• English
  • Business News
Sunday, June 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Hukumar Shari’a Ta Dakatar Da Magatakarda 2, Ta Kuma Gargaɗi Alƙalai 2 A Kano

by Sulaiman
2 months ago
in Manyan Labarai
0
kotu
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Hukumar kula da shari’a ta jihar Kano ta dauki matakin ladabtarwa a kan wasu jami’an kotuna hudu, inda ta dakatar da wasu magatakarda biyu tare da yin gargadi ga alkalan kotun shari’a biyu bisa nuna rashin kwarewa da cin zarafin aikinsu.

 

Mai magana da yawun hukumar, Baba Ibrahim ne ya fitar da sanarwar daukar hukuncin ladabtarwar.

  • Ƴansanda Sun Damke Ango Da Abokansa Bayan Mutuwar Amarya A Jigawa
  • Liverpool Sun Zama Zakaran Gasar Premier Bayan Lallasa Tottenham

Ibrahim ya bayyana cewa, an cimma matsayar ne a yayin taron hukumar karo na 80 da aka gudanar a ranar 22 ga Afrilu, 2025, bisa ga shawarwarin kwamitin korafe-korafen jama’a na bangaren shari’a.

 

Labarai Masu Nasaba

Wutar Lantarki Mai Ƙarfi Ta Yi Ajalin Mutum Biyar A Gombe

DA ƊUMI-ƊUMI: Gwamnati Ta Janye Taron Addu’ar Neman Wadatar Abinci

Daga cikin wadanda aka dakatar har da Ibrahim Adamu, babban magatakarda na biyu a babbar kotun shari’a, wanda aka dakatar da shi ba tare da biyansa albashi ba na tsawon watanni shida.

 

Har ila yau, an dage kara masa girma bayan da aka same shi da laifin zagi da kuma yunkurin kai wa nagaba da shi hari – wanda ya saba wa dokokin ma’aikatan jihar Kano (2004) da kuma dokokin hukumar kula da harkokin shari’a.

 

A wata shari’ar kuma, Maigida Lawan, babban magatakarda na kotun daukaka kara ta Shari’a, an hukunta shi ne bisa laifin nema tare da kuma yunkurin biyan bukatun kansa ta hanyar da bata dace ba – karya.

 

Hukumar ta rage masa girma daga mataki na 13 zuwa mataki na 12 sannan ta dakatar da shi ba tare da biyansa albashi ba na tsawon watanni shida, nan take.

 

Har ila yau, Alkalin Kotun Shari’ar Musulunci, Alkali Mansur Ibrahim, ya samu gargadi a hukumance bayan da aka tabbatar da cewa ya yi kalaman batanci ga mai kara.

 

An kuma gargadi abokin aikin sa Alkali Nasiru Ahmad, biyo bayan nuna bangaranci a shari’ar da ya yi.

 

Hukumar ta sake jaddada matsayar ta na yaki da cin hanci da rashawa da rashin da’a, inda ta yi gargadin cewa, duk wani jami’in kotu da aka samu da aikata rashin da’a zai fuskanci hukuncin ritayar dole.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Ƴansanda Sun Damke Ango Da Abokansa Bayan Mutuwar Amarya A Jigawa

Next Post

Cibiyar Yaƙi da Ta’addanci Ta Yaba Wa Gwamna Lawal Kan Matakan Yaƙi Da ‘Yan Bindiga A Zamfara

Related

Wutar Lantarki Mai Ƙarfi Ta Yi Ajalin Mutum Biyar A Gombe
Manyan Labarai

Wutar Lantarki Mai Ƙarfi Ta Yi Ajalin Mutum Biyar A Gombe

8 hours ago
DA ƊUMI-ƊUMI: Gwamnati Ta Janye Taron Addu’ar Neman Wadatar Abinci
Manyan Labarai

DA ƊUMI-ƊUMI: Gwamnati Ta Janye Taron Addu’ar Neman Wadatar Abinci

15 hours ago
Majalisar Tarayya Na Ƙoƙarin Zama Ƴar Amshin Shata – Saraki
Manyan Labarai

