• English
  • Business News
Saturday, August 23, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Hukumar Shige Da Fice Ta Shirya Wa Jami’anta Gwaji Kan Shan Miyagun Kwayoyi Da Horo Na Musamman A Yenaguwa

by Sadiq
3 years ago
in Labarai
0
Hukumar Shige Da Fice Ta Shirya Wa Jami’anta Gwaji Kan Shan Miyagun Kwayoyi Da Horo Na Musamman A Yenaguwa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kwanturolan Hukumar Shige Da Fice na Jihar Bayelsa, James Sunday, ya bukaci sauran jami’an hukumar da su gudanar da gwaji na musamman da horo ga jami’an hukumar da ke jihohinsu kan sanin makamar aiki.

Wannan na dauke ne cikin wata sanarwa da kakakin hukumar ya fitar a ranar Talata, ta ofishin kwanturolan hukumar a jihar.

  • Muna Kan Kokarin Magance Matsalar Hauhawar Farashin Kayan Masarufi —Buhari
  • An Ba Ma’aikatan Bayelsa Hutun Kwana 7 Kan Ibtila’in Ambaliyar Ruwa

A cewarsa dole ne su tuna ranstuwar da suka yi lokacin fara aikin ta hanyar tsare sirri, martaba da darajar aikin, wanda kowane ma’aikacin hukumar ake sa ran zai samu horo na musamman duba da irin ayyukan da suke gudanarwa wanda ke da alaka da kasashen ketare da kuma cikin gida da kuma yin mu’amala da wadanda ba ‘yan Nijeriya ba, mutane daga kasashen waje wadanda suke sa ran samun kyakkyawar mu’amala daga gare mu ta hanyar jami’an hukumar shige da fice ta kasa ta kowace fuska.

A cewar sanarwar, ana sa ran jami’in hukumar shige da fice ya kasance mai dabi’u masu nagarta a bangarori da dama ba wai iya abin da ya shafi samar sa fasfo da sauran takardu na yin tafiye-tafiye zuwa wasu kasashe ba, alaka mai kyau da kasashen waje da kuma mu’amalar diflomasiyya, kungiyoyi da sauran hada-hada a filayen jiragen sama, tashoshin jiragen ruwa da kuma kan iyakokin kasa wanda ta nan wasu ‘yan kasashen ke kararowa zuwa Nijeriya, ana sa ran jami’i zai ba da himma wajen cika muradan aikinsa.

Horon ya zo a kan lokaci duba da samun sabbin jami’ai da ke bukatar ja a jiki, don ba su horo kulawa don ganin sun bada cikakkiyar gudunmawa, ta hanyar samun gogewa da dabi’u masu kyau ga kasa da kuma al’umma.

Labarai Masu Nasaba

Masana Sun Gano Dalilan Da Ke Taimaka Wa Ballewar Daurarru A Gidan Yari

UNICEF Na Neman Naira Biliyan 240 Don Ayyukan Agaji A Nijeriya

Kwanturolan ya ware lokaci inda ya gargadi jami’an hukumar kan amfani da kafafen sada zumunta, inda ya bukace su da su san irin abin da za su ke wallafawa a kafafen sada zumunta, wanda ya ce su guji yada abin da zai zubar da kima, daraja ko mutuncin hukumar, musamman duba da yadda zaben 2023 ke kara karatowa.

Kwanturolan ya jaddada cewae hukumar ta shirya hanyoyin daukar hukunci kan duk wani yanayi da ka iya haifar da rashin jin dadi, inda ya ce hukumar ba za ta yi kasa a gwiwa ba duk da barazanar ambaliyar ruwa da ake fuskanta a Jihar Bayelsa, amma a cewarsa hukumar ta kwashe dukkan wasu kayan aikinta da ka iya lalacewa saboda ambaliyar ruwan zuwa wani waje da babu ruwa ko raba.

Ya kara da cewar duk da jihar na cikin mawuyacin hali a dalilin ambaliyar ruwan, amma akwai wuraren da abun bai shafa ba, suna cikin yanayi mai kyau, inda ya ce hukumar ta mayar da ayyukanta zuwa rukunin gidaje da ke Okaka a cikin kwaryar birnin jihar.

Sannan ya ce ayyukan hukumar za su ci gaba da wakana a can na wucin gadi, inda ya ce hukumar a jihar da jami’anta sun yi wannan dabara ne don gudun tsayuwar ayyukanta ga jama’ar jihar.

