ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, July 10, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Illar Kakaba Wa Majalisa Ta 10 Shugabanni Ga Gwamnatin Tinubu – Dattawan Arewa

by Yusuf Shuaibu
3 years ago
Majalisa

Kungiyar Dattawan Arewa (NEF) ta bayyana cewa kokarin kakaba shugabanci a majalisa 10 da ake shirin kaddamarwa ba zai harfar wa da gwamnatin shugaban kasa Bola Tinubu da mai ido ba.

Kakakin NEF, Hakeem Baba-Ahmed shi ya bayyana haka a wata hira da ya yi da gidan talabijin na Channels tb a ranar Talata.

  • Majalisar Dokokin Jihar Taraba Ta Bukaci Tinubu Ya Ayyana Dokar Ta-baci Kan Tsaro Jihar
  • Sin: Yin Katsa-landan Da Sanya Takunkumin Kashin Kai Ba Za Su Warware Batun Tsakiyar Afirka Ba

Hakeem ya ce, “Ba amfanin Shugaba Tinubu ba ne ya dora shugabannin a majalisar kasa. Ba ya cikin maslaha.

ADVERTISEMENT

“Abin da ya fi dacewa shi ne, Tinubu ya nisanta kansa daga zaben shugabanin majalisar dattawa da mataimakinsa,” in ji shi.

Kakakin NEF ya jaddada cewa a bar ‘yan majalisar dattawa da ta wakilai su yanke hukunci wajen zaben shugabanninsu ba tare da tsoma bakin shugaban kasa ba.

LABARAI MASU NASABA

Ci-ma-zaunen Ƴan Siyasa Ne Ke Tunanin Yin Maguɗi A Zaɓen 2027 – Makarfi

An Samu Ruɗani Kan Rashin Bayyana Jerin Ƴan Takarar Jam’iyyun Siyasa Na Zaɓen 2027

Ya ce, “Ya kamata a bar ‘yan majalisa su yanke hukunci kan wurin da shugabanci zai nufa. Wannan ita ce ra’ayina da na tsaya a kai. Ban da ra’ayin cewa sai shugabancin majalisa ya koma yankin arewa. Na ce akwai sauran abubuwan da ya kamata a yi la’akari da su.

“Idan ‘yan majalisa suka yanke hukunci cikin adalci, to shugabancin majalisa zai iya komawa kudu, mun tabbatar da haka. Sanna kuma zai iya zuwa arewa, babu wata matsala.”

Ya ce matsayin shugaban majalisar dattawa ana iya nada kowa kuma ana iya tsige shi.

Idan za a iya tuna jam’iyyar APC mai mulki ita ke da yawan kujeru a majalisar wakilai da suka kai 170 daga cikin kujeru 360 na zauren majalisar.

Babbar jam’iyyar adawa ta PDP ta zo ta biyu da kujeru sama da 100, jam’iyyar LP mai kujeru sama da 35, jam’iyyar NNPP ta samu kusan 20.

‘Yan majalisar APC da suka nuna sha’awarsu na zama shugaban majalisar wakilai dai sun hada da Benjamin Kalu, Ahmed Wase, Alhassan Ado-Doguwa, Yusuf Gagdi, Aliyu Betara, Tajudeen Abbas, Abdulraheem Olawuyi, Sani Jaji, Gimbiya Onuoha da dai sauransu.

Haka kuma a bangaren majalisar dattawa kuwa, masu sha’awar zama shugaban majalisar dattawa sun hada da Sanata Abdulaziz Yari, Orji Kalu, Godswill Akpabio da dai sauransu.

Sai dai kuma jam’iyyar APC ta tsayar da Akpabio daga yankin kudu maso kudu a matsayin shugaban majalisar dattawa da kuma Barau Jibrin daga yankin arewa maso yamma a matsayin mataimakin shugaban majalisar dattawa.

Jam’iyyar ta kuma tsayar da shugabancin majalisar wakilai zuwa arewa maso yamma wanda ta bai wa Abass, da mataimakin shugaban majalisar daga kudu maso gabas da ta bai wa Kalu.

Sai dai kuma hukuncin jam’iyyar ta gamu da rashin amincewa daga mafi yawancin ‘ya’yan jam’iyyar APC, inda suka bukaci a sake duba tsarin da zai shafi shiyyar arewa ta tsakiya ba wai matsayi biyu na yankin krewa maso yamma ba.

