• English
  • Business News
Tuesday, October 28, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Hujjojin Obasanjo Na Cewa “Dimokuradiyyar Turawan Yamma Ba Ta Karbi Afirka Ba”

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
Obasanjo

Tsohon shugaban kasa, Olusegun Obasanjo ya jaddada cewa tsarin dimokuradiyyar Turawan yamma da kasashen Afirka suka kwaikwaya bai karbe su ba, inda ya bayar da hujjojinsa kan fadar haka.

Da farko Obasanjo ya ce dimokuradiyyar turawan ba ta dace da yanayin tarihi, al’adu da kabilun mutanen yammacin Afirka ba.

  • An Gudanar Da Bikin Reel Africa A Birnin Shanghai
  • Ya Zuwa Karshen Shekarar Bara Tsayin Manyan Titunan Mota Na Kasar Sin Ya Kai Kilomita 177,000

Haka nan, tsohon shugaban kasar ya bayyana cewa salon dimokuradiyyar kasashen yammacin duniya ya gaza a Nahiyar Afirka domin ba ta la’akari da ra’ayin mafi yawan jama’a.

Ya bayyana hakan ne a lokacin da yake gabatar da jawabin a wani babban taron tuntuba kan sake tunanin dimokuradiyyar Turawan yamma a Afirka, wanda ya gudana a Abeokuta, Babban Birnin Jihar Ogun.

Obasanjo, wanda ya kira taron, ya kuma siffanta dimokaradiyyar turawan na yamma a matsayin gwamnatin mutane kalilan da ke mulkan mutane masu dimbin yawa, kuma wadannan tsirarun mutane ne kawai wakilan wasu daga cikin jama’a, amma ba wakilan al’umma ba.

LABARAI MASU NASABA

Manyan Kalubalen Da Sabon Shugaban INEC Zai Fuskanta

2027: Peter Obi Ya Shiga Rudani Kan Jam’iyyar Da Zai Tsaya Takara

Ya ba da shawarar a sauya dimokuradiyyar Turawan yamma a kasashen Afirka.

A cewarsa, kasashen Afirka ba su da wata alaka wajen tafiyar da tsarin gwamnati wanda ba su da hannu a cikinsa.

Obasanjo ya ce, “Rauni da gazawar dimokuradiyyar Turawan yamma dai ya kunshi yadda ake aiwatar da ita ya saba da al’adun kasashen Afirka.

“Da zarar ka tashi wakiltar mutane, za ka fara fuskantar kalubale da matsaloli. Ga wadanda suka ayyanata a matsayin mulkin mafi rinjaye, shin ya kamata a yi watsi da tsiraru.?

“A takaice, muna da tsarin gwamnati wanda ba mu da hannun wajen tsarawa da kuma aiwatarwa, bai kamata mu ci gaba da amfani da shi ba, alhalin mun san ba ya mana aiki.

“Wadanda suka kawo mana shi a yanzu suna kokwanton sahihancinsa da suka kirkira, a yanzu kuma bai dace ba idan har ba za a gyara ba.

“Muhimmancin kowane tsarin gwamnati shi ne walwala da jin dadin al’ummar kasa.

“A nan, dole ne mu yi duba yanayin kwazon dimokuradiyyar Turawan yamma da suka gadar mana tun lokacin mulkin mallaka.

“Mun taro a nan ne don yin tunani a matsayinmu na jagororin ilimi da kuma na siyasa wajen fitar da matsaya kan dimokuradiyyar Turawan yamma.”

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Manyan Kalubalen Da Sabon Shugaban INEC Zai Fuskanta
Tambarin Dimokuradiyya

Manyan Kalubalen Da Sabon Shugaban INEC Zai Fuskanta

October 17, 2025
peter
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Peter Obi Ya Shiga Rudani Kan Jam’iyyar Da Zai Tsaya Takara

October 17, 2025
peter
Tambarin Dimokuradiyya

Peter Obi Ya Bukaci INEC Ta Tabbatar Da Shaidar Karatun Dan Takara Kafin Shiga Zabe

October 10, 2025
Next Post
Duniya Na Bukatar Matasa Masu Ilimin Fasaha Domin Magance Tarin Matsaloli – Gwamnatin Tarayya

Duniya Na Bukatar Matasa Masu Ilimin Fasaha Domin Magance Tarin Matsaloli – Gwamnatin Tarayya

LABARAI MASU NASABA

Kuri’un Jin Ra’ayin Jama’a Na CGTN Sun Nuna Gamsuwar Jama’a Ga Tsarin Jagoranci Na Sin

Kuri’un Jin Ra’ayin Jama’a Na CGTN Sun Nuna Gamsuwar Jama’a Ga Tsarin Jagoranci Na Sin

October 28, 2025
Kano Ta Bai Wa Mata 5,200 Tallafin Naira Miliyan 260

Kano Ta Bai Wa Mata 5,200 Tallafin Naira Miliyan 260

October 28, 2025
An Kusa Kammala Shirye-shiryen Baje Kolin CIIE Karo Na Takwas

An Kusa Kammala Shirye-shiryen Baje Kolin CIIE Karo Na Takwas

October 28, 2025
Gwamna Bago Ya Amince Da Biyan Karin Albashin Naira 20,000 Ga Ma’aikata 

Gwamnatin Neja Ta Bayar Da Hutun Kwanaki 2 Don Zaɓen Ƙananan Hukumomi

October 28, 2025
Fasahohin Sin Za Su Iya Kyautata Makomar Nahiyar Afrika

Fasahohin Sin Za Su Iya Kyautata Makomar Nahiyar Afrika

October 28, 2025
Xi Ya Yi Karin Haske Kan Muhimman Shawarwarin Da Kwamitin Kolin JKS Ya Gabatar Yayin Tsara Shirin Raya Kasa Karo Na 15

Xi Ya Yi Karin Haske Kan Muhimman Shawarwarin Da Kwamitin Kolin JKS Ya Gabatar Yayin Tsara Shirin Raya Kasa Karo Na 15

October 28, 2025
gaza

Majalisar Dattawa Ta Maido Da Ranar Tantance Sabbin Shugabannin Sojoji Zuwa Laraba

October 28, 2025
Duk Da Barazanar Tattalin Arzikin Duniya, Kasar Sin Ta Sanya Tabbaci Da Kwanciyar Hankali A Duniyarmu Mai Cike Da Ruɗani

Duk Da Barazanar Tattalin Arzikin Duniya, Kasar Sin Ta Sanya Tabbaci Da Kwanciyar Hankali A Duniyarmu Mai Cike Da Ruɗani

October 28, 2025
Ina Fatan Buga Kofin Duniya Na 2026 — Messi

Ina Fatan Buga Kofin Duniya Na 2026 — Messi

October 28, 2025
Tsohon Kwamishina Ya Zargi Gwamnatin Kano Da Sayar Da Filin Makaranta Kan Miliyan 100

Tsohon Kwamishina Ya Zargi Gwamnatin Kano Da Sayar Da Filin Makaranta Kan Miliyan 100

October 28, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.