ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, July 17, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Hatsarin Jiragen Ruwa: Sakacin Hukumar Kula Da Hanyoyin Ruwa Ya Janyo Mutuwar Mutum 911

by Khalid Idris Doya
3 years ago
Hatsarin Jiragen Ruwa

Yawaitar hatsarin jiragen ruwa a fadin Kasar Nijeriya na da alaka da rashin bin dokoki tare da dibar kaya fiye da kima a jiragen ruwa da rashin yin amfani da rigunan kariya da rashin bin matakan kariya da rashin wadatattun kayan gyaran jiragen ruwa da kuma tafiye-tafiyen dare, hadi da kwasan fasinjoji fiye da karfin jirgin, kamar yadda binciken da jaridar LEADERSHIP ta tabbatar.

Kazalika, bayanan da LEADERSHIP ta samu daga sashin hakar ma’adinai na cewa, adadin mutum 911 da suka kunshi maza da mata da yara ne suka rasa rayukansu a hatsarin jiragen ruwa guda 61 da suka faru a tsakanin watan Junairun 2020 zuwa watan Nuwamban 2023.

  • Matatar Dangote Ta Karbi Danyen Man Farko Da Za Ta Fara Tacewa
  • Ya Kamata Kasashen Turai Su Kara Fahimtar Kasar Sin Don Karfafa Dangantakar Dake Tsakaninsu

Bayanan na nuni cewa, a tsawon shekaru shida da suka gabata, Nijeriya ta fuskaci hatsarin jiragen ruwa mafiya muni, inda rayukan mutum 1,204 suka salwatanta a tsakanin 2018 da Nuwamba 2023. A shekaru biyar da suka wuce, an samu rahotonnin afkuwar hatsarin kwale-kwale da rasa rayukan mutane da dama a jihohi 28 da ake iya bi ta hanyar ruwa a Nijeriya. Wadanda suka mutu sun hada da mata da yara, ko da yake an yi kokarin ceto wasu da dama a lokacin da suka gamu da hatsarin.

ADVERTISEMENT

Rahotonni sun yi nuni da cewa a shekaru shida da suka gabata, sama da jihohi 12 ne aka samu rahotonnin mace-mace sakamakon hatsarin jiragen ruwa. Baya ga daruruwan mutanen da suka nutse suka baci a sakamakon hatsarin ruwa mafi muni da ake yawan samu a kasar nan.

A cewar rahoto, daga watan Janairun 2018 da Oktoba na 2023, an samu mutum 285 da suka mutu a Jihar Neja, Kebbi 144, Kwara 125, Sakkwato 117, Lagos 92, Anambra 80, Bauchi 76, Kano 45, Bayelsa 40, Taraba 50, Adamawa 60, sannan a Jihar Ondo da Benwai kuma aka samu mutum 34 da suka salwanta sakamakon wannan hatsarin.
A baya-bayan nan, an samu hatsarin kwale-kwale a karamar hukumar Shiroro ta Jihar Neja a ranar Juma’a 16 ga watan Nuwamban 2023 da ya ci rayukan mutum 10.

LABARAI MASU NASABA

Tinubu Ya Miƙa Wa Shettima Takardar Tabbatar Da Shi Abokin Takararsa A Zaɓen 2027

Mutfwang Ya Buƙaci Sojoji Su Ƙara Ƙaimi A Aikinsu

A cewar rahotonni, jirgin ya gamu da hatsari ne a gundumar Gijiwa/Kato da ke Shiroro bayan da ya tashi daga Zangaro/Bassa/Kukoki dauke da fasinja sama da mutum 34 da suka hada da maza 20, mata 14.
Bugu kuma da kari, a watan Oktoban 2023, a kalla ‘yan kasuwan kauye 70 ne suka nutse a cikin ruwa yayin da wani kwale-kwale ya kife da su a Jihar Taraba da ke arewa maso gabashin Nijeriya, kamar yadda jami’an hukumar agajin gaggawa suka shaida.

Kwale-kwalen da ya kwaso fasinjoji 100 da suka kunshi ‘yan kasuwa ciki har da yara, ya gamu da hatsari ne a gundumar Karim Lamido.