Hujjarsu ita ce arewa maso yamma sun bai wa shugaban kasa kuri’a mafi girma don haka ya cancanci a biya su diyya na kai shugabancin majalisar ga yankin.

Majalisa
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Ci-ma-zaunen Ƴan Siyasa Ne Ke Tunanin Yin Maguɗi A Zaɓen 2027 – Makarfi
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    An Samu Ruɗani Kan Rashin Bayyana Jerin Ƴan Takarar Jam’iyyun Siyasa Na Zaɓen 2027
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Rashin Tsaro Na Barazana Ga Zaben 2027 —Rahotanni
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku

MASU ALAKA

makarfi
Tambarin Dimokuradiyya

Ci-ma-zaunen Ƴan Siyasa Ne Ke Tunanin Yin Maguɗi A Zaɓen 2027 – Makarfi

June 26, 2026
Rashin Tsaro Na Barazana Ga Zaben 2027 —Rahotanni
Tambarin Dimokuradiyya

An Samu Ruɗani Kan Rashin Bayyana Jerin Ƴan Takarar Jam’iyyun Siyasa Na Zaɓen 2027

June 26, 2026
Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku
Tambarin Dimokuradiyya

Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku

June 19, 2026
Next Post
Sharhi: Shin Tinubu Zai Iya Kai Bantensa Bisa Yadda Ya Fara?

Sharhi: Shin Tinubu Zai Iya Kai Bantensa Bisa Yadda Ya Fara?

LABARAI MASU NASABA

Asusun IMF Ya Rage Hasashen Bunkasar Tattalin Arzikin Duniya, Ya Kuma Kara Na Sin

Asusun IMF Ya Rage Hasashen Bunkasar Tattalin Arzikin Duniya, Ya Kuma Kara Na Sin

July 9, 2026
Alkaluman Farashin Kayayyakin Masarufi Na Kasar Sin Sun Karu Da Kaso 1 A Watan Yuni

Alkaluman Farashin Kayayyakin Masarufi Na Kasar Sin Sun Karu Da Kaso 1 A Watan Yuni

July 9, 2026
‘Yansandan Jihohi Za Su Bai Wa Gwamnoni Cikakken Iko Wajen Yaƙi Da Matsalar Tsaro — Gwamna Dauda

‘Yansandan Jihohi Za Su Bai Wa Gwamnoni Cikakken Iko Wajen Yaƙi Da Matsalar Tsaro — Gwamna Dauda

July 9, 2026
Taron Intanet Na Sin Karo Na 25 Ya Bayyana Yadda Ake Amfani Da Fasahar AI A Rayuwar Yau Da Kullum

Taron Intanet Na Sin Karo Na 25 Ya Bayyana Yadda Ake Amfani Da Fasahar AI A Rayuwar Yau Da Kullum

July 9, 2026
Tunanin Xi Jinping kan JKS: Hikimar Mulki Ta Farfado Da Kasa Da Kuma Tasirinta A Duniya

Tunanin Xi Jinping kan JKS: Hikimar Mulki Ta Farfado Da Kasa Da Kuma Tasirinta A Duniya

July 9, 2026
Rashin Tsaro: Tinubu Ya Gana Da Shugabannin Hukumomin Tsaro

Rashin Tsaro: Tinubu Ya Gana Da Shugabannin Hukumomin Tsaro

July 9, 2026
Motoci Masu Aiki Da Lantarki Kirar Kasar Sin Na Kara Samun Tagomashi A Kasuwannin Duniya

Motoci Masu Aiki Da Lantarki Kirar Kasar Sin Na Kara Samun Tagomashi A Kasuwannin Duniya

July 9, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Ɗaga Albashin Sojoji Daga Naira 49,000 Zuwa Naira 100,000 – Ministan Tsaro

Gwamnatin Tarayya Ta Ɗaga Albashin Sojoji Daga Naira 49,000 Zuwa Naira 100,000 – Ministan Tsaro

July 9, 2026
An Gabatar Da Shirin Fadar Potala Ta Kafar CMG

An Gabatar Da Shirin Fadar Potala Ta Kafar CMG

July 9, 2026
kebbi

Makarantu Za Su Ci Gaba Da Zama A Rufe Har Sai Yanayin Tsaro Ya Inganta – Gwamnatin Kebbi

July 9, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.