ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Hukumar Shige Da Fice Ta Shirya Wa Jami’anta Gwaji Kan Shan Miyagun Kwayoyi Da Horo Na Musamman A Yenaguwa

by Sadiq
4 years ago
Shige Da Fice

Kwanturolan Hukumar Shige Da Fice na Jihar Bayelsa, James Sunday, ya bukaci sauran jami’an hukumar da su gudanar da gwaji na musamman da horo ga jami’an hukumar da ke jihohinsu kan sanin makamar aiki.

Wannan na dauke ne cikin wata sanarwa da kakakin hukumar ya fitar a ranar Talata, ta ofishin kwanturolan hukumar a jihar.

  • Muna Kan Kokarin Magance Matsalar Hauhawar Farashin Kayan Masarufi —Buhari
  • An Ba Ma’aikatan Bayelsa Hutun Kwana 7 Kan Ibtila’in Ambaliyar Ruwa

A cewarsa dole ne su tuna ranstuwar da suka yi lokacin fara aikin ta hanyar tsare sirri, martaba da darajar aikin, wanda kowane ma’aikacin hukumar ake sa ran zai samu horo na musamman duba da irin ayyukan da suke gudanarwa wanda ke da alaka da kasashen ketare da kuma cikin gida da kuma yin mu’amala da wadanda ba ‘yan Nijeriya ba, mutane daga kasashen waje wadanda suke sa ran samun kyakkyawar mu’amala daga gare mu ta hanyar jami’an hukumar shige da fice ta kasa ta kowace fuska.

ADVERTISEMENT

A cewar sanarwar, ana sa ran jami’in hukumar shige da fice ya kasance mai dabi’u masu nagarta a bangarori da dama ba wai iya abin da ya shafi samar sa fasfo da sauran takardu na yin tafiye-tafiye zuwa wasu kasashe ba, alaka mai kyau da kasashen waje da kuma mu’amalar diflomasiyya, kungiyoyi da sauran hada-hada a filayen jiragen sama, tashoshin jiragen ruwa da kuma kan iyakokin kasa wanda ta nan wasu ‘yan kasashen ke kararowa zuwa Nijeriya, ana sa ran jami’i zai ba da himma wajen cika muradan aikinsa.

Horon ya zo a kan lokaci duba da samun sabbin jami’ai da ke bukatar ja a jiki, don ba su horo kulawa don ganin sun bada cikakkiyar gudunmawa, ta hanyar samun gogewa da dabi’u masu kyau ga kasa da kuma al’umma.

LABARAI MASU NASABA

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Kwanturolan ya ware lokaci inda ya gargadi jami’an hukumar kan amfani da kafafen sada zumunta, inda ya bukace su da su san irin abin da za su ke wallafawa a kafafen sada zumunta, wanda ya ce su guji yada abin da zai zubar da kima, daraja ko mutuncin hukumar, musamman duba da yadda zaben 2023 ke kara karatowa.

Kwanturolan ya jaddada cewae hukumar ta shirya hanyoyin daukar hukunci kan duk wani yanayi da ka iya haifar da rashin jin dadi, inda ya ce hukumar ba za ta yi kasa a gwiwa ba duk da barazanar ambaliyar ruwa da ake fuskanta a Jihar Bayelsa, amma a cewarsa hukumar ta kwashe dukkan wasu kayan aikinta da ka iya lalacewa saboda ambaliyar ruwan zuwa wani waje da babu ruwa ko raba.

Ya kara da cewar duk da jihar na cikin mawuyacin hali a dalilin ambaliyar ruwan, amma akwai wuraren da abun bai shafa ba, suna cikin yanayi mai kyau, inda ya ce hukumar ta mayar da ayyukanta zuwa rukunin gidaje da ke Okaka a cikin kwaryar birnin jihar.

Sannan ya ce ayyukan hukumar za su ci gaba da wakana a can na wucin gadi, inda ya ce hukumar a jihar da jami’anta sun yi wannan dabara ne don gudun tsayuwar ayyukanta ga jama’ar jihar.

Kwanturolan ya jaddada cewar hukumar ba ta dakatar da ayyukanta ba, “Muna yin aiki kuma jami’anmu da mutanenmu na aiki kamar kowane lokaci,” kamar yadda sanarwar ta bayyana.

MASU ALAKA

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba
Labaran Kasuwanci

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026
Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City
Wasanni

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed
Labarai

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Next Post
‘Yan Bindiga Sun Yi Awon-Gaba Da Jami’an Lafiya Da Marasa Lafiya A Jihar Neja

'Yan Bindiga Sun Yi Awon-Gaba Da Jami'an Lafiya Da Marasa Lafiya A Jihar Neja

LABARAI MASU NASABA

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026
Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

June 4, 2026
Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

June 4, 2026
Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

June 4, 2026
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.