ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 26, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Hanyar Gaskiya Ba Kaya

by CGTN Hausa and Sulaiman
2 years ago
Gaskiya

Paul Kagame, shugaban kasar Rwanda, ya yaba wa kasar Sin, a taron dandalin tattaunawa na Doha, da ya gudana a kasar Qatar, a farkon watan nan da muke ciki. Inda shugaban ya ce, tasowar kasar Sin a duniya dama ce mai kyau ga kasashe masu tasowa, ganin yadda hadin gwiwar da suke yi tare da Sin ke haifar da alfanu ga dukkan bangarori masu ruwa da tsaki.

Sai dai kafin na ga rubutaccen bayani na jawabin shugaban, na ga labari mai alaka da batun, da kafar watsa labarai ta VOA ta kasar Amurka ta gabatar. Inda a kan shafin yanar gizo na VOA, an rubuta maganar da shugaba Kagame ya fada, kana a dab da zancen, an sanya alamar sokewa mai launin ja, gami da rubuta cewa “Kuskure ne”. Sa’an nan a cikin bayanin da ta wallafa, VOA ta zargi shugaba Kagame da “murde gaskiya”, kana ta ambaci dimbin laifuka na wai “tarkon bashi”, da “kwace damar yin aiki na ‘yan Afirka”, da “keta hakkin dan Adam”, da dai sauransu, wadanda kafofin yada labaru na kasashen yamma su kan dora wa kasar Sin.

  • Noman Zamani: Jigawa Ta Rattaba Hannu Kan Yarjejeniya Da Kamfanin CAMCE A Birnin Beijing 
  • ‘Yan Bindiga Sun Ƙwace Kayan Abincin Kirsimeti A Kaduna

Amma a hakika, wani abu da VOA din ba ta ambata shi ne, yayin da shugaba Kagame ke jawabi a wajen wani taro a karkashin dandalin Doha, wani shugaba na daban daga nahiyar Afirka na tare da shi, wato shugaban kasar Namibia Nangolo Mbumba. Sa’an nan a cikin jawabinsa, shugaba Mbumba shi ma ya yi wa kasar Sin yabo, kan yadda ta yi kokarin tabbatar da amfanawa dukkan bangarori, yayin da take hadin kai da sauran kasashe. To, watakila a ganin VOA, wannan shugaba na Afirka shi ma yana “murde gaskiya”? Watakila VOA din za ta sanya karin wata alamar sokewa mai launin ja a shafinta na yanar gizo?

ADVERTISEMENT

Sai dai wani rahoton da cibiyar nazarin manufofi ta kungiyar Asiya, dake birnin New York na kasar Amurka, ta gabatar a farkon watan nan, ya nuna cewa, kasar Sin tana samu karbuwa a tsakanin al’ummun kasashen Afirka, saboda a ganinsu kasar Sin ta samar da damammaki na raya tattalin arziki ga nahiyar Afirka. An ce ko a kasar Eswatini, wata kasar da ba ta kulla huldar diplomasiyya tare da Jamhuriyar Jama’ar kasar Sin ba tukuna, al’ummarta su ma suna amincewa da kasar Sin sosai, inda kaso 73% cikin jama’ar kasar ke ganin cewa, ayyuka masu alaka da tattalin arziki da kasar Sin ke aiwatarwa na haifar da tasiri mai yakini kan ci gaban tattalin arzikin kasarsu.

To, idan ka tambayi ra’ayina dangane da batun, zan ce, sam ban yi mamaki ba, kan goyon bayan da al’ummun kasashen Afirka ke nunawa kasar Sin. Saboda na san ka’idar tushe ta gwamnatin kasar Sin a fannin hulda da kasashen Afirka ita ce, nuna gaskiya, da kauna, da sahihanci, da samar da takamaiman alfanu ga jama’ar kasashen Afirka.

LABARAI MASU NASABA

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Sin Na Daukar hakikanan Matakan Gina Kyakkaywar Makomar Al’ummun Sin Da Afirka Ta Bai Daya

A ganina, bai kamata kafofin watsa labarai na kasashen yamma su wuce gona da iri a yunkurinsu na shafa wa kasar Sin kashin kaza ba, har ma sun dora wa shugaban wata kasa laifi, da sanya alamar sokewa mai launin ja a dab da maganarsa, cikin matukar fushi. Kana zan ba su karin magana guda 2 a matsayin abun tunasarwa, wato: “Hanyar gaskiya ba kaya.” Kana, “kowa ya yi karyar dare, gari ya waye.” (Bello Wang)

