ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Sauye-Sauyen Da Aka Yi A Fannin Mai Da Iskar Gas Suka Samar Da Gagarumin Ci Gaba A Wannan Shekarar

by Bello Hamza
8 months ago
Mai

Babban Shugaban Hukumar Kula da ke Kula da Harkokin Man Fetur da ake Hakowa na Kan Tudu Injiya Gbenga Komolafe ya bayyana cewa, bisa ingantattaun sauye-sauyen da aka samar a kasar nan, na kara bunkasa tattalin arzikin kasar, sun sanya Nijeriya ta samu dala biliyan 18.2 a bangaren zuba hannun jari.

Hakan na kunshe ne, a cikin sanarwar da Hukumar ta fitar, inda sanarwar ta ce, ana kuma sa ran hako ganguna Man Fetur biliyan 1.4 da kuma wasu ganguna biliyan 5.4 na Iskar Gas.

  • Sojoji Sun Kama ‘Yan Ta’adda 25, Sun Ceto Mutum 16 Da Aka Sace
  • Ƴan Bindiga Sun Harbe Wanda Suka Sace Saboda Rashin Isassun Kuɗi A Asusunsa

Sanarwar ta kara da cewa, ana kuma sa ran hako ganguna 591,000 na Man a kullum da kuma wasu ganguna 2.1 na Iskar Gas.

ADVERTISEMENT

Hakan zai kuma kara sanya burin da ake da shi, na samar da sarrafa ganguna miliyan uku na danyen Mai.

Komolafe wanda ya bayyana hakan a wani taro mako na Mai na Afrika da ya gudana a babban birnin Accara na kasar Ghana, ya kara nuna kokarin da gwamnatin shugaban kasa Bola Tinubu ke ci gaba da yi, na cimma kuurin da gwamnatinsa ta sanya a gaba.

LABARAI MASU NASABA

Kamfanin Simintin Ɗangote Ya Ƙaddamar Da Shirye-shiryen Tallafa Wa Mazauna Jihar Biniwe

Dole Ne Afirka Ta Zamanantar Da Sufurin Jiragen Ruwa —Ɗantsoho

Shugaban a kasidar da ya gabatar a wajen taron mai taken: “Ingantattun Sauye-Sauyen da Nijeriya ta kirkiro da su domin cin gajiyar albarkatun da ke a Man Fetur da Iskar Gas”, ya jaddada mahimmancin da ke a fannin Makamashi, musamman wajen kara bunkasa tattalin arzikin kasa da kuma yadda Afirka, za ta amfana.

Ya ci gaba da cewa, sabon sauyen da aka samar a kasar nan a karkashin dokar Masana’antar Man Fetur ta 2021 ta samar da sabon sauyi, a bangaren gudanar da shugabanci na gari.

Shugaban ya kara da cewa, Hukumar musamman a karkashin shugabancin shugaba Tinubu, ta kara zagayewa wajen sanya ido sosai a fannin na sarrafa Mai da Iskar Gas.

Ya ce, Hukumar kusana a cikin shekaru hudu da suka gabata, ta samar da sabbin ka’idoji sanya ido guda 24 a fannin sarrafa Mai da Iskar Gas, inda ya zuwa yanzu, guda 19, aka sanya su a cikin kundin gudanar da ayyuka.

A cewarsa, Hukumar ta kuma kaddamar da cikakken shiri na RAP, wanda ya yi daidai da tsarin dokar ta Masana’antar Man Fetur ta 2021, wanda hakan ya taimaka wajen magance kalubalen da ake fuskanta da kuma tabbatar da ana samar sa Lasisi, a cikin sauki.

Ya kara da cewa, an samu sakamako mai kyau a shirye-shiryen da Hukumar ta kirkiro da su, inda Jaren Ruwan dakon Man suka karu daga takwa zuwa 43 daga watan Satumbar 2021 zuwa watan Satumbar 2025.

“A 2025 kadai Hukumar ta amince da sabbin ayyukan bunkasa FDP guda 28 domin a ci gajiyar gangunan Mai miliyan 1.4 da kuma Iskar Gas 5.4, inda kuma ake sa ran samun gangunan Mai guda 591,000 a kullum da kuma karin wani Iskar Gas 2.1,” A cewarsa.

“Wannan ayyukan na FDP wanda ya kai na dala biliyan 18.2 hakan ya nuna kokarin da ake yin a janyo masu zuba hannun jari a fannin hako da Man na kan Tudu,” Inji Shugaban.

Ya kara da cewa, sauran sun hada da, aikin dala biliyan biyar na FID wanda ake gudanarwa a arewacin Bonga da kuma aikin dala miliyan 500 na Gas da ake yi a yankin Ubeta tare da kuma karin wani akin ne FID kamar na yankunan Ima Gas, Owowo da kuma na Preowei.

Ya ci gaba da cewa, bayan da shugaba Tinubu ya zama shugaban kasa, ya amince da wasu manyan ayyuka guda biyar da suka kai na sama da dala biliyan biyart, wanda hakan ya kara bayar da dama ga masu ruwa da tsaki, na cikin gida da ke a fannin.

Mai
Bello Hamza
+ postsBio
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Dole Ne Afirka Ta Zamanantar Da Sufurin Jiragen Ruwa —Ɗantsoho
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Yadda Oyetola Ya Ƙaddamar Da Babban Taron Ƙungiyar  PMAWCA A Legas
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Lokaci Ya Yi Da Matasan Nijeriya Za Su Ƙwato Ƙasarsu — Kwamred Yahaya Abdullahi
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Kamfanin Dangote Na Kara Karfafa Hadin Gwiwar Tattalin Arziki Da Jihar Neja

MASU ALAKA

Kamfanin Simintin Ɗangote Ya Ƙaddamar Da Shirye-shiryen Tallafa Wa Mazauna Jihar Biniwe
Tattalin Arziki

Kamfanin Simintin Ɗangote Ya Ƙaddamar Da Shirye-shiryen Tallafa Wa Mazauna Jihar Biniwe

May 29, 2026
Dole Ne Afirka Ta Zamanantar Da Sufurin Jiragen Ruwa —Ɗantsoho
Tattalin Arziki

Dole Ne Afirka Ta Zamanantar Da Sufurin Jiragen Ruwa —Ɗantsoho

May 29, 2026
Laifukan Intanet: Kotun Abuja Ta Karɓi Rahoton DSS, Ta Ba Da Belin Wani Ɗan Gwagwarmaya
Tattalin Arziki

Yadda Oyetola Ya Ƙaddamar Da Babban Taron Ƙungiyar  PMAWCA A Legas

May 24, 2026
Next Post
NECO 2025: Gwamnan Kano Ya Bayyana Bayanai Ba Daidai Ba

NECO 2025: Gwamnan Kano Ya Bayyana Bayanai Ba Daidai Ba

LABARAI MASU NASABA

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026
Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

June 4, 2026
Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

June 4, 2026
Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

June 4, 2026
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.