ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Hanyar Gaskiya Ba Kaya

by CGTN Hausa and Sulaiman
1 year ago
Gaskiya

Paul Kagame, shugaban kasar Rwanda, ya yaba wa kasar Sin, a taron dandalin tattaunawa na Doha, da ya gudana a kasar Qatar, a farkon watan nan da muke ciki. Inda shugaban ya ce, tasowar kasar Sin a duniya dama ce mai kyau ga kasashe masu tasowa, ganin yadda hadin gwiwar da suke yi tare da Sin ke haifar da alfanu ga dukkan bangarori masu ruwa da tsaki.

Sai dai kafin na ga rubutaccen bayani na jawabin shugaban, na ga labari mai alaka da batun, da kafar watsa labarai ta VOA ta kasar Amurka ta gabatar. Inda a kan shafin yanar gizo na VOA, an rubuta maganar da shugaba Kagame ya fada, kana a dab da zancen, an sanya alamar sokewa mai launin ja, gami da rubuta cewa “Kuskure ne”. Sa’an nan a cikin bayanin da ta wallafa, VOA ta zargi shugaba Kagame da “murde gaskiya”, kana ta ambaci dimbin laifuka na wai “tarkon bashi”, da “kwace damar yin aiki na ‘yan Afirka”, da “keta hakkin dan Adam”, da dai sauransu, wadanda kafofin yada labaru na kasashen yamma su kan dora wa kasar Sin.

  • Noman Zamani: Jigawa Ta Rattaba Hannu Kan Yarjejeniya Da Kamfanin CAMCE A Birnin Beijing 
  • ‘Yan Bindiga Sun Ƙwace Kayan Abincin Kirsimeti A Kaduna

Amma a hakika, wani abu da VOA din ba ta ambata shi ne, yayin da shugaba Kagame ke jawabi a wajen wani taro a karkashin dandalin Doha, wani shugaba na daban daga nahiyar Afirka na tare da shi, wato shugaban kasar Namibia Nangolo Mbumba. Sa’an nan a cikin jawabinsa, shugaba Mbumba shi ma ya yi wa kasar Sin yabo, kan yadda ta yi kokarin tabbatar da amfanawa dukkan bangarori, yayin da take hadin kai da sauran kasashe. To, watakila a ganin VOA, wannan shugaba na Afirka shi ma yana “murde gaskiya”? Watakila VOA din za ta sanya karin wata alamar sokewa mai launin ja a shafinta na yanar gizo?

ADVERTISEMENT

Sai dai wani rahoton da cibiyar nazarin manufofi ta kungiyar Asiya, dake birnin New York na kasar Amurka, ta gabatar a farkon watan nan, ya nuna cewa, kasar Sin tana samu karbuwa a tsakanin al’ummun kasashen Afirka, saboda a ganinsu kasar Sin ta samar da damammaki na raya tattalin arziki ga nahiyar Afirka. An ce ko a kasar Eswatini, wata kasar da ba ta kulla huldar diplomasiyya tare da Jamhuriyar Jama’ar kasar Sin ba tukuna, al’ummarta su ma suna amincewa da kasar Sin sosai, inda kaso 73% cikin jama’ar kasar ke ganin cewa, ayyuka masu alaka da tattalin arziki da kasar Sin ke aiwatarwa na haifar da tasiri mai yakini kan ci gaban tattalin arzikin kasarsu.

To, idan ka tambayi ra’ayina dangane da batun, zan ce, sam ban yi mamaki ba, kan goyon bayan da al’ummun kasashen Afirka ke nunawa kasar Sin. Saboda na san ka’idar tushe ta gwamnatin kasar Sin a fannin hulda da kasashen Afirka ita ce, nuna gaskiya, da kauna, da sahihanci, da samar da takamaiman alfanu ga jama’ar kasashen Afirka.

LABARAI MASU NASABA

Abokin Jibi Shi Ne Aboki

Rayukan Mutanen Kenya Na Da Muhimmanci Daidai Da Na ‘Yan Amurka

A ganina, bai kamata kafofin watsa labarai na kasashen yamma su wuce gona da iri a yunkurinsu na shafa wa kasar Sin kashin kaza ba, har ma sun dora wa shugaban wata kasa laifi, da sanya alamar sokewa mai launin ja a dab da maganarsa, cikin matukar fushi. Kana zan ba su karin magana guda 2 a matsayin abun tunasarwa, wato: “Hanyar gaskiya ba kaya.” Kana, “kowa ya yi karyar dare, gari ya waye.” (Bello Wang)

Gaskiya
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito
Gaskiya
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci
  • Sulaiman
    Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa
  • Sulaiman
    Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku
  • Sulaiman
    Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

MASU ALAKA

Abokin Jibi Shi Ne Aboki
Ra'ayi Riga

Abokin Jibi Shi Ne Aboki

June 3, 2026
Rayukan Mutanen Kenya Na Da Muhimmanci Daidai Da Na ‘Yan Amurka
Ra'ayi Riga

Rayukan Mutanen Kenya Na Da Muhimmanci Daidai Da Na ‘Yan Amurka

June 1, 2026
Nagartattun Manufofin Sin Suna Janyo Hankalin Kasashen Duniya
Ra'ayi Riga

Nagartattun Manufofin Sin Suna Janyo Hankalin Kasashen Duniya

May 29, 2026
Next Post
Ganduje Ya Zargi Gwamna Yusuf Da Ɗaukar Nauyin Zanga-zanga A Kano

Sanata Barau Ya Roƙi Ganduje Ya Ƙwato Jihohin Da Suka Yi Wa Jam'iyyar APC Tutsu

LABARAI MASU NASABA

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026
Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

June 4, 2026
Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

June 4, 2026
Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

June 4, 2026
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.