Hukumar kula da Tashoshin Jiragen Ruwa ta Kasa NPA, ta karyata zarge-zargeb batun cin hanci da rasha, inda kuma ta jaddada cewa, samun aukwar yin ba daidai ba ga abinda kasafin kudi ya tanadar, wani abu ne da ba zai taba yuwu wa kan kiyayewar da Hukumar ke yim wajen bin ka’ijojinta ba.
Janar Manja na Hudda da Jama’a da Tsare-Tsare da Samar da Bayanai na Hukumar ta NPA Ikechukwu Onyemekara, ya bayyana haka a cikin sanawar da ya fitar a ranar Lahadi a jihar Legas.
- Masanan Najeriya Sun Bayyana Muhimmancin Hadin Gwiwar Afirka Da Sin A Fannin Tinkarar Kalubalen Harajin Kwastam Na Amurka
- Za Mu RiÆ™e Wa Minista Tijjani MuÆ™aminsa Bayan HamÉ“arar Da Tinubu A 2027 – El-RufaiÂ
Onyemekara ya sanar da cewa, Ma’aikatar Bunkasa Tattalin Arzikin Ruwa da Ofishin Kula da Kasafin Kudi da kuma Majalisar Tarayya, na sanya ido kan yadda Hukumar ta NPA, ke kashe kudaden da aka ware mata a cikin kasafin kudi na kasa.
Ya ci gaba da cewa, aikin yashe hanyar ruwa ta Warri Escrabos, abu ne, da ya zama wajbi, musamman duba da lalacewar hanyar ruwan wanda hakan ya zamo barazana ga zirga-zirgane Jiragen ruwa da kuma shafar ayyukan Man Fetur da na Iskar Gas.
Ya kara da cewa, gwangilar aikin yasar hanyar ruwan, an bayar da ita ne a cikin gagggawa, wadda kuma an bayar da ita ne, a karkashin dokar 2007.
Onyemekara ya sanar da cewa, rahoton na karya da kafar yada labaran ta wallafa kan zargin cin hancin na biliyoyin Naira, na kanzon Kurege ne, wanda kuma bai da wata tushe, ballantana wata makama.
Kazalika, ya bayar da tabbacin cewa, NPA kamar yadda ta saba, za ta ci gaba da gudanar da ayyukanta bisa gaskiya da rikon amana, musamman kan abinda ya shafi, ayyukan kashe kudade.
Onyemekara ya kuma yi watsi da batun zargin badakalar hada-hada a ofishin Hukumar NPA da ke a Birtaniya, inda ya sanar da cewa, babu wani batun wata hada-hadar ayyuka a ofishin makamancin haka, da aka gudanar a ofishin.
Ya yi kira ga kafafen yada labarai na kasar nan, da su tabbatar da suna tuntubar Hukumar kan duk wani rahoton da suke son wallafawa, musamman duba da cewa, kofar Hukumar ako da yaushe bude take, domin yin duk wata suka, mai ma’ana.
Ya sanar da cewa, a karkashin Shugabancin Shugaban Hukumar Abubakar Dantsoho, ya mayar da hankali wajen ganin an zamanantar da ayyukan NPA, musamman ta hanyar samar da kayan aiki, da kuma kara gyara sauran kayan da NPA ke amfani da su.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp