• English
  • Business News
Thursday, September 18, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Hujjojin Obasanjo Na Cewa “Dimokuradiyyar Turawan Yamma Ba Ta Karbi Afirka Ba”

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
in Tambarin Dimokuradiyya
0
Hujjojin Obasanjo Na Cewa “Dimokuradiyyar Turawan Yamma Ba Ta Karbi Afirka Ba”
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Tsohon shugaban kasa, Olusegun Obasanjo ya jaddada cewa tsarin dimokuradiyyar Turawan yamma da kasashen Afirka suka kwaikwaya bai karbe su ba, inda ya bayar da hujjojinsa kan fadar haka.

Da farko Obasanjo ya ce dimokuradiyyar turawan ba ta dace da yanayin tarihi, al’adu da kabilun mutanen yammacin Afirka ba.

  • An Gudanar Da Bikin Reel Africa A Birnin Shanghai
  • Ya Zuwa Karshen Shekarar Bara Tsayin Manyan Titunan Mota Na Kasar Sin Ya Kai Kilomita 177,000

Haka nan, tsohon shugaban kasar ya bayyana cewa salon dimokuradiyyar kasashen yammacin duniya ya gaza a Nahiyar Afirka domin ba ta la’akari da ra’ayin mafi yawan jama’a.

Ya bayyana hakan ne a lokacin da yake gabatar da jawabin a wani babban taron tuntuba kan sake tunanin dimokuradiyyar Turawan yamma a Afirka, wanda ya gudana a Abeokuta, Babban Birnin Jihar Ogun.

Obasanjo, wanda ya kira taron, ya kuma siffanta dimokaradiyyar turawan na yamma a matsayin gwamnatin mutane kalilan da ke mulkan mutane masu dimbin yawa, kuma wadannan tsirarun mutane ne kawai wakilan wasu daga cikin jama’a, amma ba wakilan al’umma ba.

Labarai Masu Nasaba

Rudani Ya Kunno Kai Yayin Da INEC Ta Ki Amincewa Da Shugabancin ADC

‘Yan Nijeriya Suna Shan Wahala A Lokacin Da Gwamnatin Tinubu Ta Fi Damuwa Da Aljihunta – Sule Lamido

Ya ba da shawarar a sauya dimokuradiyyar Turawan yamma a kasashen Afirka.

A cewarsa, kasashen Afirka ba su da wata alaka wajen tafiyar da tsarin gwamnati wanda ba su da hannu a cikinsa.

Obasanjo ya ce, “Rauni da gazawar dimokuradiyyar Turawan yamma dai ya kunshi yadda ake aiwatar da ita ya saba da al’adun kasashen Afirka.

“Da zarar ka tashi wakiltar mutane, za ka fara fuskantar kalubale da matsaloli. Ga wadanda suka ayyanata a matsayin mulkin mafi rinjaye, shin ya kamata a yi watsi da tsiraru.?

“A takaice, muna da tsarin gwamnati wanda ba mu da hannun wajen tsarawa da kuma aiwatarwa, bai kamata mu ci gaba da amfani da shi ba, alhalin mun san ba ya mana aiki.

“Wadanda suka kawo mana shi a yanzu suna kokwanton sahihancinsa da suka kirkira, a yanzu kuma bai dace ba idan har ba za a gyara ba.

“Muhimmancin kowane tsarin gwamnati shi ne walwala da jin dadin al’ummar kasa.

“A nan, dole ne mu yi duba yanayin kwazon dimokuradiyyar Turawan yamma da suka gadar mana tun lokacin mulkin mallaka.

“Mun taro a nan ne don yin tunani a matsayinmu na jagororin ilimi da kuma na siyasa wajen fitar da matsaya kan dimokuradiyyar Turawan yamma.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Sharhi: Raunin Jam’iyyun Adawa Da Barazana Ga Dimokuradiyyar Nijeriya

Next Post

Duniya Na Bukatar Matasa Masu Ilimin Fasaha Domin Magance Tarin Matsaloli – Gwamnatin Tarayya

Related

Fursunoni Ba Za Su Samu Damar Kada Kuri’a Ba A Zaben 2023 – INEC
Tambarin Dimokuradiyya