Gaskiya
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Tsohon Mataimakin Babban Sakataren MDD Ya Yaba Wa Dabarun Sin Kan Mulkin Kasa
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Ta Habaka Karfin Soja Ne Don Kare Ikon Mallakar Kasa Da Muradun Ci Gaba
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Ta Yi Allah Wadai Da Amfani Da Haraji Ba Bisa Ka’ida Ba Ta Fakewa Da Zargin “Kwadagon Tilas”
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Xi Ya Mika Jaje Kan Mummunar Girgizar Kasar Venezuela
Gaskiya
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Tsohon Mataimakin Babban Sakataren MDD Ya Yaba Wa Dabarun Sin Kan Mulkin Kasa
  • Sulaiman
    Gwamnatin Kaduna Ta Ƙaddamar Da Sabbin Matakan Dakile Haɗura A Titin Bypass
  • Sulaiman
    Sin Ta Habaka Karfin Soja Ne Don Kare Ikon Mallakar Kasa Da Muradun Ci Gaba
  • Sulaiman
    Sin Ta Yi Allah Wadai Da Amfani Da Haraji Ba Bisa Ka’ida Ba Ta Fakewa Da Zargin “Kwadagon Tilas”

MASU ALAKA

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
Ra'ayi Riga

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Sin Na Daukar hakikanan Matakan Gina Kyakkaywar Makomar Al’ummun Sin Da Afirka Ta Bai Daya
Ra'ayi Riga

Sin Na Daukar hakikanan Matakan Gina Kyakkaywar Makomar Al’ummun Sin Da Afirka Ta Bai Daya

June 19, 2026
A Yi Watsi Da Wannan “Mummunan Teburi”
Ra'ayi Riga

A Yi Watsi Da Wannan “Mummunan Teburi”

June 18, 2026
Next Post
Ganduje Ya Zargi Gwamna Yusuf Da Ɗaukar Nauyin Zanga-zanga A Kano

Sanata Barau Ya Roƙi Ganduje Ya Ƙwato Jihohin Da Suka Yi Wa Jam'iyyar APC Tutsu

LABARAI MASU NASABA

Tsohon Mataimakin Babban Sakataren MDD Ya Yaba Wa Dabarun Sin Kan Mulkin Kasa

Tsohon Mataimakin Babban Sakataren MDD Ya Yaba Wa Dabarun Sin Kan Mulkin Kasa

June 26, 2026
Gwamnatin Kaduna Ta Ƙaddamar Da Sabbin Matakan Dakile Haɗura A  Titin Bypass

Gwamnatin Kaduna Ta Ƙaddamar Da Sabbin Matakan Dakile Haɗura A Titin Bypass

June 26, 2026
Disu

IGP Disu Ya Hana Jami’an Ƴansanda Yin Amfani Da TikTok Da Instagram Da Sauransu

June 26, 2026
Sin Ta Habaka Karfin Soja Ne Don Kare Ikon Mallakar Kasa Da Muradun Ci Gaba

Sin Ta Habaka Karfin Soja Ne Don Kare Ikon Mallakar Kasa Da Muradun Ci Gaba

June 26, 2026
Gaskiya

Dalilin Gwamnatin Tarayya Na Fara Aikin Gina Mayankar Zamani A Garin Jos

June 26, 2026
Sin Ta Yi Allah Wadai Da Amfani Da Haraji Ba Bisa Ka’ida Ba Ta Fakewa Da Zargin “Kwadagon Tilas”

Sin Ta Yi Allah Wadai Da Amfani Da Haraji Ba Bisa Ka’ida Ba Ta Fakewa Da Zargin “Kwadagon Tilas”

June 26, 2026
NDC Ta Ce Za Ta Ɗaukaka Ƙara Kan Hukuncin Soke Rajistarta

NDC Ta Ce Za Ta Ɗaukaka Ƙara Kan Hukuncin Soke Rajistarta

June 26, 2026
An Fitar da Jadawalin Wasannin Zagayen Farko Na Gasar Carabao Cup ta 2026/2027

An Fitar da Jadawalin Wasannin Zagayen Farko Na Gasar Carabao Cup ta 2026/2027

June 26, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Kotu Ba Ta Da Hujjar Umartar INEC Ta Soke Rajistar Jam’iyyu —Uban Doman Lafiya

June 26, 2026
Xi Ya Mika Jaje Kan Mummunar Girgizar Kasar Venezuela

Xi Ya Mika Jaje Kan Mummunar Girgizar Kasar Venezuela

June 26, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.