• English
  • Business News
Sunday, June 29, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Hidimar Da Daular Sakkwato Ke Yi Wajen Buga Miliyoyin Littafai – Sarkin Musulmi

by Sadiq
2 years ago
in Labarai
0
Hidimar Da Daular Sakkwato Ke Yi Wajen Buga Miliyoyin Littafai – Sarkin Musulmi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Labarai Masu Nasaba

Za A Ci Gaba Da Tunawa Da Aminu Ɗantata A Ɓangaren Taimakon Jama’a — Buhari

Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

Sarkin Musulmi, Alhaji Muhammad Sa’ad Abubakar II, ya bayyana cewa akalla litattafai miliyan 3.2 daga ayyukan Malaman Addinin Musulunci 200 na Daular Usmaniyya ne aka gyara tare da buga su don rarraba su a fadin kasar nan.

Sarkin Musulmin ya bayyana hakan ne a lokacin da yake jawabi a wajen wani taro na kwanaki uku kan koyar da Addinin Musulunci a Afirka wanda ya gudana a dakin taro na Arewa House da ke Jihar Kaduna a ranar Talata.

  • An Kunna Wutar Gasar Wasannin Asiya Ta Hangzhou 2022
  • Gwamnan Gombe Ya Nada Njodi Sakataren Gwamnati, Misilli Daraktan Yada Labarai

Taron ya samu hadin gwiwar kungiyar hadin kan kasashen musulmi (OIC) da cibiyar bincike kan al’adun Musulunci da tarihin Musulunci (IRCICA) Turkiyya da kuma Al Istikama suka shirya.

Sultan Abubakar, ya ce an buga littattafan a cikin harsunan Ingilishi da Larabci da Hausa.

Ya bayyana cewa, baje kolin kayayyakin tarihi na Afirka zai taimaka wajen dawo da martabar ‘yan Afirka da kimarsu a nan gaba.

“Shugabannin Halifanci kadai sun yi rubuce-rubuce sama da 300 kan ayyukan diyar Shehu Usman Danfodio, Nana Asma’u da wasu dalibansa irin su AbdulKadir zul Mustapha.  Wadannan ayyuka sun shafi batutuwa da dama daga sanannun masana kimiyyar Musulunci na tafsirin Alkur’ani, ilimin zamantakewa, tattalin arziki, kimiyyar siyasa da likitanci.

“Ya zuwa yanzu mun gyara tare da buga littattafai sama da miliyan 3.2 na ayyuka 200 na wadannan manyan shugabanni kuma sun zagaya kasa da dakunan karatu na daidaikun mutane da makarantu a fadin duniya.

“Wadannan littafai an buga su cikin harshen Turanci da Larabci da Hausa ne kuma insha Allahu a karshen wannan taro zan kawo wasu daga cikin wadannan littattafai. Muna cikin zamanin da turawan mulkin mallaka suka boye wadannan ayyuka ta hanyar kin sanya su cikin tsarin karatun makarantun gwamnati don wasu manufofi nasu

“Amma mun kudiri aniyar fito da wadannan ayyuka na ilimi don sanya su cikin harsunan da za su ba da damar yin amfani da su. Ya kuma kamata taron ya taimaka wajen gano abubuwan da muka gada don ganin sun shiga duniya.”

Shugaban taron, Farfesan tarihi kuma tsohon mataimakin shugaban Jami’ar Jihar Adamawa, Farfesa Al Kasum Abba ya ce babu wani abu da ya wuce tallafin karatu domin babu wata kungiya da za a iya tafiyar da ita bisa jahilci.

“Abin farin ciki ne cewa wannan taro yana gudana ne kan ilimin Musulunci da karatu a Afirka.  Mutane ba su gane cewa tun kafin Turanci ya zo akwai ilimi a Musulunci.  Idan aka nutsa cikin tarihi, ilimin Musulunci a Afirka yana da matukar muhimmanci.

“Jihadin Sakkwato wani yunkuri ne na zamantakewa amma Turawan Ingila sun zo suka kira shi da jihadin Fulani saboda suna son kafa tasu daular. Ba ma yin karatu ba, amma muna tsara guraben karatu na Musulunci yadda ya kamata a tsara shi. Sarkin Musulmi da Shehun Borno ya kamata su taimaka wajen samar da kudade don nazarin jihadin karni na 19 domin ya dauki matakai daban-daban na jihadin Sakkwato da Borno.  Haka kuma muna bukatar kudi don fassara duk rubuce-rubucen karni na 19 domin mu fahimci tarihin al’ummarmu.”

Gwamna Uba Sani na Jihar Kaduna, wanda shi ne babban mai masaukin baki, ya ce taron ya zoa kan gaba kuma ya dace wajen bayyana irin gudunmawar da al’ummar Musulmi ke bayarwa ga ilimin duniya.

Gwamnan ya yi nuni da cewa, Daular Sakkwato na kan gaba wajen bayar da gudunmawar ilimi a Afrika. Ya ce Sheikh Usman Bin Fodio da dan uwansa Sheikh Abdullahi Fodio sun bayar da gudunmawa a fannonin jagoranci na dabi’a, ilimi, noma da kasuwanci.