Majalisar Tarayya Na Ƙoƙarin Zama Ƴar Amshin Shata – Saraki

2 days ago
Cikin Shekaru 2, Tinubu Ya Karɓo Bashi Fiye da Shugabannin Nijeriya 3 – Obi
Manyan Labarai

Cikin Shekaru 2, Tinubu Ya Karɓo Bashi Fiye da Shugabannin Nijeriya 3 – Obi

2 days ago
nijeriya
Manyan Labarai

Yadda Badakalar Tallafin Man Fetur Ta Zame Wa Nijeriya Alakakai

2 days ago
Ba Zan Bar Nijeriya Ta Zama Kasa Mai Jam’iyya Daya Ba – Tinubu
Manyan Labarai

Ba Zan Bar Nijeriya Ta Zama Kasa Mai Jam’iyya Daya Ba – Tinubu

2 days ago
Next Post
Cibiyar Yaƙi da Ta’addanci Ta Yaba Wa Gwamna Lawal Kan Matakan Yaƙi Da ‘Yan Bindiga A Zamfara

Cibiyar Yaƙi da Ta'addanci Ta Yaba Wa Gwamna Lawal Kan Matakan Yaƙi Da 'Yan Bindiga A Zamfara

LABARAI MASU NASABA

Wakilin Sin A IAEA Ya Yi Tir Da Harin Isra’ila Kan Cibiyoyin Sarrafa Nukiliyar Iran

Wakilin Sin A IAEA Ya Yi Tir Da Harin Isra’ila Kan Cibiyoyin Sarrafa Nukiliyar Iran

June 14, 2025
Za A Watsa Shirin “Bayanan Magabata Dake Jan Hankalin Xi Jinping” A Kafofin Watsa Shirye-shiryen Kasashen Tsakiyar Asiya Biyar

Za A Watsa Shirin “Bayanan Magabata Dake Jan Hankalin Xi Jinping” A Kafofin Watsa Shirye-shiryen Kasashen Tsakiyar Asiya Biyar

June 14, 2025
Muhammad Salah: Gwarzon Afirka A Firimiyar Ingila

Rawar Da ‘Yan Wasan Afirka Suka Taka A Gasar Premier Ta Ingila

June 14, 2025
Wakilin Sin: Matakin Amurka Game Da Harajin Kwastam Bai Yi La’akari Da Rarar Cinikayyar Hidimomi Ba

Wakilin Sin: Matakin Amurka Game Da Harajin Kwastam Bai Yi La’akari Da Rarar Cinikayyar Hidimomi Ba

June 14, 2025
Kuri’un Jin Ra’ayin Jama’a Na CGTN Sun Shaida Gamsuwa Da Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Tsakiyar Asiya

Kuri’un Jin Ra’ayin Jama’a Na CGTN Sun Shaida Gamsuwa Da Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Tsakiyar Asiya

June 14, 2025
Danbun Shinkafa Da Nama Da Kifi

Danbun Shinkafa Da Nama Da Kifi

June 14, 2025
Wutar Lantarki Mai Ƙarfi Ta Yi Ajalin Mutum Biyar A Gombe

Wutar Lantarki Mai Ƙarfi Ta Yi Ajalin Mutum Biyar A Gombe

June 14, 2025
Sin Ta Harba Tauraron Dan Adam Na Lura Da Yanayin Bala’u

Sin Ta Harba Tauraron Dan Adam Na Lura Da Yanayin Bala’u

June 14, 2025
An Samu Babban Canji Kan Tsarin Ciniki A Tsakanin Sin Da Afirka

An Samu Babban Canji Kan Tsarin Ciniki A Tsakanin Sin Da Afirka

June 14, 2025
Muhimmanci, Tasiri Da Kuma Amfanin Jigida Ga Mata

Muhimmanci, Tasiri Da Kuma Amfanin Jigida Ga Mata

June 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.