• English
  • Business News
Wednesday, May 21, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Hanyoyin Rigakafin Cututtukan Da Ke Illata Amfanin Gona

by Abubakar Abba
9 months ago
in Noma Da Kiwo
0
Hanyoyin Rigakafin Cututtukan Da Ke Illata Amfanin Gona

An agriculture officer inspects maize plants damaged by fall armyworm in the Trans Mzoia region of Kenya, on Wednesday, May 24, 2017. A fall armyworm outbreak in Kenya has affected more than a government estimate of more than 100,000 hectares just weeks ago, according to Director of Crops in Agriculture Ministry Johnson Irungu. Photographer: Riccardo Gangale/Bloomberg via Getty Images

Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Biyo bayan samun wasu cututtukan da ke kara jawo raguwar samun girbi mai yawa a wannan nazari, an samar da wasu muhimman matakai guda hudu da manoma za su kare amfaninsu daga wannan bazarana.

Ana so manomi ya fahimci cutar: Bullar cutar da ke yi wa amfanin gona illa, ta kan sha banban daga shekara zuwa shekara; wanda kuma ake so manoma a koda-yaushe su rika kasancewa a ankare, don sanin wace sabuwar cuta ce za ta iya bulla.

  • Yawan Kudin Cinikin Samar Da Hidima Na Shigi Da Fici A Farkon Rabin Bana A Kasar Sin Ya Karu Da 14%

Misali, idan a kan ganyen Dawa ta bulla, ganyen zai koma tsanwa ko kuma alamar gansa-kuka.

Tsallake siradin cutar: Manoma za su iya tsallake wannan siradi ne ta hanyar lura da nau’in cutar da ka iya harbin jijiyar amfanin da suka shuka.

Misali, sauyin yanayi a fannin noman Dawa, zai iya jawo yaduwar cutar, saboda haka ba a so manomi ya yi sako-sako a dukkanin kakar noma koda kuwa, an samu ruwan sama mai yawa.

Labarai Masu Nasaba

Tinubu Ya Kira Taron Manyan Kafafen Yada Labarai Kan Samar Da Wadataccen Abinci

Gwamnatin Tarayya Ta Gabatar Da Wasu Shirye-shirye Na Bunƙasa Kiwon Shanu

Samun bullar wannan cuta, kan iya yi wa amfaninin manomi illa matukar bai mayar da hankali kan amfanin da ya shuka ba.

Shiga cikin filin gona a kan lokaci: Idan manoma suka shiga filin gonar da za su yi shuka a kan lokaci, hakan zai ba su damar daukar matakan gaggawa; ta hanyar sanin kowace irin cuta ce, da za ta yi wa amfaninsu illa tare da sanin wane irin magani ya fi dacewa su yi amfani da shi.

Ana kuma bukatar manomi ya tabbatar yana auna kimar amfanin da ya shuka, duba da cewa; cutar da ke lalata amfanin za ta iya bulla a wani yanayi na daban.

Haza zalika, fara bayyanar matsala a Jijiyar amfani na nuna alamar cewa, wata cuta ta bulla; misali jijiar za ta fara lalacewa.

Fahimtar mahimmanci yin amfani da maganin kashe cutar: Yana da kyau manomi ya fahimci muhimmancin amfanin da maganin da zai kashe cutar.

Magance cutar da ke bijere wa magani: Yana da matukar kyau, manomi ya tabbatar ya sa a zuciyarsa cewa; abu na farko da zai yi shi ne, magance cutar da ke bijere wa magani, musamman wajen samun damar daukar matakin gaggawa a kanta.

