Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home MANYAN LABARAI

Har Yanzu Tattalin Arzikin Nijeriya Na Fuskantar Barazana –Amurka

by Tayo Adelaja
September 13, 2017
in MANYAN LABARAI
2 min read
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Daga Sulaiman Bala Idris

A ranar Juma’a 8 ga watan Satumba, 2017 ne kasar Amurka ta bayyana cewa har yanzun tattalin arzikin Nijeriya na fuskantar barazana, wanda ke da alaka da ayyukan tada kayar baya da ‘yan ta’addan Neja Delta ke yi, na tarwatsa bututun man fetur da ke yankin.

samndaads

Wannan gargadi na kasar Amurka ya fito ne daga bakin Shugaban Hafsan Sojin Ruwan Amurka, mai lura da yankunan Turai da Afrika, Admiral Michelle Howard. A yayin kuma da gargadin ya zo daidai lokacin da hukumar kididdiga ta kasa (NBS) ta fid da rahoton da ke cewa Nijeriya ta fice daga matsin tattalin arziki da karin 0.55.

Howard, ya bayyana haka ne a lokacin da yake mika lambar yabo ga mataimakin wakilin sojin Nijeriya a Amurka, Kaftin Kolawole Oguntuda, a babban hedikwatar Sojin Ruwa da ke Abuja.

“A irin wannan halin ne ake matukar bukatar aikin Sojin Ruwa. A matsayina na kwamanda, na dauki Sojin Ruwan Nijeriya a matsayin muhimmai kuma wadanda zasu iya taka muhimmiyar rawa wurin tabbatar da tsaro a yankin Afrika ta Yamma. Kuma zamu kara karfin alaka tsakanin rundunarmu da takwarorinmu na Afrika wurin wanzar da zaman lafiya.”

A yayin nasa jawabin, Shugaban Rundunar Sojin Ruwa ta Nijeriya, Mataimakin Admiral Ibok-Ete Ekwe Ibas ya bayar da tabbacin cewa Rundunar Sojin Ruwa ta Nijeriya a shirye suke domin fuskantar duk wata barazana da tsageran Neja Delta zasu yiwa Nijeriya.

“Ba sai wasu daga kasashen ketare sun fadi mana abin da ya kamace mu ba, ko yadda zamu magance duk wata barazana ko matsala da ke fuskantarmu da ma yankin Afrika ta Yamma.

“Tuni mun saba da ire-iren wadannan barazana da farmaki daga ‘yan fashi, da tsagera, musamman ma a shekarar bara. Haka kuma mun yi fama da barayin man fetur, da masu fasa bututu, har ma da masuntan da suke diban kifi a tekunmu ba tare da cika ka’ida ba.  Don haka barazanar da kake cewa Nijeriya na fuskanta daga yankin Neja Delta. Zan so in tabbatar maka da cewa matukar mutum na raye, dole ne ya cigaba da ganin irin wannan rikice – rikice, sannan akwai hanyoyin magance wadannan matsaloli.” In ji Ibas

SendShareTweetShare
Previous Post

Nnamdi Kanu: Gwamnati Ta Sanya dokar Ta-Baci A Abia

Next Post

Ganin Dala Ba Shiga Birni Ba: Yunkurin Rage Shekarun Yin Takara A Nijeriya

RelatedPosts

Bude Makarantu

Korona: Ba Ja Baya Ga Bude Makarantu – Gwamnatin Bauchi

by Muhammad
6 days ago
0

Daga Khalid Idris Doya, Ma’aikatar Ilimi ta Jihar Bauchi ta...

Harshen Hausa

Taron ‘Waiwaye Adon Tafiya’: Masana Sun Damu Bisa Nakasta Harshen Hausa

by Muhammad
7 days ago
0

Akwai Damuwa Kan Yadda Zamani Ke Tafiya Da Al’adun Bahaushe...

'Yan Kwaya

Zaben Kananan Hukumomin Kano: Yadda Aka Tono ’Yan Kwaya A ’Yan Takara

by Muhammad
1 week ago
0

Daga Abdullahi Muhammad Sheka, Shugaban hukumar zabe mai zaman kanta...

Next Post

Ganin Dala Ba Shiga Birni Ba: Yunkurin Rage Shekarun Yin Takara A Nijeriya

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

Leadership Epaper
ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version