• English
  • Business News
Thursday, May 22, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Illar Kakaba Wa Majalisa Ta 10 Shugabanni Ga Gwamnatin Tinubu – Dattawan Arewa

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
in Tambarin Dimokuradiyya
0
Illar Kakaba Wa Majalisa Ta 10 Shugabanni Ga Gwamnatin Tinubu – Dattawan Arewa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kungiyar Dattawan Arewa (NEF) ta bayyana cewa kokarin kakaba shugabanci a majalisa 10 da ake shirin kaddamarwa ba zai harfar wa da gwamnatin shugaban kasa Bola Tinubu da mai ido ba.

Kakakin NEF, Hakeem Baba-Ahmed shi ya bayyana haka a wata hira da ya yi da gidan talabijin na Channels tb a ranar Talata.

  • Majalisar Dokokin Jihar Taraba Ta Bukaci Tinubu Ya Ayyana Dokar Ta-baci Kan Tsaro Jihar
  • Sin: Yin Katsa-landan Da Sanya Takunkumin Kashin Kai Ba Za Su Warware Batun Tsakiyar Afirka Ba

Hakeem ya ce, “Ba amfanin Shugaba Tinubu ba ne ya dora shugabannin a majalisar kasa. Ba ya cikin maslaha.

“Abin da ya fi dacewa shi ne, Tinubu ya nisanta kansa daga zaben shugabanin majalisar dattawa da mataimakinsa,” in ji shi.

Kakakin NEF ya jaddada cewa a bar ‘yan majalisar dattawa da ta wakilai su yanke hukunci wajen zaben shugabanninsu ba tare da tsoma bakin shugaban kasa ba.

Labarai Masu Nasaba

Shugaban INEC Ya Yi Kira Da A Sake Fasalin Tsarin Zabe Gabanin 2027

Amfani Da Karfin Gwamnati Kan ‘Yan Adawa Zai Jawo Wa Tinubu Illa A 2027 – Sule Lamido

Ya ce, “Ya kamata a bar ‘yan majalisa su yanke hukunci kan wurin da shugabanci zai nufa. Wannan ita ce ra’ayina da na tsaya a kai. Ban da ra’ayin cewa sai shugabancin majalisa ya koma yankin arewa. Na ce akwai sauran abubuwan da ya kamata a yi la’akari da su.

“Idan ‘yan majalisa suka yanke hukunci cikin adalci, to shugabancin majalisa zai iya komawa kudu, mun tabbatar da haka. Sanna kuma zai iya zuwa arewa, babu wata matsala.”

Ya ce matsayin shugaban majalisar dattawa ana iya nada kowa kuma ana iya tsige shi.

Idan za a iya tuna jam’iyyar APC mai mulki ita ke da yawan kujeru a majalisar wakilai da suka kai 170 daga cikin kujeru 360 na zauren majalisar.

Babbar jam’iyyar adawa ta PDP ta zo ta biyu da kujeru sama da 100, jam’iyyar LP mai kujeru sama da 35, jam’iyyar NNPP ta samu kusan 20.

‘Yan majalisar APC da suka nuna sha’awarsu na zama shugaban majalisar wakilai dai sun hada da Benjamin Kalu, Ahmed Wase, Alhassan Ado-Doguwa, Yusuf Gagdi, Aliyu Betara, Tajudeen Abbas, Abdulraheem Olawuyi, Sani Jaji, Gimbiya Onuoha da dai sauransu.

Haka kuma a bangaren majalisar dattawa kuwa, masu sha’awar zama shugaban majalisar dattawa sun hada da Sanata Abdulaziz Yari, Orji Kalu, Godswill Akpabio da dai sauransu.

Sai dai kuma jam’iyyar APC ta tsayar da Akpabio daga yankin kudu maso kudu a matsayin shugaban majalisar dattawa da kuma Barau Jibrin daga yankin arewa maso yamma a matsayin mataimakin shugaban majalisar dattawa.

Jam’iyyar ta kuma tsayar da shugabancin majalisar wakilai zuwa arewa maso yamma wanda ta bai wa Abass, da mataimakin shugaban majalisar daga kudu maso gabas da ta bai wa Kalu.

Sai dai kuma hukuncin jam’iyyar ta gamu da rashin amincewa daga mafi yawancin ‘ya’yan jam’iyyar APC, inda suka bukaci a sake duba tsarin da zai shafi shiyyar arewa ta tsakiya ba wai matsayi biyu na yankin krewa maso yamma ba.

Hujjarsu ita ce arewa maso yamma sun bai wa shugaban kasa kuri’a mafi girma don haka ya cancanci a biya su diyya na kai shugabancin majalisar ga yankin.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: majalisaTambarin Dimokuradiyya
ShareTweetSendShare
Previous Post

GORON JUMA’A

Next Post

Sharhi: Shin Tinubu Zai Iya Kai Bantensa Bisa Yadda Ya Fara?