Kwanturolan ya jaddada cewar hukumar ba ta dakatar da ayyukanta ba, “Muna yin aiki kuma jami’anmu da mutanenmu na aiki kamar kowane lokaci,” kamar yadda sanarwar ta bayyana.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: BayelsaGwajin Shan Miyagun KwayoyiHoroHukumar Shige Da FiceJami'aiSanin Makamar AikiYenaguwa
ShareTweetSendShare
Previous Post

Muna Kan Kokarin Magance Matsalar Hauhawar Farashin Kayan Masarufi —Buhari

Next Post

‘Yan Bindiga Sun Yi Awon-Gaba Da Jami’an Lafiya Da Marasa Lafiya A Jihar Neja

Related

Masana Sun Gano Dalilan Da Ke Taimaka Wa Ballewar Daurarru A Gidan Yari
Rahotonni

Masana Sun Gano Dalilan Da Ke Taimaka Wa Ballewar Daurarru A Gidan Yari

2 hours ago
UNICEF Na Neman Naira Biliyan 240 Don Ayyukan Agaji A Nijeriya
Labarai

UNICEF Na Neman Naira Biliyan 240 Don Ayyukan Agaji A Nijeriya

11 hours ago
Ɓarayin Waya Sun Hallaka Ɗalibin ATAP A Bauchi
Labarai

Ɓarayin Waya Sun Hallaka Ɗalibin ATAP A Bauchi

12 hours ago
JAMB Ta Kaddamar Da Kwamitin Bincike Kan Satar Jarabawa
Labarai

JAMB Ta Kaddamar Da Kwamitin Bincike Kan Satar Jarabawa

12 hours ago
Raguwar Hauhawar Farashi: ‘Yan Nijeriya Da ‘Yan Kasuwa Ba Su Ga Saukin A Zahirance Ba
Labarai

Raguwar Hauhawar Farashi: ‘Yan Nijeriya Da ‘Yan Kasuwa Ba Su Ga Saukin A Zahirance Ba

13 hours ago
Mahara Sun Kai Hari Banki A Kogi
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Kama Jagororin ‘Yan Bindiga A Abuja, Sun Ƙwato Makamai Da ₦7.4m

15 hours ago
Next Post
‘Yan Bindiga Sun Yi Awon-Gaba Da Jami’an Lafiya Da Marasa Lafiya A Jihar Neja

'Yan Bindiga Sun Yi Awon-Gaba Da Jami'an Lafiya Da Marasa Lafiya A Jihar Neja

LABARAI MASU NASABA

Zaben Cike Gurbi: Tinubu Ya Lalata Tsarin Zaben Nijeriya — ADC

Zaben Cike Gurbi: Tinubu Ya Lalata Tsarin Zaben Nijeriya — ADC

August 23, 2025
Masana Sun Gano Dalilan Da Ke Taimaka Wa Ballewar Daurarru A Gidan Yari

Masana Sun Gano Dalilan Da Ke Taimaka Wa Ballewar Daurarru A Gidan Yari

August 23, 2025
Wajibi Ne Sassan Kasa Da Kasa Su Raya Ruhin Jin Kan Bil’adama

Wajibi Ne Sassan Kasa Da Kasa Su Raya Ruhin Jin Kan Bil’adama

August 22, 2025
UNICEF Na Neman Naira Biliyan 240 Don Ayyukan Agaji A Nijeriya

UNICEF Na Neman Naira Biliyan 240 Don Ayyukan Agaji A Nijeriya

August 22, 2025
Sin Ta Samu Karin Kamfanoni Kusan Miliyan 20 A Cikin Shirin Shekaru Biyar Karo Na 14

Sin Ta Samu Karin Kamfanoni Kusan Miliyan 20 A Cikin Shirin Shekaru Biyar Karo Na 14

August 22, 2025
Ɓarayin Waya Sun Hallaka Ɗalibin ATAP A Bauchi

Ɓarayin Waya Sun Hallaka Ɗalibin ATAP A Bauchi

August 22, 2025
JAMB Ta Kaddamar Da Kwamitin Bincike Kan Satar Jarabawa

JAMB Ta Kaddamar Da Kwamitin Bincike Kan Satar Jarabawa

August 22, 2025
Wadanda Suka Mutu A Wani Hadarin Ginin Gada A Sin Sun Karu Zuwa 12

Wadanda Suka Mutu A Wani Hadarin Ginin Gada A Sin Sun Karu Zuwa 12

August 22, 2025
Raguwar Hauhawar Farashi: ‘Yan Nijeriya Da ‘Yan Kasuwa Ba Su Ga Saukin A Zahirance Ba

Raguwar Hauhawar Farashi: ‘Yan Nijeriya Da ‘Yan Kasuwa Ba Su Ga Saukin A Zahirance Ba

August 22, 2025
Kamfanin Novo Nordisk Na Denmark Zai Ci Gaba Da Zuba Jari A Kasar Sin A Bana

Kamfanin Novo Nordisk Na Denmark Zai Ci Gaba Da Zuba Jari A Kasar Sin A Bana

August 22, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.