Don haka, ana so manomi ya rika amafani da magungunan kashe wannan cuta da ke da inganci, wanda hakan zai taimaka masa wajen magance irin wadannan cututtuka masu bijire wa magani.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Amfanin GonaNomaRigakafi
ShareTweetSendShare
Previous Post

Kasar Sin Ta Kira NED Dan Aike Na Gwamnatin Amurka

Next Post

Abubuwa Biyar Game Da Kiwon Talotalo

Related

Tinubu Ya Kira Taron Manyan Kafafen Yada Labarai Kan Samar Da Wadataccen Abinci
Noma Da Kiwo

Tinubu Ya Kira Taron Manyan Kafafen Yada Labarai Kan Samar Da Wadataccen Abinci

5 days ago
Gwamnatin Tarayya Ta Gabatar Da Wasu Shirye-shirye Na Bunƙasa Kiwon Shanu
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Tarayya Ta Gabatar Da Wasu Shirye-shirye Na Bunƙasa Kiwon Shanu

1 week ago
Nazari Kan Dabarun Taimaka Wa Masu Kiwon Kifi Domin Jurewa Sauyin Yanayi
Noma Da Kiwo

Nazari Kan Dabarun Taimaka Wa Masu Kiwon Kifi Domin Jurewa Sauyin Yanayi

2 weeks ago
Noman 2025: Dole Ne Manoma Su Kiyaye Hasashen Hukumar NiMet
Noma Da Kiwo

Noman 2025: Dole Ne Manoma Su Kiyaye Hasashen Hukumar NiMet

2 weeks ago
Masana Sun Bayyana Ingancin TELA Maize Ga Rayuwar Al’umma
Noma Da Kiwo

Masana Sun Bayyana Ingancin TELA Maize Ga Rayuwar Al’umma

2 weeks ago
Nazari Kan Dabarun Gargajiya Domin Jawo Hankalin Zuma
Noma Da Kiwo

Nazari Kan Dabarun Gargajiya Domin Jawo Hankalin Zuma

3 weeks ago
Next Post

Abubuwa Biyar Game Da Kiwon Talotalo

LABARAI MASU NASABA

Sara Da Sassaka Ba Ya Hana Gamji Toho

Sara Da Sassaka Ba Ya Hana Gamji Toho

May 21, 2025
Babu Wata Matar Da Aka Gurfanar Saboda Wai Ta Zama Kirista – Gwamnatin Zamfara

Babu Wata Matar Da Aka Gurfanar Saboda Wai Ta Zama Kirista – Gwamnatin Zamfara

May 21, 2025
Hajjin Bana: Jihar Filato Ta Ba Da Kyautar Kujera 500 Da Tallafin Miliyan 2 Ga Duk Maniyyaci

Hajji: NAHCON Ta Kammala Jigilar Kashi 77 Na Mahajjatan Nijeriya Zuwa Saudiyya 

May 21, 2025
Dan Sanda Ya Kashe Abokin Aikinsa Da Almakashi Har Lahira A Kebbi

‘Yansanda Sun Kama Matasa 2 Da Ake Zargi Da Satar Mota A Kebbi

May 21, 2025
Tattalin Arziƙin Nijeriya Na Ƙara Farfaɗowa – Gwamnan CBN

Tattalin Arziƙin Nijeriya Na Ƙara Farfaɗowa – Gwamnan CBN

May 21, 2025
Gwamnan Filato Ya Kafa Kwamiti Don Binciken Hare-Haren Da Ake Kai Wa A Jihar

Gwamnan Filato Ya Kafa Kwamiti Don Binciken Hare-Haren Da Ake Kai Wa A Jihar

May 21, 2025
Sarkin Yawa Ya Fi Sarkin Karfi

Sarkin Yawa Ya Fi Sarkin Karfi

May 21, 2025
Wani Mutum Ya Kashe Matarsa Da Duka Har Lahira A Edo

Wani Mutum Ya Kashe Matarsa Da Duka Har Lahira A Edo

May 21, 2025
Na Kwana A Marte Ne Don Ƙarfafa Gwiwar Jama’a Bayan Harin Boko Haram – Zulum

Na Kwana A Marte Ne Don Ƙarfafa Gwiwar Jama’a Bayan Harin Boko Haram – Zulum

May 21, 2025
Gwamnatin Kano Ta Hana Tallace-tallacen Magungunan Gargajiya A Fina-finai Da Kan Tituna

Gwamnatin Kano Ta Hana Tallace-tallacen Magungunan Gargajiya A Fina-finai Da Kan Tituna

May 20, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.