• English
  • Business News
Sunday, May 11, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Hatsarin Jiragen Ruwa: Sakacin Hukumar Kula Da Hanyoyin Ruwa Ya Janyo Mutuwar Mutum 911

by Khalid Idris Doya
1 year ago
in Labarai
0
Hatsarin Jiragen Ruwa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Yawaitar hatsarin jiragen ruwa a fadin Kasar Nijeriya na da alaka da rashin bin dokoki tare da dibar kaya fiye da kima a jiragen ruwa da rashin yin amfani da rigunan kariya da rashin bin matakan kariya da rashin wadatattun kayan gyaran jiragen ruwa da kuma tafiye-tafiyen dare, hadi da kwasan fasinjoji fiye da karfin jirgin, kamar yadda binciken da jaridar LEADERSHIP ta tabbatar.

Kazalika, bayanan da LEADERSHIP ta samu daga sashin hakar ma’adinai na cewa, adadin mutum 911 da suka kunshi maza da mata da yara ne suka rasa rayukansu a hatsarin jiragen ruwa guda 61 da suka faru a tsakanin watan Junairun 2020 zuwa watan Nuwamban 2023.

  • Matatar Dangote Ta Karbi Danyen Man Farko Da Za Ta Fara Tacewa
  • Ya Kamata Kasashen Turai Su Kara Fahimtar Kasar Sin Don Karfafa Dangantakar Dake Tsakaninsu

Bayanan na nuni cewa, a tsawon shekaru shida da suka gabata, Nijeriya ta fuskaci hatsarin jiragen ruwa mafiya muni, inda rayukan mutum 1,204 suka salwatanta a tsakanin 2018 da Nuwamba 2023. A shekaru biyar da suka wuce, an samu rahotonnin afkuwar hatsarin kwale-kwale da rasa rayukan mutane da dama a jihohi 28 da ake iya bi ta hanyar ruwa a Nijeriya. Wadanda suka mutu sun hada da mata da yara, ko da yake an yi kokarin ceto wasu da dama a lokacin da suka gamu da hatsarin.

Rahotonni sun yi nuni da cewa a shekaru shida da suka gabata, sama da jihohi 12 ne aka samu rahotonnin mace-mace sakamakon hatsarin jiragen ruwa. Baya ga daruruwan mutanen da suka nutse suka baci a sakamakon hatsarin ruwa mafi muni da ake yawan samu a kasar nan.

A cewar rahoto, daga watan Janairun 2018 da Oktoba na 2023, an samu mutum 285 da suka mutu a Jihar Neja, Kebbi 144, Kwara 125, Sakkwato 117, Lagos 92, Anambra 80, Bauchi 76, Kano 45, Bayelsa 40, Taraba 50, Adamawa 60, sannan a Jihar Ondo da Benwai kuma aka samu mutum 34 da suka salwanta sakamakon wannan hatsarin.
A baya-bayan nan, an samu hatsarin kwale-kwale a karamar hukumar Shiroro ta Jihar Neja a ranar Juma’a 16 ga watan Nuwamban 2023 da ya ci rayukan mutum 10.

Labarai Masu Nasaba

Tsohon Dan Takarar Gwamna A NNPP A Jihar Ondo Ya Yi Murabus Daga Jam’iyyar

Shugaban NPA Ya Sha Yabo Kan Yadda Ya Bunƙasa Tashar Jiragen Ruwa Ta Onne

A cewar rahotonni, jirgin ya gamu da hatsari ne a gundumar Gijiwa/Kato da ke Shiroro bayan da ya tashi daga Zangaro/Bassa/Kukoki dauke da fasinja sama da mutum 34 da suka hada da maza 20, mata 14.
Bugu kuma da kari, a watan Oktoban 2023, a kalla ‘yan kasuwan kauye 70 ne suka nutse a cikin ruwa yayin da wani kwale-kwale ya kife da su a Jihar Taraba da ke arewa maso gabashin Nijeriya, kamar yadda jami’an hukumar agajin gaggawa suka shaida.

Kwale-kwalen da ya kwaso fasinjoji 100 da suka kunshi ‘yan kasuwa ciki har da yara, ya gamu da hatsari ne a gundumar Karim Lamido.

