• English
  • Business News
Sunday, September 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Hidimar Da Daular Sakkwato Ke Yi Wajen Buga Miliyoyin Littafai – Sarkin Musulmi

by Sadiq
2 years ago
in Labarai
0
Hidimar Da Daular Sakkwato Ke Yi Wajen Buga Miliyoyin Littafai – Sarkin Musulmi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Labarai Masu Nasaba

DAPPMAN Ta Soki Matatar Dangote Kan Rage Farashin Man Fetur

Yadda Wani Ya Kashe Ƙaninsa, Ya Ɓoye Gawar A Duro

Sarkin Musulmi, Alhaji Muhammad Sa’ad Abubakar II, ya bayyana cewa akalla litattafai miliyan 3.2 daga ayyukan Malaman Addinin Musulunci 200 na Daular Usmaniyya ne aka gyara tare da buga su don rarraba su a fadin kasar nan.

Sarkin Musulmin ya bayyana hakan ne a lokacin da yake jawabi a wajen wani taro na kwanaki uku kan koyar da Addinin Musulunci a Afirka wanda ya gudana a dakin taro na Arewa House da ke Jihar Kaduna a ranar Talata.

  • An Kunna Wutar Gasar Wasannin Asiya Ta Hangzhou 2022
  • Gwamnan Gombe Ya Nada Njodi Sakataren Gwamnati, Misilli Daraktan Yada Labarai

Taron ya samu hadin gwiwar kungiyar hadin kan kasashen musulmi (OIC) da cibiyar bincike kan al’adun Musulunci da tarihin Musulunci (IRCICA) Turkiyya da kuma Al Istikama suka shirya.

Sultan Abubakar, ya ce an buga littattafan a cikin harsunan Ingilishi da Larabci da Hausa.

Ya bayyana cewa, baje kolin kayayyakin tarihi na Afirka zai taimaka wajen dawo da martabar ‘yan Afirka da kimarsu a nan gaba.

“Shugabannin Halifanci kadai sun yi rubuce-rubuce sama da 300 kan ayyukan diyar Shehu Usman Danfodio, Nana Asma’u da wasu dalibansa irin su AbdulKadir zul Mustapha.  Wadannan ayyuka sun shafi batutuwa da dama daga sanannun masana kimiyyar Musulunci na tafsirin Alkur’ani, ilimin zamantakewa, tattalin arziki, kimiyyar siyasa da likitanci.

“Ya zuwa yanzu mun gyara tare da buga littattafai sama da miliyan 3.2 na ayyuka 200 na wadannan manyan shugabanni kuma sun zagaya kasa da dakunan karatu na daidaikun mutane da makarantu a fadin duniya.

“Wadannan littafai an buga su cikin harshen Turanci da Larabci da Hausa ne kuma insha Allahu a karshen wannan taro zan kawo wasu daga cikin wadannan littattafai. Muna cikin zamanin da turawan mulkin mallaka suka boye wadannan ayyuka ta hanyar kin sanya su cikin tsarin karatun makarantun gwamnati don wasu manufofi nasu

“Amma mun kudiri aniyar fito da wadannan ayyuka na ilimi don sanya su cikin harsunan da za su ba da damar yin amfani da su. Ya kuma kamata taron ya taimaka wajen gano abubuwan da muka gada don ganin sun shiga duniya.”

Shugaban taron, Farfesan tarihi kuma tsohon mataimakin shugaban Jami’ar Jihar Adamawa, Farfesa Al Kasum Abba ya ce babu wani abu da ya wuce tallafin karatu domin babu wata kungiya da za a iya tafiyar da ita bisa jahilci.

“Abin farin ciki ne cewa wannan taro yana gudana ne kan ilimin Musulunci da karatu a Afirka.  Mutane ba su gane cewa tun kafin Turanci ya zo akwai ilimi a Musulunci.  Idan aka nutsa cikin tarihi, ilimin Musulunci a Afirka yana da matukar muhimmanci.

“Jihadin Sakkwato wani yunkuri ne na zamantakewa amma Turawan Ingila sun zo suka kira shi da jihadin Fulani saboda suna son kafa tasu daular. Ba ma yin karatu ba, amma muna tsara guraben karatu na Musulunci yadda ya kamata a tsara shi. Sarkin Musulmi da Shehun Borno ya kamata su taimaka wajen samar da kudade don nazarin jihadin karni na 19 domin ya dauki matakai daban-daban na jihadin Sakkwato da Borno.  Haka kuma muna bukatar kudi don fassara duk rubuce-rubucen karni na 19 domin mu fahimci tarihin al’ummarmu.”

Gwamna Uba Sani na Jihar Kaduna, wanda shi ne babban mai masaukin baki, ya ce taron ya zoa kan gaba kuma ya dace wajen bayyana irin gudunmawar da al’ummar Musulmi ke bayarwa ga ilimin duniya.

Gwamnan ya yi nuni da cewa, Daular Sakkwato na kan gaba wajen bayar da gudunmawar ilimi a Afrika. Ya ce Sheikh Usman Bin Fodio da dan uwansa Sheikh Abdullahi Fodio sun bayar da gudunmawa a fannonin jagoranci na dabi’a, ilimi, noma da kasuwanci.

Sani ya bayyana fatan taron zai samar da wani tsari na sake farfado da ilimin Addinin Musulunci domin ya dace da yanayin duniya wajen bai wa matasa dabarun rayuwa, tare da jaddada cewa yana da kyau a samar wa matasa sana’o’in da za su ba su damar yin takara a duniya da kuma bayar da gudunmawa mai ma’ana ga al’umma.

