• Leadership Hausa
Friday, August 12, 2022
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result
Home Labarai Kananan Labarai

Harin Kuje Da Tawagar Buhari: Ya Kamata A Sauya Shugabannin Tsaro – Alhaji Ibrahim

by yahuzajere
1 month ago
in Kananan Labarai
0
Harin Kuje Da Tawagar Buhari: Ya Kamata A Sauya Shugabannin Tsaro – Alhaji Ibrahim
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gamayyar Ƙungiyoyin Matasan Arewa Mazauna Kudancin Nijeriya ta yi kiran a sauya shugabannin rundunonin tsaro bisa mummunan harin da ‘yan ta’adda suka kai gidan gyara halinka na Kuje da kuma farmakin da aka kai wa tawagar hadiman Shugaba Buhari a kan hanyarsu ta zuwa Daura domin shirye-shiryen Babbar Sallah.

  • Harin Gidan Yarin Kuje: An Kwashe Sojoji Sa’o’i 24 Kafin Kai Harin

Shugaban gamayyar da ke Legas, Alhaji Ibrahim Ya’u Suleiman Galadanci ya ce harin na gidan gyara hakalinka da ya yi sanadiyyar ɓallewar fursunoni fiye da 600 babban bala’i ne da wasu maƙiya ƙasa ke son ganin yana aukuwa a Nijeriya.

 

“Lallai muna nuna takaicinmu a kan farmakin da aka kai wa tawagar shugaban ƙasa da kuma mummunan harin da aka kai gidan gyara halinka na Kuje da ya yi sanadin tserewar aƙalla fursunoni 600. Wannan al’amari ya sake caɓe yanayin rashin tsaron da ake fama da shi a arewa.

“Dan haka muna kira ga gwamnati da ta sauya shugabannin jami’an tsaro domin wannan lamarin ya kai intaha babu inda ake yi wa al’umma kisan gillah sama da Nijeriya kuma wannan abin shiryayye ne, abu ne wanda aka kasa shawo kansa. Mun daɗe muna yi wa shuganinmu bayanin cewa abubuwan da ke faruwa a arewa fa akwaifa lauje cikin naɗi, amma sun yi biris kamar ba a jikinsu ba,
“To amma idan kunne ya ji jiki ya tsira.” In ji shi.

Labarai Masu Nasaba

Labarin Asadulmuluuk (36)

Gwamnatin Gombe Ta Kafa Kwamitin Sayarwa Da Raba Takin Zamani Don Saukaka Wa Manoma 

Gamayyar matasan ta kuma ce yana daga matsalolin da suka hana shawo kan wannan rashin tsaro da ake fama, samun shugabanni nagari masu kishi, inda shugaban gamayyar ya ƙara da cewa, “A gaskiya ba mu da shugabanni nagari waɗanda za su yi kishin Nijeriya da kuma arewacin ƙasar gaba ɗaya, yanzu harin da aka kai wa tawagar shugaban ƙasa da ajali ya zo fa? Wannan babban abin kunya ne.To ya kamata mu tashi daga baccin da muke yi.”

  • https://leadership.ng/kuje-prison-attack-madalla-nyanya-bombers-62-terrorists-264-others-on-the-loose/

Gamayyar matasan ta kuma yi kira ga ‘yan ƙasa nagari masu kishi su ci gaba da addu’ar Allah ya tsare gaba kar a samu makamancin irin wannan harin na Kuje da sauran ayyukan ta’addancin da ake fama da su a Nijeriya.

ShareTweetSendShare
Previous Post

Sarkin Musulmi Ya Bukaci Yin Addu’o’i Na Musanman Don Magance Matsalar Tsaro

Next Post

Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ta Yabawa China Daily Saboda Bincike Tare Da Gabatar Da Bayanai Game Da Jita-jitar Da Wata Hukumar Birtaniya Ta Bayar Kan Batun Xinjiang

Related

Labarin Asadulmuluuk (36)
Kananan Labarai

Labarin Asadulmuluuk (36)

9 hours ago
Gwamnatin Gombe Ta Kafa Kwamitin Sayarwa Da Raba Takin Zamani Don Saukaka Wa Manoma 
Kananan Labarai

Gwamnatin Gombe Ta Kafa Kwamitin Sayarwa Da Raba Takin Zamani Don Saukaka Wa Manoma 