Related

Shugaban INEC Ya Yi Kira Da A Sake Fasalin Tsarin Zabe Gabanin 2027
Tambarin Dimokuradiyya

Shugaban INEC Ya Yi Kira Da A Sake Fasalin Tsarin Zabe Gabanin 2027

3 weeks ago
Majalisa
Tambarin Dimokuradiyya

Amfani Da Karfin Gwamnati Kan ‘Yan Adawa Zai Jawo Wa Tinubu Illa A 2027 – Sule Lamido

3 weeks ago
‘Yan Siyasa Na Gwagwarmaya Ne Kadai Wajen Neman Mukami Ba Wai Don Talakawa Ba — Bafarawa
Tambarin Dimokuradiyya

‘Yan Siyasa Na Gwagwarmaya Ne Kadai Wajen Neman Mukami Ba Wai Don Talakawa Ba — Bafarawa

3 weeks ago
Gwamnoni 9 Da Har Yanzu Ba Su Babe Da Iyayen Gidansu Ba
Tambarin Dimokuradiyya

Jihohi Sun Samu Naira Tiriliyan 1 Na Kudaden Kananan Hukumomi A Zango Na Daya

4 weeks ago
2027: Baba-Ahmed Ya Bukaci Tinubu Ya Janye, Ya Bar Matasa Su Yi Takara 
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Babu Dan Takarar Da Zai Iya Cin Zabe Ba Tare Da Goyon Bayan Arewa Ba – Baba Ahmed

4 weeks ago
arewa
Tambarin Dimokuradiyya

Kawunan Shugabannin Arewa Sun Rabu Kan Siyasar 2027

4 weeks ago
Next Post
Sharhi: Shin Tinubu Zai Iya Kai Bantensa Bisa Yadda Ya Fara?

Sharhi: Shin Tinubu Zai Iya Kai Bantensa Bisa Yadda Ya Fara?

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Majalisar Dokokin Nijeriya Sun Bukaci Karin Albashi

Yadda ‘Yan Majalisa Ke Cusa Ayyuka Marasa Amfani A Kasafin Kuɗi – Rahoto

May 22, 2025
Wasu ‘Yan Siyasa Da Jami’an Tsaro Na Taimaka Wa Boko Haram – Zulum

Wasu ‘Yan Siyasa Da Jami’an Tsaro Na Taimaka Wa Boko Haram – Zulum

May 22, 2025
‘Yansanda Sun Tarwatsa Wuraren Haɗa Jabun Taki A Bauchi, An Cafke Mutum 5

‘Yansanda Sun Tarwatsa Wuraren Haɗa Jabun Taki A Bauchi, An Cafke Mutum 5

May 21, 2025
Kocin Super Eagle Ya Gayyaci Ahmed Musa Buga Gasar Kofin Unity A Landan

Kocin Super Eagle Ya Gayyaci Ahmed Musa Buga Gasar Kofin Unity A Landan

May 21, 2025
Farar Dabarar Da Tsoffin Masana’antu Ke Yi A Kasar Sin Don Tafiya Da Zamani

Farar Dabarar Da Tsoffin Masana’antu Ke Yi A Kasar Sin Don Tafiya Da Zamani

May 21, 2025
Tottenham Ta Doke Manchester United A Wasan Karshe Na Europa 

Tottenham Ta Doke Manchester United A Wasan Karshe Na Europa 

May 21, 2025
Kotu Ta Soke Umarnin Kwace Filin Asibitin Tiamin, Ta Umarci Gwamnatin Kano Ta Biya Diyyar ₦2.6bn

Kotu Ta Soke Umarnin Kwace Filin Asibitin Tiamin, Ta Umarci Gwamnatin Kano Ta Biya Diyyar ₦2.6bn

May 21, 2025
Shirye-shiryen Tinubu Suna Buɗe Hanyar Farfaɗowar Tattalin Arzikin Nijeriya – Minista

Shirye-shiryen Tinubu Suna Buɗe Hanyar Farfaɗowar Tattalin Arzikin Nijeriya – Minista

May 21, 2025
Salon “Kasa Daya Manufa Daya” Ya Dace Da “Ayyuka Goma” Na Hadin Gwiwa Da Afirka

Salon “Kasa Daya Manufa Daya” Ya Dace Da “Ayyuka Goma” Na Hadin Gwiwa Da Afirka

May 21, 2025
Sin Tana Da Karfi Wajen Tinkarar Hadari Da Kalubale A Fannoni Daban Daban

Sin Tana Da Karfi Wajen Tinkarar Hadari Da Kalubale A Fannoni Daban Daban

May 21, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.