Sani ya bayyana fatan taron zai samar da wani tsari na sake farfado da ilimin Addinin Musulunci domin ya dace da yanayin duniya wajen bai wa matasa dabarun rayuwa, tare da jaddada cewa yana da kyau a samar wa matasa sana’o’in da za su ba su damar yin takara a duniya da kuma bayar da gudunmawa mai ma’ana ga al’umma.

Taron dai ya samu halartar malaman Addinin Musulunci da masu bincike da masana daga sassa daban-daban na Afirka da ma duniya baki daya.

Daga cikin manyan baki sun hada da Shehun Borno, Alhaji Umar Garbai el-Kanemi, mataimakin gwamnan Jihar Kano, Alhaji Aminu Abdussalam Gwarzo, wanda ya wakilci gwamna Abba Kabir Yusuf.

Sauran sun hada da Dokta Usman Bugaje, babban daraktan IRCICA, Mahmud Erol Kilic, babban sakataren kungiyar OIC, Hissein Brahim Taha ya samu wakilcin daraktan kula da harkokin al’adu, mataimakin shugaban Jami’ar Ahmadu Bello da ke Zariya, ya samu wakilcin mataimakin shugaban hukumar, Farfesa Ibrahim Dogo.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: KadunaLitattafaiSarkin MusulmiTaro
ShareTweetSendShare
Previous Post

Mukaddashiyar Shugabar NIS Ta Ayyana Dokar Ta-baci Kan Ayyukan Fasfo

Next Post

GORON JUMA’A

Related

Bashin Da Ake Bin Nijeriya Ya Kai Tiriliyan 46.25
Labarai

Za A Ci Gaba Da Tunawa Da Aminu Ɗantata A Ɓangaren Taimakon Jama’a — Buhari

8 hours ago
Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa
Manyan Labarai

Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

8 hours ago
Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (3)
Labarai

Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (3)

9 hours ago
An Kai Wa Magoya Bayan Atiku Hari A Gombe
Manyan Labarai

Rasuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Afirka – Atiku

9 hours ago
Rasuwar Ɗantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya –  Shugaban ƘasaTinubu
Manyan Labarai

Rasuwar Ɗantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya –  Shugaban ƘasaTinubu

11 hours ago
Bam Ya Kashe Mutane 4, Ya Jikkata 21 A Yobe
Manyan Labarai

Bam Ya Kashe Mutane 4, Ya Jikkata 21 A Yobe

12 hours ago
Next Post
GORON JUMA’A

GORON JUMA’A

LABARAI MASU NASABA

Kasar Sin Ta Sake Ware Yuan Miliyan 100 Domin Tallafawa Lardin Guizhou Dake Fama Da Ambaliya 

Kasar Sin Ta Sake Ware Yuan Miliyan 100 Domin Tallafawa Lardin Guizhou Dake Fama Da Ambaliya 

June 28, 2025
An Kaddamar Da Aikin Hadin-Gwiwar Kafafen Yada Labaran Sin Da Kasashen Waje Wajen Watsa Labarai Game Da Jihar Xizang Ta Kasar Sin

An Kaddamar Da Aikin Hadin-Gwiwar Kafafen Yada Labaran Sin Da Kasashen Waje Wajen Watsa Labarai Game Da Jihar Xizang Ta Kasar Sin

June 28, 2025
Jakadun Kasa Da Kasa Sun Bayyana Muhimmancin Hadin Gwiwa Wajen Amfani Da Makamashin Nukiliya Ta Hanyar Lumana

Jakadun Kasa Da Kasa Sun Bayyana Muhimmancin Hadin Gwiwa Wajen Amfani Da Makamashin Nukiliya Ta Hanyar Lumana

June 28, 2025
Kokarin Zamanantar Da Sin Da Afrika Na Kara Karfafa

Kokarin Zamanantar Da Sin Da Afrika Na Kara Karfafa

June 28, 2025
Bashin Da Ake Bin Nijeriya Ya Kai Tiriliyan 46.25

Za A Ci Gaba Da Tunawa Da Aminu Ɗantata A Ɓangaren Taimakon Jama’a — Buhari

June 28, 2025
Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

June 28, 2025
Hukumar NPA Na Son Tara Kuɗaɗen Shiga Naira Tiriliyan 1.2 A 2025

Hukumar NPA Na Son Tara Kuɗaɗen Shiga Naira Tiriliyan 1.2 A 2025

June 28, 2025
An Horas Da Kwararrun Ma’aikata Sama Da Dubu 500 Karkashin Hadin Gwiwar Sin Da Sassan Kasa Da Kasa A Fannin Inganta Kwarewar Ma’aikata

An Horas Da Kwararrun Ma’aikata Sama Da Dubu 500 Karkashin Hadin Gwiwar Sin Da Sassan Kasa Da Kasa A Fannin Inganta Kwarewar Ma’aikata

June 28, 2025
Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (3)

Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (3)

June 28, 2025
An Kai Wa Magoya Bayan Atiku Hari A Gombe

Rasuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Afirka – Atiku

June 28, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.