1 week ago
Hukumar Raya Birnin Tarayya Abaju Ta Rusa Garejin Kanikawa Da Ke Nyanya
Kananan Labarai

Kungiyar NARTO Ta Bayyana Damuwarta Kan Karancin Man Fetur A Abuja

1 week ago
Munazzamatu Fityanul Islam Reshen Abuja Ta Nesanta Kanta Da Wata Kungiya Mai Irin Sunanta
Kananan Labarai

Munazzamatu Fityanul Islam Reshen Abuja Ta Nesanta Kanta Da Wata Kungiya Mai Irin Sunanta

1 week ago
Ministar Jin Kai Ta Raba Wa Mata 3,500 Tallafin Kudi A Gombe
Kananan Labarai

Ministar Jin Kai Ta Raba Wa Mata 3,500 Tallafin Kudi A Gombe

1 week ago
Gwamnatin Gombe Za Ta Tallafa Wa Wadanda Ambaliyar Ruwa Ta Shafa A Funakaye
Kananan Labarai

Gwamnatin Gombe Za Ta Tallafa Wa Wadanda Ambaliyar Ruwa Ta Shafa A Funakaye

1 week ago
Next Post
Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ta Yabawa China Daily Saboda Bincike Tare Da Gabatar Da Bayanai Game Da Jita-jitar Da Wata Hukumar Birtaniya Ta Bayar Kan Batun Xinjiang

Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ta Yabawa China Daily Saboda Bincike Tare Da Gabatar Da Bayanai Game Da Jita-jitar Da Wata Hukumar Birtaniya Ta Bayar Kan Batun Xinjiang

LABARAI MASU NASABA

Shugaba Xi Ya Yi Kira Ga Sassan Kasa Da Kasa Da Su Yi Hadin Gwiwar Samar Da Ci Gaban Duniya

Shugaba Xi Ya Yi Kira Ga Sassan Kasa Da Kasa Da Su Yi Hadin Gwiwar Samar Da Ci Gaban Duniya

August 12, 2022
Zan Biya Wa ASUU Bukatunsu Idan Na Zama Shuagaban Kasa – Atiku

Zan Biya Wa ASUU Bukatunsu Idan Na Zama Shuagaban Kasa – Atiku

August 12, 2022
Hanyoyin Jiragen Kasa Da Sin Ta Gina Sun Zama Shaidar Raya Shirin “Ziri Daya Da Hanya Daya”

Hanyoyin Jiragen Kasa Da Sin Ta Gina Sun Zama Shaidar Raya Shirin “Ziri Daya Da Hanya Daya”

August 12, 2022
Yunkurin Amurka Kan Sana’ar Kera Sassan Na’urorin Laturoni Ba Zai Yi Nasara Ba

Yunkurin Amurka Kan Sana’ar Kera Sassan Na’urorin Laturoni Ba Zai Yi Nasara Ba

August 12, 2022
Hisbah Ta Jadadda Muhimmancin Gwajin Lafiya Kafin Aure 

Hisbah Ta Jadadda Muhimmancin Gwajin Lafiya Kafin Aure 

August 12, 2022
Shugaba Buhari Zai Kawo Karshen Rashin Tsaro A Nijeriya -Buratai

Shugaba Buhari Zai Kawo Karshen Rashin Tsaro A Nijeriya -Buratai

August 12, 2022
Gwamnatin Tarayya Ta Ware Biliyan 2.6 Domin Tsaron Abuja

Daga Asabar 8 Zuwa Talata 11 Ga Watan Muharram 1444

August 12, 2022
Akwai Alamun Ba Gudu Ba Ja Da Baya A Kan Batun Taiwan

Akwai Alamun Ba Gudu Ba Ja Da Baya A Kan Batun Taiwan

August 12, 2022
Rashin Shugabaci Nagari Ya Jefa Nijeriya Halin Da Take Ciki, In Ji SDP

Rashin Shugabaci Nagari Ya Jefa Nijeriya Halin Da Take Ciki, In Ji SDP

August 12, 2022
Yadda Mai Wanke-wanke Ta Zama Mataimakiyar Shugaban kasa

Yadda Mai Wanke-wanke Ta Zama Mataimakiyar Shugaban kasa

August 12, 2022
ADVERTISEMENT
Advertise with us

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.