• English
  • Business News
Wednesday, October 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Hukumar Aikin Hajji Ta Warware Sarkakiyar Karin Kudi Ga Maniyyata

byCMG Hausa
2 years ago
Aikin hajji

Hukumar aikin Hajji ta kasa ta kara jaddada kudurinta a kan samun nasarar aikin Hajji na shekarar 2023 da ya shafi tashin maniyata zuwa kasar Saudiyya ba tare da an fuskanci wata matsala ba.

Hukumar ta bada tabbacin hakan ne ranar Litinin da yamma lokacin da take mai da martani akan wani rahoton aikin Hajjin wannan shekara mai bayanin cewar kowane maniyyaci zai biya karin dala 100.

  • NAHCON Ta Nemi Alhazai Su Biya Kashi 40 Na Dala 250 Na Jigilarsu

Bayanin da mataimnakin darektan labarai da wallafe wallafe na hukumar Alhaji Mousa Ubandawaki,ya ce hukumar ba zata kasance daga cikin wani abin da zai sa a kara sa maniyata su shiga wani halin alakakai,domin bayan biyan karin dala $250 da masu kamfanonin jiragen sama suka bukata bayan an rufe sararin samaniyar kasar Sudan da taro da kamfanonin.Hukummin kula da tashohin jiragen sama da na al’amuran Hajji na Jihohi, sai hukumar taga yafi dacewa ta yi maganin matsalarda kanta.

“Hukumar ta nemi ta nemi taimakon gwamnatin tarayya data amince ta yafe masu saura kashi 35 na kudaden da za a ba kamfanonin jiragen saman wanda za su kai dala $55.Tsarin zai zama wani karin kudi ne da zai kasance ne akan maniyyatan Nijeriya.

Tun da farko gwamnatin tarayya ta yafe masu kashi 65 na kudaden da hukumar kula da jiragen sama ga maniyyata zuwa aikin Hajji.Idan aka yi la’akari da karin dala $250 da aka yi da kamfanonin jiragen sama za a rage su da dala $55.

LABARAI MASU NASABA

Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

Nijeriya A 65: ACF Da Afenifere Sun Yi Hannun Riga Kan Makomar Nijeriya

“Sauran dala $195 maniyyata 75,000 ne za su biya inda kowane maniyyaci zai biya dala $117.
“La’akari da aka yi biyan dala $117 na iya kasancewa karin wahala ga maniyyata, shi yasa hukumar ta yanke shawarar a rage kudin tafiyar na Hajjin 2023 daga dala 800 zuwa dala700 kamar yadda su maniyyatan suka biya dala 800.

“Maganar sauran dala $17 bugu da kari hukumar ta sake neman hadin kan kamfanonin jiragen sama su dauki al’amarin dala 17 a matsayin wata garabasa ce ga maniyyatan Nijeriya wadanda tuni al’amarin rufe sararin samaniyar Sudan ya shafe su.

“Saboda haka ne muke ta kara kira na cewa da zarar an kare takaddamar tashin hankali da ke faruwa a kasar Sudan idan aka samu damar kawo karshen ta, wanda zai sa a ci gaba da zurga- zurgar jiragen sama,hakan zai sa a sake maidawa mainiyyata wasu kudaden kamar yadda hukumar ta bayyana.

Wannan ya nuna ke nan:“Idan har ya kasance halin daake cikin Sudan ya sa ahar an rufe sararin samaniyarta saboda al’amarin daya shafi tsaro.

Irin hakan zai sa a samu wasu hanyoyin sararin samaniya da jiragen saman za su bi,ana iya samun karin awa daya da rabi ko kuma awa uku, wannan ya danganta ne daga wurin da jirgin zai tashi a Nijeriya.
Wannan sabuwar hanya ta sararin samaniya zai sa kamfanonin jiragen saman su bi ta sararin samaniyar kasashen.

Kamaru,jamhuriyyar Afirka ta tsakiya,Uganda, Kenya,Habasha da kuma Eriteriya, da karin kudin man jirgi, sai kuma karin kudin lokacin da aka yi ana tafiya.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce
Manyan Labarai

Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

October 4, 2025
Nijeriya A 65: ACF Da Afenifere Sun Yi Hannun Riga Kan Makomar Nijeriya
Rahotonni

Nijeriya A 65: ACF Da Afenifere Sun Yi Hannun Riga Kan Makomar Nijeriya

October 4, 2025
Bashin Karatun Dalibai: Arewa Maso Yamma Ce Kan Gaba Wajen Cin Gajiyar Shirin
Rahotonni

Bashin Karatun Dalibai: Arewa Maso Yamma Ce Kan Gaba Wajen Cin Gajiyar Shirin

October 3, 2025
Next Post
Kasar Sin Na Son Raba Gajiya Daga Bude Kofofin Ta Na Kasuwannin Gida Tare Da Kamfanonin Kasashe Daban-Daban

Kasar Sin Na Son Raba Gajiya Daga Bude Kofofin Ta Na Kasuwannin Gida Tare Da Kamfanonin Kasashe Daban-Daban

LABARAI MASU NASABA

ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

October 8, 2025
Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

October 8, 2025
Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

October 8, 2025
A Kama Wani Likitan Bogi A Neja

‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 153, Sun Ƙwato Miyagun Ƙwayoyi A Jihar Jigawa

October 8, 2025
An Fara Biyan Ma’aikata Sabon Mafi Ƙarancin Albashin N70,000 A Borno

‘Yansanda Da Mutanen Gari Sun Daƙile Harin Boko Haram A Borno

October 8, 2025
…ACF Ta Nesanta Kanta Da Goyon Bayan Akpabio

‘Yan Nijeriya Sama Da Miliyan 33 Ne Ke Fama Da Matsananciyar Yunwa – Akpabio

October 8, 2025
Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

October 7, 2025
Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

October 7, 2025
Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

October 7, 2025
Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

October 7, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Go to mobile version