Dan takarar shugaban kasa a jam’iyyar APC, Asiwaju Bola Ahmed Tinubu, ya bayyana cewar har yanzu yana neman wanda zai yi masa takarar mataimaki a zaben 2023 da ke kara karatowa.
Tinubu, ya bayyana haka ne a ranar Lahadi a Abuja, a wurin bikin cikar kakakin majalisar wakilai, Femi Gbajabiamila, shekara 60 a duniya.
- An Gano Gawar Tsohon Jakadan Nijeriya Da Ya Bace A Amurka
- Da Alamun Daliban Kano Ba Zasu Rubuta NECO A Bana Ba Kan Bashin 1.5 Da Ake Bin Gwamnatin Kano
Tsohon gwamnan na Jihar Legas, ya jinjinawa kakakin kan yadda ya taimaka wajen ci gaban dimokuradiyya a Nijeriya.
Idan za a iya tunawa, Tinubu ya dauki Kabiru Ibrahim Masari daga Jihar Katsina a matsayin abokin takara na wucin gadi.
Sai dai hakan ya haifar da ciwon baki, ga masu sharhi akan harkokin siyasa da kuma al’muran yau da kullum.
A baya-bayan nan Kabiru Masari, ya bayyana cewar zai iya ajiye takarar mataimakin dan takarar shugaban kasa na APC, matukar aka samu wanda ya fi shi nagarta.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp