ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Hukumar Shige Da Fice Ta Shirya Wa Jami’anta Gwaji Kan Shan Miyagun Kwayoyi Da Horo Na Musamman A Yenaguwa

by Sadiq
4 years ago
Shige Da Fice

Kwanturolan Hukumar Shige Da Fice na Jihar Bayelsa, James Sunday, ya bukaci sauran jami’an hukumar da su gudanar da gwaji na musamman da horo ga jami’an hukumar da ke jihohinsu kan sanin makamar aiki.

Wannan na dauke ne cikin wata sanarwa da kakakin hukumar ya fitar a ranar Talata, ta ofishin kwanturolan hukumar a jihar.

  • Muna Kan Kokarin Magance Matsalar Hauhawar Farashin Kayan Masarufi —Buhari
  • An Ba Ma’aikatan Bayelsa Hutun Kwana 7 Kan Ibtila’in Ambaliyar Ruwa

A cewarsa dole ne su tuna ranstuwar da suka yi lokacin fara aikin ta hanyar tsare sirri, martaba da darajar aikin, wanda kowane ma’aikacin hukumar ake sa ran zai samu horo na musamman duba da irin ayyukan da suke gudanarwa wanda ke da alaka da kasashen ketare da kuma cikin gida da kuma yin mu’amala da wadanda ba ‘yan Nijeriya ba, mutane daga kasashen waje wadanda suke sa ran samun kyakkyawar mu’amala daga gare mu ta hanyar jami’an hukumar shige da fice ta kasa ta kowace fuska.

ADVERTISEMENT

A cewar sanarwar, ana sa ran jami’in hukumar shige da fice ya kasance mai dabi’u masu nagarta a bangarori da dama ba wai iya abin da ya shafi samar sa fasfo da sauran takardu na yin tafiye-tafiye zuwa wasu kasashe ba, alaka mai kyau da kasashen waje da kuma mu’amalar diflomasiyya, kungiyoyi da sauran hada-hada a filayen jiragen sama, tashoshin jiragen ruwa da kuma kan iyakokin kasa wanda ta nan wasu ‘yan kasashen ke kararowa zuwa Nijeriya, ana sa ran jami’i zai ba da himma wajen cika muradan aikinsa.

Horon ya zo a kan lokaci duba da samun sabbin jami’ai da ke bukatar ja a jiki, don ba su horo kulawa don ganin sun bada cikakkiyar gudunmawa, ta hanyar samun gogewa da dabi’u masu kyau ga kasa da kuma al’umma.

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa’ — Atiku

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Kwanturolan ya ware lokaci inda ya gargadi jami’an hukumar kan amfani da kafafen sada zumunta, inda ya bukace su da su san irin abin da za su ke wallafawa a kafafen sada zumunta, wanda ya ce su guji yada abin da zai zubar da kima, daraja ko mutuncin hukumar, musamman duba da yadda zaben 2023 ke kara karatowa.

Kwanturolan ya jaddada cewae hukumar ta shirya hanyoyin daukar hukunci kan duk wani yanayi da ka iya haifar da rashin jin dadi, inda ya ce hukumar ba za ta yi kasa a gwiwa ba duk da barazanar ambaliyar ruwa da ake fuskanta a Jihar Bayelsa, amma a cewarsa hukumar ta kwashe dukkan wasu kayan aikinta da ka iya lalacewa saboda ambaliyar ruwan zuwa wani waje da babu ruwa ko raba.

Ya kara da cewar duk da jihar na cikin mawuyacin hali a dalilin ambaliyar ruwan, amma akwai wuraren da abun bai shafa ba, suna cikin yanayi mai kyau, inda ya ce hukumar ta mayar da ayyukanta zuwa rukunin gidaje da ke Okaka a cikin kwaryar birnin jihar.

Sannan ya ce ayyukan hukumar za su ci gaba da wakana a can na wucin gadi, inda ya ce hukumar a jihar da jami’anta sun yi wannan dabara ne don gudun tsayuwar ayyukanta ga jama’ar jihar.

Kwanturolan ya jaddada cewar hukumar ba ta dakatar da ayyukanta ba, “Muna yin aiki kuma jami’anmu da mutanenmu na aiki kamar kowane lokaci,” kamar yadda sanarwar ta bayyana.

MASU ALAKA

Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku
Manyan Labarai

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa’ — Atiku

June 25, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
Labarai

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
Ra'ayi Riga

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Next Post
‘Yan Bindiga Sun Yi Awon-Gaba Da Jami’an Lafiya Da Marasa Lafiya A Jihar Neja

'Yan Bindiga Sun Yi Awon-Gaba Da Jami'an Lafiya Da Marasa Lafiya A Jihar Neja

LABARAI MASU NASABA

Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa’ — Atiku

June 25, 2026
Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.