• English
  • Business News
Friday, August 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Hanyoyin Kare Lafiya Lokacin Hunturu – Dakta Sufyan 

by Shehu Yahaya
2 years ago
in Labarai
0
Hanyoyin Kare Lafiya Lokacin Hunturu – Dakta Sufyan 
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Labarai Masu Nasaba

Ba Sulhu Ko Sassauci Ga Ƴan Bindiga A Zamfara – Gwamna Lawal Dare

NLC Ta Baiwa Gwamnati Kwanaki 7 Don Magance Badaƙalar Satar Kuɗin Ma’aikata

Lokacin huturu, lokacin ne da jiki da fatar mutane ke wahala matuka saboda kura da iskar da ake yawan fama da ita.

Kamar yadda aka sani hunturu kan fara ne a tsakanin watan Nuwamba zuwa Maris. A irin wannan lokaci fatar mutane kan rika yakunewa yana karkarcewa wasu ma har yankewa yake wato abin da ake kira da fasau a kafar mutane.

  • Yadda Rakiyar Gwamnan Kano Ga Tagwayen da ke Manne Da Juna Ta Dauki Hankalin Al’umma
  • Hukumar Alhazai Ta Jihar Kebbi Ta Samu Sabon Shugaba

Matsalolin da irin wannan canjin yanayin ke kawowa sun hada da bashewar leben baki, tsagewar kafafen hanci, mura da dai sauran su matsaloli da ke yi wa lafiyar jiki illa.

Masana harkar lafiya sun bayyana irin matakan da ya kamata mutane su bi domin rigakafi yayin shigowar hunturu, inda suka ba da shawarar a rika saka kaya masu nauyi kuma wadanda ke rufe jiki kaf da takalma da za su rufe kafafuwa domin kare mutum daga iska.

Sun ci gaba da cewa akwai bukatar mutane su rinka shafa man kade, domin shi man kade na da ingancin hana bushewar jiki.

Wakilinmu ya zanta da babban likitan asibitin Na Kowa da ke Marabar Jos a cikin karamar hukumar Igabi ta Jihar Kaduna, Dakta Sufyan Umar Yari ya bayyana cewa, “Abin da ya kamata a duba shi ne, wadanne irin cututtuka ne aka fi samu lokaci sanyi kan manyan mutane da kuma kananan yara. Idan muka lura yanayin yana canzawa, ya kan zo da kura da iska kuma yana iya zuwa da tsananin sanyi.

“Mafi akasari dai an fi samun cututtuka da suka fi alaka da huhu irin su cutar nimoniya da asma wacce ba cuta ba ce da ake dauka a tsakanin mutane, amma dai ta fi ta shi a lokacin sanyi, saboda abin da ke ta da ta shi ne iska ko kura ko kuma shan wani abu mai sanyi,” in ji shi.

Dakta Sufyan ya ci gaba da cewa cutar nimoniya ga kananan yara ta fi tashi lokacin hunturu. Likitan ya bukaci iyaye da su takaita zirga-zirgan ‘ya’yansu da safe da kuma kula da irin kayan da ake saka musu, idan ya zama dole su fita, sai a rika saka musu kayan sanyi.

Haka zalika, ya ce, “Akwai babban kuskure da mutane suke yi lokacin hunturu na kai wuta daki ko kuma rufe daki a hana iska shigawa. Irin wannan yana haifar da matsala, saboda maimakon a kare jiki da sanyi sai kuma wata cuta da shiga. Babu wata ka’ida da ta nuna cewa dole sai mutum ya rufe ko ina kafin ya kwanta barci.  Yana iya haifar da matsala musamma idan aka rufe ko ina kuma an kai wuta dakin domin shan dumin daki, to wannan abu yana haifar da matsaloli sosai.”

“Akwai magana ta wanka da ake yi wa yara a wannan lokacin hunturu, ya zama dole a rika neman dumaman ruwa ba ruwa tafasashshe ba, maimakon a yi wa yaro wanka sai a kona shi, wanda muna cin karo da irin wadannan matsaloli. Sai ka ga an kawo musu asibiti a galabaice wanda sai da kyara ake ceto rayuwarsu. An fi samun cututtuka irinsu nimoniya da bushewar makoshi da asma a lokacin hunturu, ” in ji shi.