Rudani Ya Kunno Kai Yayin Da INEC Ta Ki Amincewa Da Shugabancin ADC

2 weeks ago
‘Yan Nijeriya Suna Shan Wahala A Lokacin Da Gwamnatin Tinubu Ta Fi Damuwa Da Aljihunta – Sule Lamido
Tambarin Dimokuradiyya

‘Yan Nijeriya Suna Shan Wahala A Lokacin Da Gwamnatin Tinubu Ta Fi Damuwa Da Aljihunta – Sule Lamido

2 weeks ago
Daraktoci Da Jami’an FCT 7 Na Fuskantar Tuhume-tuhume Kan Badakar Fili
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Idan Kana Son Tarwatsa PDP, To Ka Dawo Da Peter Obi – Wike

2 weeks ago
ADC Ta Bukaci Tinubu Ya Kafa Dokar Ta Baci A Katsina Da Zamfara Kan Rashin Tsaro
Tambarin Dimokuradiyya

ADC Ta Bukaci Tinubu Ya Kafa Dokar Ta Baci A Katsina Da Zamfara Kan Rashin Tsaro

3 weeks ago
katin zabe
Tambarin Dimokuradiyya

INEC Ta Bayyana Damuwarta Kan Katunan Zabe 360,000 Da Ba A Karba Ba A Kano

3 weeks ago
Jam’iyyar PDP Ta Janye Daga Shiga Zaɓen Ƙananan Hukumomi A Kebbi
Tambarin Dimokuradiyya

Shugabannin PDP Sun Shiga Dimuwa Yayin Da APC Ke Zawarcin Wasu Gwamnoninsu

3 weeks ago
Next Post
Duniya Na Bukatar Matasa Masu Ilimin Fasaha Domin Magance Tarin Matsaloli – Gwamnatin Tarayya

Duniya Na Bukatar Matasa Masu Ilimin Fasaha Domin Magance Tarin Matsaloli – Gwamnatin Tarayya

LABARAI MASU NASABA

Kotun Sojin Nijeriya Ta Yanke Hukuncin Kisa Kan Wani Soja Da Ya Kashe Ɗan Adaidaita

Kotun Sojin Nijeriya Ta Yanke Hukuncin Kisa Kan Wani Soja Da Ya Kashe Ɗan Adaidaita

September 18, 2025
Sashen Raya Kimiyya Da Fasaha Na Sin Ya Kai Babban Matsayi Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar-biyar Karo Na 14

Sashen Raya Kimiyya Da Fasaha Na Sin Ya Kai Babban Matsayi Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar-biyar Karo Na 14

September 18, 2025
Jose Mourinho Ya Zama Sabon Kocin Benfica

Jose Mourinho Ya Zama Sabon Kocin Benfica

September 18, 2025
An Bude Taron Dandalin Tattauna Batun Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Birnin Beijing

An Bude Taron Dandalin Tattauna Batun Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Birnin Beijing

September 18, 2025
NNPP

Gwamna Yusuf Ya Nuna Jin Daɗinsa Kan Yadda Kano Ta Zarce Legas, Oyo A Sakamakon NECO Na 2025

September 18, 2025
Shugaban Guinea-Bissau Ya Goyi Bayan Shawarar Tsarin Shugabancin Duniya Da Sin Ta Gabatar

Shugaban Guinea-Bissau Ya Goyi Bayan Shawarar Tsarin Shugabancin Duniya Da Sin Ta Gabatar

September 18, 2025
An Damke Basarake Da Wasu Mutum 10 Bisa Zargin Hada Baki Da ‘Yan Bindiga A Kudancin Kaduna

Sojoji Sun Tarwatsa Wata Haramtacciyar Masana’antar Ƙera Makamai A Filato

September 18, 2025
Ci Gaban Tattalin Arzikin Sin Na Taimaka Ga Bunkasa Al’adunta Da Mu’amalar Al’adu Tsakaninta Da Kasashen Duniya

Ci Gaban Tattalin Arzikin Sin Na Taimaka Ga Bunkasa Al’adunta Da Mu’amalar Al’adu Tsakaninta Da Kasashen Duniya

September 18, 2025
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

’Yansanda Sun Kama Sojan Gona Da Motocin Sata 3 A Jigawa

September 18, 2025
Yadda Muka Zama Bayin ‘Yan Bindiga -Mazaunin Wani Kauye

’Yan Bindiga Sun Sako Ma’aurata A Katsina Bayan Karɓar N50m A Matsayin Kuɗin Fansa

September 18, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.