Shugaban shiyya na hukumar agajin gaggawa ta kasa NEMA, Ladan Ayuba, ya shaida cewa, “Ba a iya kirga mutum 73 ba daga cikin wadanda hatsarin ya rutsa da su, an iya samun ciro gangar jikin mutum 17 zuwa yanzu. Daga cikin fasinjojin jirgin 104, mutum 14 an samu nasarar ceto su.”
Kazalika, kakakin hukumar samar da agajin gaggawa ta Jihar Taraba (SEMA), Bryson Ben, ya nakalto cewa mutum 18 ne aka samu rahoton mutuwarsu a hatsarin.

Har ila yau, labarin dai mai sosa zuciya, inda aka samu wani hatsari a Gbajibo da ke karamar hukumar Mokwa a Jihar Neja, inda fasinjoji sama da 100 ciki har da wadanda suke kan hanyarsu ta zuwa gonakai suka gamu da hatsarin kwale-kwale, lamarin ya ci rayukan mutum 24.

Wannan bala’in bai tsaya nan ba, inda a baya-bayan nan a Jihar Adamawa 15 daga cikin fasinjoji 23 sun rasa rayukansu a Njuwa Lake da ke karamar hukumar Yola ta kudu.

A shekarar 2021 an fi samun tashe-tashen hankula sakamakon hatsarin jiragen ruwa, musamman a yankin arewacin kasar nan. A Jihar Kebbi an samu wani mummunar hatsarin jirgin ruwa a watan Yuni da ya lakume rayukan mutum sama da 100, mafi yawansu ‘yan kasuwa ne da suke kan hanyarsu ta zuwa kasuwanci a Jihar Kebbi yayin da kwale-kwalen ya kife da su.

Kuma an sake samu wasu mutum 20 da suka rasa rayukansu a wani hatsarin ruwa a kogin Yauri dukka a jihar. Wadannan hatsare-hatsaren na bukatar dauka matakan gaggawa domin kyautata matakan kariya a tsarin sufurin hanyoyin ruwa.

Tashin hankalin da bacin rai kan rasa rayuka da ake yi, na ci gaba da faruwa, an samu wani hatsarin a Jihar Kano da ya ci rayukan mutum 29 ciki har da yara ‘yan makaranta da suke kan hanyarsu domin zuwa wani taron addini. Kari kuma da wasu yara bakwai da suka gamu da irin wannan matakin a Jihar Jigawa lokacin da kwale-kwale ya kife da su, dukka an gano cewa babu matakan kariya da ake bi wajen kiyaye afkuwar hakan.

Iyalai sun shiga dimuwa a Jihar Neja yayin da rayuka bakwai suka salwanta ciki har da yara a wani hatsarin jirgin ruwan a Zhigiri a watan Disamba. A Jihar Bayelsa mutum takwas suka mutu yayin da suke tafiya a kwale-kwale daga Ogboinbiri zuwa Amassoma.

A Jihar Ondo ma, ba ta tsira daga wannan mummunar ibtila’in ba, inda hukumar tsaro ta NSCDC ta ba da labarin cewa mutum hudu sun rasa rayukansu yayin da kuma wasu 19 suka jikkata a hatsarin kwale-kwale a watan Oktoba.

A watan Mayun 2021, hatsarin kwale-kwale a tsakanin jihohin Kebbi da Neja an rasa rayuka 70, yayin da mutum sama da 150 suka yi batan dabo.

A watan Oktoban 2022 a karamar hukumar Ogbaru da ke Jihar Anambra lokacin da kwale-kwale ya nutse cikin ruwa, ya janyo mutuwar mutum 76 daga cikin fasinjoji 85 da suke cikin jirgin. Mafiya yawansu kuma mata da yara ne a lokacin da suke kokarin yin hijira daga garuruwansu sakamakon ambaliyar ruwa.

A watan Mayun 2023, hatsarin kwale-kwale ya wakana a wani kogi da ke Jihar Sakkwato inda ya ci rayukan yara 15, yayin da kuma 25 suka nutse ba a iya samu su ba. A wannan watan a jihar da ke makwafta da ita wato Zamfara, mutum takwas suka salwanta a hatsarin kwale-kwalen da ya faru a Gusau.

Tashin hankali da bugun zuci bai karewa kan lamarn, inda a watan Yunin 2023 sama da mutum 106 suka rasa rayukansu a hatsarin jirgin ruwa a Patigi da ke Jihar Kwara. Kari a kan dalibai uku da suka rasa rayukansu a Kalaba ta Jihar Kurus Ribas.

