• English
  • Business News
Thursday, October 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Illar Kakaba Wa Majalisa Ta 10 Shugabanni Ga Gwamnatin Tinubu – Dattawan Arewa

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
Majalisa

Kungiyar Dattawan Arewa (NEF) ta bayyana cewa kokarin kakaba shugabanci a majalisa 10 da ake shirin kaddamarwa ba zai harfar wa da gwamnatin shugaban kasa Bola Tinubu da mai ido ba.

Kakakin NEF, Hakeem Baba-Ahmed shi ya bayyana haka a wata hira da ya yi da gidan talabijin na Channels tb a ranar Talata.

  • Majalisar Dokokin Jihar Taraba Ta Bukaci Tinubu Ya Ayyana Dokar Ta-baci Kan Tsaro Jihar
  • Sin: Yin Katsa-landan Da Sanya Takunkumin Kashin Kai Ba Za Su Warware Batun Tsakiyar Afirka Ba

Hakeem ya ce, “Ba amfanin Shugaba Tinubu ba ne ya dora shugabannin a majalisar kasa. Ba ya cikin maslaha.

“Abin da ya fi dacewa shi ne, Tinubu ya nisanta kansa daga zaben shugabanin majalisar dattawa da mataimakinsa,” in ji shi.

Kakakin NEF ya jaddada cewa a bar ‘yan majalisar dattawa da ta wakilai su yanke hukunci wajen zaben shugabanninsu ba tare da tsoma bakin shugaban kasa ba.

LABARAI MASU NASABA

ADC Ta Umarci Dukkan Mambobinta Su Yi Murabus Daga Tsoffin Jam’iyyunsu

Dage Zaben Shugabannin PDP Na Jihohi Ya Kara Ruruta Wutar Rikici A Jam’iyyar

Ya ce, “Ya kamata a bar ‘yan majalisa su yanke hukunci kan wurin da shugabanci zai nufa. Wannan ita ce ra’ayina da na tsaya a kai. Ban da ra’ayin cewa sai shugabancin majalisa ya koma yankin arewa. Na ce akwai sauran abubuwan da ya kamata a yi la’akari da su.

“Idan ‘yan majalisa suka yanke hukunci cikin adalci, to shugabancin majalisa zai iya komawa kudu, mun tabbatar da haka. Sanna kuma zai iya zuwa arewa, babu wata matsala.”

Ya ce matsayin shugaban majalisar dattawa ana iya nada kowa kuma ana iya tsige shi.

Idan za a iya tuna jam’iyyar APC mai mulki ita ke da yawan kujeru a majalisar wakilai da suka kai 170 daga cikin kujeru 360 na zauren majalisar.

Babbar jam’iyyar adawa ta PDP ta zo ta biyu da kujeru sama da 100, jam’iyyar LP mai kujeru sama da 35, jam’iyyar NNPP ta samu kusan 20.

‘Yan majalisar APC da suka nuna sha’awarsu na zama shugaban majalisar wakilai dai sun hada da Benjamin Kalu, Ahmed Wase, Alhassan Ado-Doguwa, Yusuf Gagdi, Aliyu Betara, Tajudeen Abbas, Abdulraheem Olawuyi, Sani Jaji, Gimbiya Onuoha da dai sauransu.

Haka kuma a bangaren majalisar dattawa kuwa, masu sha’awar zama shugaban majalisar dattawa sun hada da Sanata Abdulaziz Yari, Orji Kalu, Godswill Akpabio da dai sauransu.

Sai dai kuma jam’iyyar APC ta tsayar da Akpabio daga yankin kudu maso kudu a matsayin shugaban majalisar dattawa da kuma Barau Jibrin daga yankin arewa maso yamma a matsayin mataimakin shugaban majalisar dattawa.

Jam’iyyar ta kuma tsayar da shugabancin majalisar wakilai zuwa arewa maso yamma wanda ta bai wa Abass, da mataimakin shugaban majalisar daga kudu maso gabas da ta bai wa Kalu.

Sai dai kuma hukuncin jam’iyyar ta gamu da rashin amincewa daga mafi yawancin ‘ya’yan jam’iyyar APC, inda suka bukaci a sake duba tsarin da zai shafi shiyyar arewa ta tsakiya ba wai matsayi biyu na yankin krewa maso yamma ba.