Shugaban shiyya na hukumar agajin gaggawa ta kasa NEMA, Ladan Ayuba, ya shaida cewa, “Ba a iya kirga mutum 73 ba daga cikin wadanda hatsarin ya rutsa da su, an iya samun ciro gangar jikin mutum 17 zuwa yanzu. Daga cikin fasinjojin jirgin 104, mutum 14 an samu nasarar ceto su.”
Kazalika, kakakin hukumar samar da agajin gaggawa ta Jihar Taraba (SEMA), Bryson Ben, ya nakalto cewa mutum 18 ne aka samu rahoton mutuwarsu a hatsarin.

Har ila yau, labarin dai mai sosa zuciya, inda aka samu wani hatsari a Gbajibo da ke karamar hukumar Mokwa a Jihar Neja, inda fasinjoji sama da 100 ciki har da wadanda suke kan hanyarsu ta zuwa gonakai suka gamu da hatsarin kwale-kwale, lamarin ya ci rayukan mutum 24.

Wannan bala’in bai tsaya nan ba, inda a baya-bayan nan a Jihar Adamawa 15 daga cikin fasinjoji 23 sun rasa rayukansu a Njuwa Lake da ke karamar hukumar Yola ta kudu.

A shekarar 2021 an fi samun tashe-tashen hankula sakamakon hatsarin jiragen ruwa, musamman a yankin arewacin kasar nan. A Jihar Kebbi an samu wani mummunar hatsarin jirgin ruwa a watan Yuni da ya lakume rayukan mutum sama da 100, mafi yawansu ‘yan kasuwa ne da suke kan hanyarsu ta zuwa kasuwanci a Jihar Kebbi yayin da kwale-kwalen ya kife da su.

Kuma an sake samu wasu mutum 20 da suka rasa rayukansu a wani hatsarin ruwa a kogin Yauri dukka a jihar. Wadannan hatsare-hatsaren na bukatar dauka matakan gaggawa domin kyautata matakan kariya a tsarin sufurin hanyoyin ruwa.

Tashin hankalin da bacin rai kan rasa rayuka da ake yi, na ci gaba da faruwa, an samu wani hatsarin a Jihar Kano da ya ci rayukan mutum 29 ciki har da yara ‘yan makaranta da suke kan hanyarsu domin zuwa wani taron addini. Kari kuma da wasu yara bakwai da suka gamu da irin wannan matakin a Jihar Jigawa lokacin da kwale-kwale ya kife da su, dukka an gano cewa babu matakan kariya da ake bi wajen kiyaye afkuwar hakan.

Iyalai sun shiga dimuwa a Jihar Neja yayin da rayuka bakwai suka salwanta ciki har da yara a wani hatsarin jirgin ruwan a Zhigiri a watan Disamba. A Jihar Bayelsa mutum takwas suka mutu yayin da suke tafiya a kwale-kwale daga Ogboinbiri zuwa Amassoma.

A Jihar Ondo ma, ba ta tsira daga wannan mummunar ibtila’in ba, inda hukumar tsaro ta NSCDC ta ba da labarin cewa mutum hudu sun rasa rayukansu yayin da kuma wasu 19 suka jikkata a hatsarin kwale-kwale a watan Oktoba.

A watan Mayun 2021, hatsarin kwale-kwale a tsakanin jihohin Kebbi da Neja an rasa rayuka 70, yayin da mutum sama da 150 suka yi batan dabo.

A watan Oktoban 2022 a karamar hukumar Ogbaru da ke Jihar Anambra lokacin da kwale-kwale ya nutse cikin ruwa, ya janyo mutuwar mutum 76 daga cikin fasinjoji 85 da suke cikin jirgin. Mafiya yawansu kuma mata da yara ne a lokacin da suke kokarin yin hijira daga garuruwansu sakamakon ambaliyar ruwa.

A watan Mayun 2023, hatsarin kwale-kwale ya wakana a wani kogi da ke Jihar Sakkwato inda ya ci rayukan yara 15, yayin da kuma 25 suka nutse ba a iya samu su ba. A wannan watan a jihar da ke makwafta da ita wato Zamfara, mutum takwas suka salwanta a hatsarin kwale-kwalen da ya faru a Gusau.

