ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Sauye-Sauyen Da Aka Yi A Fannin Mai Da Iskar Gas Suka Samar Da Gagarumin Ci Gaba A Wannan Shekarar

by Bello Hamza
12 months ago
Mai

Babban Shugaban Hukumar Kula da ke Kula da Harkokin Man Fetur da ake Hakowa na Kan Tudu Injiya Gbenga Komolafe ya bayyana cewa, bisa ingantattaun sauye-sauyen da aka samar a kasar nan, na kara bunkasa tattalin arzikin kasar, sun sanya Nijeriya ta samu dala biliyan 18.2 a bangaren zuba hannun jari.

Hakan na kunshe ne, a cikin sanarwar da Hukumar ta fitar, inda sanarwar ta ce, ana kuma sa ran hako ganguna Man Fetur biliyan 1.4 da kuma wasu ganguna biliyan 5.4 na Iskar Gas.

  • Sojoji Sun Kama ‘Yan Ta’adda 25, Sun Ceto Mutum 16 Da Aka Sace
  • Ƴan Bindiga Sun Harbe Wanda Suka Sace Saboda Rashin Isassun Kuɗi A Asusunsa

Sanarwar ta kara da cewa, ana kuma sa ran hako ganguna 591,000 na Man a kullum da kuma wasu ganguna 2.1 na Iskar Gas.

ADVERTISEMENT

Hakan zai kuma kara sanya burin da ake da shi, na samar da sarrafa ganguna miliyan uku na danyen Mai.

Komolafe wanda ya bayyana hakan a wani taro mako na Mai na Afrika da ya gudana a babban birnin Accara na kasar Ghana, ya kara nuna kokarin da gwamnatin shugaban kasa Bola Tinubu ke ci gaba da yi, na cimma kuurin da gwamnatinsa ta sanya a gaba.

LABARAI MASU NASABA

Yadda Taron Bikin Maulidi Ya Gudana A Unguwar Mile 12 A Legas

NPA Ta Bayyana Cewa Kirkiro Da Sabuwar Hukumar NPERA Ba Zai Zame Mata Tarnaki Ba

Shugaban a kasidar da ya gabatar a wajen taron mai taken: “Ingantattun Sauye-Sauyen da Nijeriya ta kirkiro da su domin cin gajiyar albarkatun da ke a Man Fetur da Iskar Gas”, ya jaddada mahimmancin da ke a fannin Makamashi, musamman wajen kara bunkasa tattalin arzikin kasa da kuma yadda Afirka, za ta amfana.

Ya ci gaba da cewa, sabon sauyen da aka samar a kasar nan a karkashin dokar Masana’antar Man Fetur ta 2021 ta samar da sabon sauyi, a bangaren gudanar da shugabanci na gari.

Shugaban ya kara da cewa, Hukumar musamman a karkashin shugabancin shugaba Tinubu, ta kara zagayewa wajen sanya ido sosai a fannin na sarrafa Mai da Iskar Gas.

Ya ce, Hukumar kusana a cikin shekaru hudu da suka gabata, ta samar da sabbin ka’idoji sanya ido guda 24 a fannin sarrafa Mai da Iskar Gas, inda ya zuwa yanzu, guda 19, aka sanya su a cikin kundin gudanar da ayyuka.

A cewarsa, Hukumar ta kuma kaddamar da cikakken shiri na RAP, wanda ya yi daidai da tsarin dokar ta Masana’antar Man Fetur ta 2021, wanda hakan ya taimaka wajen magance kalubalen da ake fuskanta da kuma tabbatar da ana samar sa Lasisi, a cikin sauki.

Ya kara da cewa, an samu sakamako mai kyau a shirye-shiryen da Hukumar ta kirkiro da su, inda Jaren Ruwan dakon Man suka karu daga takwa zuwa 43 daga watan Satumbar 2021 zuwa watan Satumbar 2025.

“A 2025 kadai Hukumar ta amince da sabbin ayyukan bunkasa FDP guda 28 domin a ci gajiyar gangunan Mai miliyan 1.4 da kuma Iskar Gas 5.4, inda kuma ake sa ran samun gangunan Mai guda 591,000 a kullum da kuma karin wani Iskar Gas 2.1,” A cewarsa.

“Wannan ayyukan na FDP wanda ya kai na dala biliyan 18.2 hakan ya nuna kokarin da ake yin a janyo masu zuba hannun jari a fannin hako da Man na kan Tudu,” Inji Shugaban.

Ya kara da cewa, sauran sun hada da, aikin dala biliyan biyar na FID wanda ake gudanarwa a arewacin Bonga da kuma aikin dala miliyan 500 na Gas da ake yi a yankin Ubeta tare da kuma karin wani akin ne FID kamar na yankunan Ima Gas, Owowo da kuma na Preowei.

Ya ci gaba da cewa, bayan da shugaba Tinubu ya zama shugaban kasa, ya amince da wasu manyan ayyuka guda biyar da suka kai na sama da dala biliyan biyart, wanda hakan ya kara bayar da dama ga masu ruwa da tsaki, na cikin gida da ke a fannin.

Mai
Bello Hamza
+ postsBio
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Jihar Kano Za Ta Amfana Matuka Da Gidauniyar Aliko Dangote – Masu Ruwa Da Tsaki
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    An Nuna Damuwa Kan Sake Kamun Da DSS Ta Yi Wa Boɗejo Bayan Samun Belin EFCC
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Dole Al’ummar Arewa Su Rungumi Hanyoyin Kasuwanci Na Zamani —Alfa Musa
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Ba Mu Taba Biyan Kudin Fansa Ba Kuma Ba Za Mu Biya Ba – Kwamishinan Katsina

MASU ALAKA

Yadda Taron Bikin Maulidi Ya Gudana A Unguwar Mile 12 A Legas
Tattalin Arziki

Yadda Taron Bikin Maulidi Ya Gudana A Unguwar Mile 12 A Legas

September 4, 2026
NPA Ta Bayyana Cewa Kirkiro Da Sabuwar Hukumar NPERA Ba Zai Zame Mata Tarnaki Ba
Tattalin Arziki

NPA Ta Bayyana Cewa Kirkiro Da Sabuwar Hukumar NPERA Ba Zai Zame Mata Tarnaki Ba

September 4, 2026
NPA Ta Tabbatar Da Maido Da Manyan Kayan Aikin Hukumar Wuta Ta Neja Delta —Babbar Manaja
Tattalin Arziki

NPA Ta Tabbatar Da Maido Da Manyan Kayan Aikin Hukumar Wuta Ta Neja Delta —Babbar Manaja

August 28, 2026
Next Post
NECO 2025: Gwamnan Kano Ya Bayyana Bayanai Ba Daidai Ba

NECO 2025: Gwamnan Kano Ya Bayyana Bayanai Ba Daidai Ba

LABARAI MASU NASABA

Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.