• English
  • Business News
Saturday, September 13, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ina Da Yakinin Samun Nasara A Kotu -Dan Takarar Gwamnan APC A Bauchi

by Khalid Idris Doya
2 years ago
in Labarai
0
Ina Da Yakinin Samun Nasara A Kotu -Dan Takarar Gwamnan APC A Bauchi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Dan takarar Gwamnan Jihar Bauchi a zaben 2023 a jam’iyyar APC, Sadique Baba Abubakar, ya nuna kwarin guiwar cewa zai samu nasarar a kotun sauraren kararrakin zabe.

Abubakar ya ce a zaben da aka gudanar shi ne ya samu nasara kuma yana da tulin hujjojin da za su gabatar a gaban kotun sauraron kararrakin zabe da hakan zai kai a dawo masa da wadanda suka zabe shi kujerar.

  • Ranar Ma’aikata: NLC Ta Bukaci Daidaita Albashin Ma’aikata A Kebbi
  • NAFDAC Ta Haramta Shigo Da Indomie Saboda Zargin Sanya Ciwon Daji

A hirarsa da ‘yan jarida bayan dawowarsa daga tafiya a ranar Litinin a Bauchi, Sadique ya ce, sashin shari’a a kasar nan yanzu ya ingantu don haka yana da cikakken kwarin guiwar za su wanzar da adalci da gaskiya a tsakani.

“Nasara a hannun Allah ya ke. Mun tabbatar zalumci aka yi kuma da izinin Allah, Allah zai kwato hakkin jama’a. Sannan mun tabbatar yanayin shari’a na Nijeriya na da kyau don mutane ne adilai wadanda za su tabbatar da gaskiya.”

A cewarsa, “Muna godiya wa Allah (SWT) wanda ya ba mu dama muka dawo bayan mun fara wannan gwagwarmayar da muka sanya a gaba na tabbatar da cewa an kwato hakkin jama’a an maida musu.

Labarai Masu Nasaba

Etsu Nupe Ginshiƙin Zaman Lafiya Da Haɗin Kai Ne A Nijeriya — Ministan Yaɗa Labarai

Shugaban Rundunar Sojin Sama Ya Buƙaci Ɗaukar Matakin Yaƙi Da Barazanar Tsaro

“Wannan gwagwarmayar mun dauke shi kuma da izinin Allah, Allah zai ba mu nasara a kai.”

Ya gode wa jama’a bisa addu’o’in da ya ce sun yi masa musamman a lokacin azumi da kuma fatan alkairi da suke masa, kana ya kuma jinjina wa kokarin jam’iyyar APC da ta yi kuma take musu. Sai ya nemi masoya da magoya bayansa da su cigaba da kasance masu bin doka da oda har zuwa lokacin da kotu za ya saurari kararsa.

Abubakar ya tabbatar da cewa za su ci gaba da neman hakkinsu babu dare ko rana jar sai sun tabbatar sun kwace mulki, “Ina da kwarin guiwar Allah zai kwato wa jama’a hakkinsu domin Allah ya san abun da ya faru a lokacin zaben nan kuma mun tabbatar matakan da muka dauka za su fito da abubuwan da ake nema na ganin an kwato hakkin jama’a an dawo da shi.

“Na tabbatar da jama’anmu ba su bukatar cigaba da tsarin da ba a biyan albashi, tsarin da yara ke karatu a kasa alhalin ana nan ana gina manya-manyan ofisoshi na biliyoyi wanda ba shi ne ya dami al’umma ba.

“Saboda haka ganin yadda mutane suka ba mu hadin kai a ziyarar da muka kai kananan hukumomi muka ga ya wajaba a kanmu mu cigaba da wannan gwagwarmayar har sai mun tabbatar an kwato hakkin jama’a.”

Idan za ku tuna dai a zaben da aka fafata na 2023 da jam’iyyun siyasa daban-daban guda 14 suka shiga aka fafata da su, sakamakon ya nuna cewa Gwamnan da ke kan kujerar Bala Muhammad na jam’iyyar PDP ya samu nasarar tazarce da kuri’u 525, 280 yayin da abokin hamayyarsa na kusa-kusa Sadique Baba Abubakar ya tashi da kuri’u 432, 272 kamar yadda INEC ta shelanta. To sai dai Abubakar ya kalubanci sakamakon a gaban kotu.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: APCBauchiKotuPDPSiddiqueZaben Gwamna
ShareTweetSendShare
Previous Post