Tashin hankali da bugun zuci bai karewa kan lamarn, inda a watan Yunin 2023 sama da mutum 106 suka rasa rayukansu a hatsarin jirgin ruwa a Patigi da ke Jihar Kwara. Kari a kan dalibai uku da suka rasa rayukansu a Kalaba ta Jihar Kurus Ribas.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Hatsarin Jiragen RuwaNejaTaraba
ShareTweetSendShare
Previous Post

Tashin Bom A Kaduna: Yadda Na Tsallake Rijiya Da Baya – Dattijo Mai Shekara 74

Next Post

An Bukaci Gwamnatin Kaduna  Ta Samar Da Hukumar Zakka Da Wakafi

Related

Tsohon Dan Takarar Gwamna A NNPP A Jihar Ondo Ya Yi Murabus Daga Jam’iyyar
Manyan Labarai

Tsohon Dan Takarar Gwamna A NNPP A Jihar Ondo Ya Yi Murabus Daga Jam’iyyar

1 hour ago
Shugaban NPA Ya Sha Yabo Kan Yadda Ya Bunƙasa Tashar Jiragen Ruwa Ta Onne
Labarai

Shugaban NPA Ya Sha Yabo Kan Yadda Ya Bunƙasa Tashar Jiragen Ruwa Ta Onne

4 hours ago
Tarihin Sarkin Katsina Muhammadu Dikko (5)
Labarai

Tarihin Sarkin Katsina Muhammadu Dikko (5)

5 hours ago
Kaduna Ta Gano Ma’adanai 73, Yayin Da Take Neman Masu Zuba Jari
Labarai

Kaduna Ta Gano Ma’adanai 73, Yayin Da Take Neman Masu Zuba Jari

6 hours ago
Labarai

Kungiyar Malaman Jami’o’i Ta Ba Dalibai 164 Tallafin Karatu

18 hours ago
Dalilan Da Ke Nuna Malaman Makaranta Na Da Muhimmaci (5)
Labarai

Dalilan Da Ke Nuna Malaman Makaranta Na Da Muhimmaci (5)

19 hours ago
Next Post
Zakka

An Bukaci Gwamnatin Kaduna  Ta Samar Da Hukumar Zakka Da Wakafi

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Gabatar Da Wasu Shirye-shirye Na Bunƙasa Kiwon Shanu

Gwamnatin Tarayya Ta Gabatar Da Wasu Shirye-shirye Na Bunƙasa Kiwon Shanu

May 11, 2025
Tsohon Dan Takarar Gwamna A NNPP A Jihar Ondo Ya Yi Murabus Daga Jam’iyyar

Tsohon Dan Takarar Gwamna A NNPP A Jihar Ondo Ya Yi Murabus Daga Jam’iyyar

May 11, 2025
Rashin Hadin Kai Ke Dakile Ci Gaban Masana’antar Kannywood -Ayatullahi Tage

Rashin Hadin Kai Ke Dakile Ci Gaban Masana’antar Kannywood -Ayatullahi Tage

May 11, 2025
Barin Liverpool Ita Ce Shawara Mafi Wahala Da Na Taɓa Yankewa A Rayuwata -Alexander 

Barin Liverpool Ita Ce Shawara Mafi Wahala Da Na Taɓa Yankewa A Rayuwata -Alexander 

May 11, 2025
Shugaban NPA Ya Sha Yabo Kan Yadda Ya Bunƙasa Tashar Jiragen Ruwa Ta Onne

Shugaban NPA Ya Sha Yabo Kan Yadda Ya Bunƙasa Tashar Jiragen Ruwa Ta Onne

May 11, 2025
Tarihin Sarkin Katsina Muhammadu Dikko (5)

Tarihin Sarkin Katsina Muhammadu Dikko (5)

May 11, 2025
Kaduna Ta Gano Ma’adanai 73, Yayin Da Take Neman Masu Zuba Jari

Kaduna Ta Gano Ma’adanai 73, Yayin Da Take Neman Masu Zuba Jari

May 11, 2025
Tawagar Wanzar Da Zaman Lafiya Ta Farko Ta Sin Ta Dawo Daga Abyei Cikin Nasara

Tawagar Wanzar Da Zaman Lafiya Ta Farko Ta Sin Ta Dawo Daga Abyei Cikin Nasara

May 10, 2025
An Fara Taron Tattalin Arziki Da Cinikayya Na Matakin Koli Tsakanin Sin Da Amurka A Geneva

An Fara Taron Tattalin Arziki Da Cinikayya Na Matakin Koli Tsakanin Sin Da Amurka A Geneva

May 10, 2025
Sharhi: Sin Da Rasha Suna Sauke Nauyin Dake Wuyansu

Sharhi: Sin Da Rasha Suna Sauke Nauyin Dake Wuyansu

May 10, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.