Ya ce idan lokacin hunturu ya zo, suna bai wa mutane shawarar da rinka yawaita shan ruwa. A cewarsa, fatar Dan’adam tana aiki da ruwa, rashin yawaita shan ruwa yana haifar da tamukewar fata da bushewar makoshi.

Wasu magidanta a Jihar Kaduna sun bayyana irin hanyoyin da ya kamata a bi domin kare jiki da kamuwa daga wasu cututtukan lokacin hunturu.

 Muhammadu Abdullahi magidanci ne da ke zaune a unguwar Dosa a Kaduna, ya ce lokacin hunturu akwai bukatar mutane su rika yin wanka da ruwan dumi musamman da safe ko kuma da yamma.

Ya ce za a iya cin abincin da ke dauke da kitse, fiya, kifi domin suna dauke da sinadarin da ke gyara fatar mutum.

“Kamar ni ina tabbatar da cewa kamin yarana su tafi makaranta, sai an saka musu kayan sanyi da kuma ba su abinci mai dumi. Haka ni kaina da matata duk irin matakan da muke dauka kenan lokacin hunturu. Ka ga dai yau mun tashi babu rana sai iska da hazo, wanda ya zama dole a gare ni na samar wa kaina mafita wato zan sa yi gilashi na ido da talakli mai rufi da dai sauran,” in ji shi.

Wata matar aure, Fatima Ibrahim ta ce rashin ko-in-kula da wasu iyaye mata suke yi a kan yaransu yana haifar da lalurori da yawa kama daga kamuwa da mura da masassara wadanda cututtuka ne da suke hana yara sukuni.

Ta ce a matsayinta ta uwa tana daukar matakan sanya kayan sanyi ga yaranta yayin zuwa makaranta da kuma kiyaye irin abincin da suke ci.

Fatima ta shawarci gwamnatoci da su samar da magunguna, musamma ga yara a asibitoti wanda a lokaci hunturu yara kan iya shiga halin kunci fiye da manya.

Sai dai a wani bincike da wakilinmu ya gudanar a ma’aikatar kiwon lafiya ta Jihar Kaduna, ya gano cewa lokacin hunturu ko sanyi kwakwalwar Dan’adam za ta dunga sa tsokar jiki ta rinka motsawa da sauri-sauri, wanda ake kira rawar sanyi. Amfanin hakan shi ne, samar da zafi wanda zai dumama jiki saboda haka a duk sanda wata gaba ke aiki a jikin mutum, to zafi na samuwa ta ciki kamar yadda idan ka kunna na’urar za a samu zafi.

Binciken ya nuna cewa, wannan yawan motsawar tsoka a cikin sauri lokacin da mutum ke rawar sanyi ita ce hanyar da jiki ke samar wa kansa dumi, sannan kuma a kokarin jiki na kare shigar cututtuka ta hanyar iskar da muke shaka, ya sa majina ke fita daga hancinmu.

An gano cewa a cikin iska akwai datti da kura da cututtuka iri-iri, zarar mun shaki irin wannan iskar, kwayoyin halitta da ke bututun iska da makogwaro za su gane cewa ka shaki gurbatacciyar iska, nan da nan bututun iska wanda ya fara daga kofofin hanci zuwa cikin huhu, sai ya fara samar da majina.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Bashin Biliyan 500 Da Ganduje Ya Bari Ne Ya Hana Mu Fara Aiki Akan Lokaci – Abba

Next Post

CIIE: ‘Yan Kasuwan Kasa Da Kasa Na Alla-alla Wajen Yin Amfani Da Damar Ci Gaban Kasar Sin

Related

Ba Sulhu Ko Sassauci Ga Ƴan Bindiga A Zamfara – Gwamna Lawal Dare
Labarai

Ba Sulhu Ko Sassauci Ga Ƴan Bindiga A Zamfara – Gwamna Lawal Dare

4 hours ago
NLC Ta Baiwa Gwamnati Kwanaki 7 Don Magance Badaƙalar Satar Kuɗin Ma’aikata
Labarai

NLC Ta Baiwa Gwamnati Kwanaki 7 Don Magance Badaƙalar Satar Kuɗin Ma’aikata

5 hours ago
Zaɓen Cike Gurbi: Gwamnatin Kaduna Ta Yi Watsi Da Kalaman El-rufa’i Akan Zargin Maguɗin Zaɓe
Labarai

Zaɓen Cike Gurbi: Gwamnatin Kaduna Ta Yi Watsi Da Kalaman El-rufa’i Akan Zargin Maguɗin Zaɓe