Ranar Ma’aikata: NLC Ta Bukaci Daidaita Albashin Ma’aikata A Kebbi

Next Post

Dalibin Islamiyya Ya Gina Gadar Miliyan 12.8 A Ogun

Related

Etsu Nupe Ginshiƙin Zaman Lafiya Da Haɗin Kai Ne A Nijeriya — Ministan Yaɗa Labarai
Labarai

Etsu Nupe Ginshiƙin Zaman Lafiya Da Haɗin Kai Ne A Nijeriya — Ministan Yaɗa Labarai

1 hour ago
Shugaban Rundunar Sojin Sama Ya Buƙaci Ɗaukar Matakin Yaƙi Da Barazanar Tsaro
Tsaro

Shugaban Rundunar Sojin Sama Ya Buƙaci Ɗaukar Matakin Yaƙi Da Barazanar Tsaro

2 hours ago
Sojoji Sun Kashe Ƙasurgumin Ɗan Ta’adda A Kogi
Manyan Labarai

Sojoji Sun Kashe Ƙasurgumin Ɗan Ta’adda A Kogi

2 hours ago
An Shirya Haɗin Gwiwa Da Hukumomi Don Magance Matsalar Ambaliyar Ruwa
Manyan Labarai

An Shirya Haɗin Gwiwa Da Hukumomi Don Magance Matsalar Ambaliyar Ruwa

3 hours ago
Majalisar Tarayya Ta Magantu Kan Gawar Da Aka Samu A Harabarta
Manyan Labarai

Majalisar Tarayya Ta Magantu Kan Gawar Da Aka Samu A Harabarta

4 hours ago
Gwamnatin Tarayya Ta Sanar Da Sabon Sharaɗi Na Buɗe Asusun Banki
Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Sanar Da Sabon Sharaɗi Na Buɗe Asusun Banki

5 hours ago
Next Post
Dalibin Islamiyya Ya Gina Gadar Miliyan 12.8 A Ogun

Dalibin Islamiyya Ya Gina Gadar Miliyan 12.8 A Ogun

LABARAI MASU NASABA

Aleksandar Vucic: Serbia Na Goyon Bayan Shawarar Kula Da Harkokin Duniya Da Kasar Sin Ta Gabatar

Aleksandar Vucic: Serbia Na Goyon Bayan Shawarar Kula Da Harkokin Duniya Da Kasar Sin Ta Gabatar

September 13, 2025
Etsu Nupe Ginshiƙin Zaman Lafiya Da Haɗin Kai Ne A Nijeriya — Ministan Yaɗa Labarai

Etsu Nupe Ginshiƙin Zaman Lafiya Da Haɗin Kai Ne A Nijeriya — Ministan Yaɗa Labarai

September 13, 2025
Shugaban Rundunar Sojin Sama Ya Buƙaci Ɗaukar Matakin Yaƙi Da Barazanar Tsaro

Shugaban Rundunar Sojin Sama Ya Buƙaci Ɗaukar Matakin Yaƙi Da Barazanar Tsaro

September 13, 2025
Sojoji Sun Kashe Ƙasurgumin Ɗan Ta’adda A Kogi

Sojoji Sun Kashe Ƙasurgumin Ɗan Ta’adda A Kogi

September 13, 2025
An Shirya Haɗin Gwiwa Da Hukumomi Don Magance Matsalar Ambaliyar Ruwa

An Shirya Haɗin Gwiwa Da Hukumomi Don Magance Matsalar Ambaliyar Ruwa

September 13, 2025
Majalisar Tarayya Ta Magantu Kan Gawar Da Aka Samu A Harabarta

Majalisar Tarayya Ta Magantu Kan Gawar Da Aka Samu A Harabarta

September 13, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Sanar Da Sabon Sharaɗi Na Buɗe Asusun Banki

Gwamnatin Tarayya Ta Sanar Da Sabon Sharaɗi Na Buɗe Asusun Banki

September 13, 2025
PDP Ta Dage Kan Gudanar Da Taronta Duk Da Sabbin Sharuɗɗan Da Ɓangaren Wike Ya Gindaya

PDP Ta Dage Kan Gudanar Da Taronta Duk Da Sabbin Sharuɗɗan Da Ɓangaren Wike Ya Gindaya

September 13, 2025
Ban Taɓa Nadamar Shiga Fim Ba – Kabiru Nakwango

Ban Taɓa Nadamar Shiga Fim Ba – Kabiru Nakwango

September 13, 2025
Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina

Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina

September 13, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.