Taron dai ya samu halartar malaman Addinin Musulunci da masu bincike da masana daga sassa daban-daban na Afirka da ma duniya baki daya.

Daga cikin manyan baki sun hada da Shehun Borno, Alhaji Umar Garbai el-Kanemi, mataimakin gwamnan Jihar Kano, Alhaji Aminu Abdussalam Gwarzo, wanda ya wakilci gwamna Abba Kabir Yusuf.

Sauran sun hada da Dokta Usman Bugaje, babban daraktan IRCICA, Mahmud Erol Kilic, babban sakataren kungiyar OIC, Hissein Brahim Taha ya samu wakilcin daraktan kula da harkokin al’adu, mataimakin shugaban Jami’ar Ahmadu Bello da ke Zariya, ya samu wakilcin mataimakin shugaban hukumar, Farfesa Ibrahim Dogo.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: KadunaLitattafaiSarkin MusulmiTaro
ShareTweetSendShare
Previous Post

Mukaddashiyar Shugabar NIS Ta Ayyana Dokar Ta-baci Kan Ayyukan Fasfo

Next Post

GORON JUMA’A

Related

Dangote Ya Sake Zama Wanda Ya Fi Kowa Kudi A Afrika Karo Na 12
Manyan Labarai

DAPPMAN Ta Soki Matatar Dangote Kan Rage Farashin Man Fetur

5 hours ago
Yadda Wani Ya Kashe Ƙaninsa, Ya Ɓoye Gawar A Duro
Tsaro

Yadda Wani Ya Kashe Ƙaninsa, Ya Ɓoye Gawar A Duro

6 hours ago
An Kaddamar Da Tashar Watsa Labarai Ta CMG A Chengdu
Labarai

An Kaddamar Da Tashar Watsa Labarai Ta CMG A Chengdu

8 hours ago
An Tsinci Gawar Ɗalibar Jami’ar Taraba A Ɗakin Saurayinta
Manyan Labarai

An Tsinci Gawar Ɗalibar Jami’ar Taraba A Ɗakin Saurayinta

9 hours ago
Etsu Nupe Ginshiƙin Zaman Lafiya Da Haɗin Kai Ne A Nijeriya — Ministan Yaɗa Labarai
Labarai

Etsu Nupe Ginshiƙin Zaman Lafiya Da Haɗin Kai Ne A Nijeriya — Ministan Yaɗa Labarai

12 hours ago
Shugaban Rundunar Sojin Sama Ya Buƙaci Ɗaukar Matakin Yaƙi Da Barazanar Tsaro
Tsaro

Shugaban Rundunar Sojin Sama Ya Buƙaci Ɗaukar Matakin Yaƙi Da Barazanar Tsaro

12 hours ago
Next Post
GORON JUMA’A

GORON JUMA’A

LABARAI MASU NASABA

Dangote Ya Sake Zama Wanda Ya Fi Kowa Kudi A Afrika Karo Na 12

DAPPMAN Ta Soki Matatar Dangote Kan Rage Farashin Man Fetur

September 13, 2025
Yadda Wani Ya Kashe Ƙaninsa, Ya Ɓoye Gawar A Duro

Yadda Wani Ya Kashe Ƙaninsa, Ya Ɓoye Gawar A Duro

September 13, 2025
Madabba’ar Sin Ta Ba Da Gudunmuwar Littattafai Ga Makarantun Koyar Da Sinanci A Nijeriya

Madabba’ar Sin Ta Ba Da Gudunmuwar Littattafai Ga Makarantun Koyar Da Sinanci A Nijeriya

September 13, 2025
An Kaddamar Da Tashar Watsa Labarai Ta CMG A Chengdu

An Kaddamar Da Tashar Watsa Labarai Ta CMG A Chengdu

September 13, 2025
An Gudanar Da Dandalin Tattauna Al’adu Na Kasa Da Kasa Na Golden Panda Na 2025 A Birnin Chengdu

An Gudanar Da Dandalin Tattauna Al’adu Na Kasa Da Kasa Na Golden Panda Na 2025 A Birnin Chengdu

September 13, 2025
An Tsinci Gawar Ɗalibar Jami’ar Taraba A Ɗakin Saurayinta

An Tsinci Gawar Ɗalibar Jami’ar Taraba A Ɗakin Saurayinta

September 13, 2025
Kasar Sin Za Ta Kare Hakkin Kamfanoninta Ciki Har Da Tiktok

Kasar Sin Za Ta Kare Hakkin Kamfanoninta Ciki Har Da Tiktok

September 13, 2025
Aleksandar Vucic: Serbia Na Goyon Bayan Shawarar Kula Da Harkokin Duniya Da Kasar Sin Ta Gabatar

Aleksandar Vucic: Serbia Na Goyon Bayan Shawarar Kula Da Harkokin Duniya Da Kasar Sin Ta Gabatar

September 13, 2025
Etsu Nupe Ginshiƙin Zaman Lafiya Da Haɗin Kai Ne A Nijeriya — Ministan Yaɗa Labarai

Etsu Nupe Ginshiƙin Zaman Lafiya Da Haɗin Kai Ne A Nijeriya — Ministan Yaɗa Labarai

September 13, 2025
Shugaban Rundunar Sojin Sama Ya Buƙaci Ɗaukar Matakin Yaƙi Da Barazanar Tsaro

Shugaban Rundunar Sojin Sama Ya Buƙaci Ɗaukar Matakin Yaƙi Da Barazanar Tsaro

September 13, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.