6 hours ago
Gwamnati Na Ƙoƙarin Tsoratar Da Ni Don In Shiga APC – Sanata Tambuwal
Labarai

Gwamnati Na Ƙoƙarin Tsoratar Da Ni Don In Shiga APC – Sanata Tambuwal

7 hours ago
Gidauniya Ta Rabar Da Buhun Takin Zamani 6,000 Ga Manoma A Bauchi 
Labarai

Gidauniya Ta Rabar Da Buhun Takin Zamani 6,000 Ga Manoma A Bauchi 

8 hours ago
Sojojin Nijeriya Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 139, Sun Cafke 132 A Cikin Sati 2 —Hedikwatar Tsaro
Labarai

Sojoji Sun Kama Mutane 107 Da Ake Zargi, Sun Ceto Mutane 20 A Cikin Mako Guda – DHQ

9 hours ago
Next Post
CIIE: ‘Yan Kasuwan Kasa Da Kasa Na Alla-alla Wajen Yin Amfani Da Damar Ci Gaban Kasar Sin

CIIE: ‘Yan Kasuwan Kasa Da Kasa Na Alla-alla Wajen Yin Amfani Da Damar Ci Gaban Kasar Sin

LABARAI MASU NASABA

Ba Sulhu Ko Sassauci Ga Ƴan Bindiga A Zamfara – Gwamna Lawal Dare

Ba Sulhu Ko Sassauci Ga Ƴan Bindiga A Zamfara – Gwamna Lawal Dare

August 14, 2025
NLC Ta Baiwa Gwamnati Kwanaki 7 Don Magance Badaƙalar Satar Kuɗin Ma’aikata

NLC Ta Baiwa Gwamnati Kwanaki 7 Don Magance Badaƙalar Satar Kuɗin Ma’aikata

August 14, 2025
Sashen Aikewa Da Kunshin Sakwanni Na Sin Ya Bunkasa Cikin Watanni 7 Na Farkon Bana

Sashen Aikewa Da Kunshin Sakwanni Na Sin Ya Bunkasa Cikin Watanni 7 Na Farkon Bana

August 14, 2025
Zaɓen Cike Gurbi: Gwamnatin Kaduna Ta Yi Watsi Da Kalaman El-rufa’i Akan Zargin Maguɗin Zaɓe

Zaɓen Cike Gurbi: Gwamnatin Kaduna Ta Yi Watsi Da Kalaman El-rufa’i Akan Zargin Maguɗin Zaɓe

August 14, 2025
Salon Zamanantarwa Na Sin Kyakkyawan Misali Ne Ga Kasashen Afirka

Salon Zamanantarwa Na Sin Kyakkyawan Misali Ne Ga Kasashen Afirka

August 14, 2025
Gwamnati Na Ƙoƙarin Tsoratar Da Ni Don In Shiga APC – Sanata Tambuwal

Gwamnati Na Ƙoƙarin Tsoratar Da Ni Don In Shiga APC – Sanata Tambuwal

August 14, 2025
Tsarin Samar Da Kayayyaki Na Masana’antar Lantarki Ya Ci Gaba Da Samun Karfin Juriya A Kasar Sin

Tsarin Samar Da Kayayyaki Na Masana’antar Lantarki Ya Ci Gaba Da Samun Karfin Juriya A Kasar Sin

August 14, 2025
Gidauniya Ta Rabar Da Buhun Takin Zamani 6,000 Ga Manoma A Bauchi 

Gidauniya Ta Rabar Da Buhun Takin Zamani 6,000 Ga Manoma A Bauchi 

August 14, 2025
Sojojin Nijeriya Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 139, Sun Cafke 132 A Cikin Sati 2 —Hedikwatar Tsaro

Sojoji Sun Kama Mutane 107 Da Ake Zargi, Sun Ceto Mutane 20 A Cikin Mako Guda – DHQ

August 14, 2025
‘Yan Sama Jannatin Shenzhou-20 Za Su Gudanar Da Zagaye Na 3 Na Aiki A Wajen Cibiyar Binciken Sararin Samaniya Ta Sin

‘Yan Sama Jannatin Shenzhou-20 Za Su Gudanar Da Zagaye Na 3 Na Aiki A Wajen Cibiyar Binciken Sararin Samaniya Ta Sin

August 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.