Hatsarin Jiragen Ruwa
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Gwamna Bala Ya Rushe Kwamitin Gudanarwar Wikki Tourists Bayan Rashin Nasararta A Gasar NPFL
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    M.A. Abubakar Ya Zaɓi Farouk Mustapha A Matsayin Mataimakinsa
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    ATBU Ta Janye Filin Ginin Masallaci Da Ta Bai wa TIMSAN, Ta Amince Kowa Ya Yi Addininsa Yadda Ya Fahimta
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ɗan Majalisar Dokokin Bauchi, Hon. Wanzam, Ya Rasu

MASU ALAKA

Tinubu Ya Miƙa Wa Shettima Takardar Tabbatar Da Shi Abokin Takararsa A Zaɓen 2027
Labarai

Tinubu Ya Miƙa Wa Shettima Takardar Tabbatar Da Shi Abokin Takararsa A Zaɓen 2027

July 16, 2026
Mutfwang Ya Buƙaci Sojoji Su Ƙara Ƙaimi A Aikinsu
Manyan Labarai

Mutfwang Ya Buƙaci Sojoji Su Ƙara Ƙaimi A Aikinsu

July 16, 2026
Gwamnatin Tarayya Na Biyan Tallafin Man Fetur A Asirce – El-Rufai
Siyasa

Ba Zan Iya Jure Halayen El-Rufai Ba Shi Yasa Na Fice Daga ADC – Salihu Lukman

July 16, 2026
Next Post
Zakka

An Bukaci Gwamnatin Kaduna  Ta Samar Da Hukumar Zakka Da Wakafi

LABARAI MASU NASABA

Pew: Sin Ta fi Amurka Samun Amincewar Al’ummun Duniya

Pew: Sin Ta fi Amurka Samun Amincewar Al’ummun Duniya

July 16, 2026
Sin Ta Fitar Da Tsarin Sanya Ido Don Inganta Muhalli Da Muhallin Halittu Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Fitar Da Tsarin Sanya Ido Don Inganta Muhalli Da Muhallin Halittu Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 16, 2026
Nazari Game Da Damammakin Da Sin Ta Samar Cikin Rahoton Ci Gaban Tattalin Arzikinta Na Rabin Farkon Shekara

Nazari Game Da Damammakin Da Sin Ta Samar Cikin Rahoton Ci Gaban Tattalin Arzikinta Na Rabin Farkon Shekara

July 16, 2026
Gwamna Bala Ya Rushe Kwamitin Gudanarwar Wikki Tourists Bayan Rashin Nasararta A Gasar NPFL

Gwamna Bala Ya Rushe Kwamitin Gudanarwar Wikki Tourists Bayan Rashin Nasararta A Gasar NPFL

July 16, 2026
Tasirin Da Sabbin Hare-haren Amurka Da Iran Za Su Iya Haifarwa Duniya

Tasirin Da Sabbin Hare-haren Amurka Da Iran Za Su Iya Haifarwa Duniya

July 16, 2026
Sin Na Kokarin Sanya Ci Gaban Fasaha Ya Inganta Bunkasa Da Wadatar Dan Adam

Sin Na Kokarin Sanya Ci Gaban Fasaha Ya Inganta Bunkasa Da Wadatar Dan Adam

July 16, 2026
Tinubu Ya Miƙa Wa Shettima Takardar Tabbatar Da Shi Abokin Takararsa A Zaɓen 2027

Tinubu Ya Miƙa Wa Shettima Takardar Tabbatar Da Shi Abokin Takararsa A Zaɓen 2027

July 16, 2026
Xi Jinping Ya Gana Da Shugaban Kazakhstan

Xi Jinping Ya Gana Da Shugaban Kazakhstan

July 16, 2026
Mutfwang Ya Buƙaci Sojoji Su Ƙara Ƙaimi A Aikinsu

Mutfwang Ya Buƙaci Sojoji Su Ƙara Ƙaimi A Aikinsu

July 16, 2026
An Yi Bikin Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Kafa Kungiyar Hadin Gwiwar Fasahar AI Ta Duniya A Shanghai

An Yi Bikin Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Kafa Kungiyar Hadin Gwiwar Fasahar AI Ta Duniya A Shanghai

July 16, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.