Hujjarsu ita ce arewa maso yamma sun bai wa shugaban kasa kuri’a mafi girma don haka ya cancanci a biya su diyya na kai shugabancin majalisar ga yankin.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

ADC Ta Dakatar Da Shugabanta Da Wasu Jiga-jigai 3 A Kebbi
Tambarin Dimokuradiyya

ADC Ta Umarci Dukkan Mambobinta Su Yi Murabus Daga Tsoffin Jam’iyyunsu

October 3, 2025
Dage Zaben Shugabannin PDP Na Jihohi Ya Kara Ruruta Wutar Rikici A Jam’iyyar
Tambarin Dimokuradiyya

Dage Zaben Shugabannin PDP Na Jihohi Ya Kara Ruruta Wutar Rikici A Jam’iyyar

October 3, 2025
Yadda Na Kawo Karshen Yajin Aikin ASUU Cikin Kwana Daya – Jonathan
Tambarin Dimokuradiyya

Lalacewar Tsarin Zabe Babbar Barazana Ce Ga Dorewar Dimokuradiyyar Afirka — Jonathan

September 27, 2025
Next Post
Sharhi: Shin Tinubu Zai Iya Kai Bantensa Bisa Yadda Ya Fara?

Sharhi: Shin Tinubu Zai Iya Kai Bantensa Bisa Yadda Ya Fara?

LABARAI MASU NASABA

TCN

Jami’an Tsaro Sun Cafke Ɓarayin Kayayyakin Turakun Wutar Lantarki Na Hanyar Mando Zuwa Jos

October 9, 2025
An Yi Tafiye-tafiye Miliyan 16.34 Da Suka Shafi Shiga Da Fita Daga Kasar Sin Yayin Hutun Kwanaki 8 Na Kasar 

An Yi Tafiye-tafiye Miliyan 16.34 Da Suka Shafi Shiga Da Fita Daga Kasar Sin Yayin Hutun Kwanaki 8 Na Kasar 

October 9, 2025
Nijeriya Ta Yi Asarar Ganga Miliyan 13.5 Na Ɗanyen Mai Ta Hanyar Sata Da Zagon-ƙasa – NEITI

Nijeriya Ta Yi Asarar Ganga Miliyan 13.5 Na Ɗanyen Mai Ta Hanyar Sata Da Zagon-ƙasa – NEITI

October 9, 2025
Duniya Ta Kara Ganin Bunkasuwar Sin a Lokacin Hutun Murnar Ranar Kafuwar Sabuwar Kasar

Duniya Ta Kara Ganin Bunkasuwar Sin a Lokacin Hutun Murnar Ranar Kafuwar Sabuwar Kasar

October 9, 2025
Fursunoni Ba Za Su Samu Damar Kada Kuri’a Ba A Zaben 2023 – INEC

Batun Umarnin Kotu Na Kama Tsohon Shugaban INEC Ƙage Ne Kawai – Shugaban Jam’iyyar AA 

October 9, 2025
An Samu Karuwar Sayayya Yayin Hutun Bikin Kafuwar Kasar Sin

An Samu Karuwar Sayayya Yayin Hutun Bikin Kafuwar Kasar Sin

October 9, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Zaɓi Farfesa Amupitan A Matsayin Sabon Shugaban INEC 

Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Zaɓi Farfesa Amupitan A Matsayin Sabon Shugaban INEC 

October 9, 2025
Adadin Biyan Kudade Ta Intanet Yayin Hutun Bikin Kafuwar Jamhuriyar Jama’ar Sin Ya Kai Yuan Tiriliyan 13.26

Adadin Biyan Kudade Ta Intanet Yayin Hutun Bikin Kafuwar Jamhuriyar Jama’ar Sin Ya Kai Yuan Tiriliyan 13.26

October 9, 2025
SSANU Da NASU Sun Yi Zanga-Zanga A Abuja Kan Rashin Cika Alƙawarin Gwamnati

SSANU Da NASU Sun Yi Zanga-Zanga A Abuja Kan Rashin Cika Alƙawarin Gwamnati

October 9, 2025
An Umurci Manyan Makarantu Su Mayar Da Kuɗaɗen TETFund Da Ba Su Kashe Ba

An Umurci Manyan Makarantu Su Mayar Da Kuɗaɗen TETFund Da Ba Su Kashe Ba

October 9, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.