Sin Za Ta Ci Gaba Da Ba Da Gudummawarta Wajen Kiyaye Zaman Lafiya Da Ci Gaban Duniya 

2 days ago
Sin: Bin Tafarki Na Gaskiya
Ra'ayi Riga

Sin: Bin Tafarki Na Gaskiya

3 days ago
Kyakkyawan Fata Kan Nasarar Yaki Da Akidar Mulkin Danniya A Duniya
Ra'ayi Riga

Kyakkyawan Fata Kan Nasarar Yaki Da Akidar Mulkin Danniya A Duniya

4 days ago
Shawarar GGI: Faduwa Ta Zo Daidai Da Zama
Ra'ayi Riga

Shawarar GGI: Faduwa Ta Zo Daidai Da Zama

4 days ago
Next Post
Ganduje Ya Zargi Gwamna Yusuf Da Ɗaukar Nauyin Zanga-zanga A Kano

Sanata Barau Ya Roƙi Ganduje Ya Ƙwato Jihohin Da Suka Yi Wa Jam'iyyar APC Tutsu

LABARAI MASU NASABA

Tsohon Mataimakin Gwamnan Gombe Da Wasu jigogin PDP Sun Koma APC

Tsohon Mataimakin Gwamnan Gombe Da Wasu jigogin PDP Sun Koma APC

September 6, 2025

Ilimi Shi Ne Matakin Nasarar Rayuwar Duniya Da Lahira – Yerima Shettima

September 6, 2025
NUPENG Za Ta Fara Yajin Aiki, Dangote Na Shirin Shiga Harkar Sufurin Mai

NUPENG Za Ta Fara Yajin Aiki, Dangote Na Shirin Shiga Harkar Sufurin Mai

September 6, 2025
Maulidi: Gwamnan Zamfara Ya Taya Al’ummar Musulmi Murna, Ya Buƙaci A Dage Da Addu’o’in Samun Zaman Lafiya

Maulidi: Gwamnan Zamfara Ya Taya Al’ummar Musulmi Murna, Ya Buƙaci A Dage Da Addu’o’in Samun Zaman Lafiya

September 6, 2025
Sashen Cinikayyar Bayar Da Hidima Na Sin Ya Bunkasa Cikin Watanni Bakwai Na Farkon Shekarar Bana

Sashen Cinikayyar Bayar Da Hidima Na Sin Ya Bunkasa Cikin Watanni Bakwai Na Farkon Shekarar Bana

September 5, 2025
Kasar Sin Ta Yi Nasarar Harba Wani Sabon Tauraron Dan Adam

Kasar Sin Ta Yi Nasarar Harba Wani Sabon Tauraron Dan Adam

September 5, 2025
Jami’an Kasa Da Kasa Sun Yi Matukar Jinjinawa Jawabin Xi Jinping

Jami’an Kasa Da Kasa Sun Yi Matukar Jinjinawa Jawabin Xi Jinping

September 5, 2025
Za Mu Riƙe Wa Minista Tijjani Muƙaminsa Bayan Hamɓarar Da Tinubu A 2027 – El-Rufai 

Ana Ci Gaba Da Caccakar El-rufai Kan Kalamansa Game Da Tsaron Kasa

September 5, 2025
Kasar Sin Ta Kasance Muhimmin Karfi Dake Tabbatar Da Zaman Lafiya Da Ci Gaban Duniya

Kasar Sin Ta Kasance Muhimmin Karfi Dake Tabbatar Da Zaman Lafiya Da Ci Gaban Duniya

September 5, 2025
Yadda Al’ummar Da Ke Zaune Da ‘Yan Bindiga Ke Rayuwa A Zamfara

Duk Da Sulhu Da ‘Yan Bindiga Ana Ci Gaba Da Kai Hare-hare Wasu Yankunan Zamfara

September 5, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.