• English
  • Business News
Wednesday, June 4, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ina Da Yakinin Samun Nasara A Kotu -Dan Takarar Gwamnan APC A Bauchi

by Khalid Idris Doya
2 years ago
in Labarai
0
Ina Da Yakinin Samun Nasara A Kotu -Dan Takarar Gwamnan APC A Bauchi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Dan takarar Gwamnan Jihar Bauchi a zaben 2023 a jam’iyyar APC, Sadique Baba Abubakar, ya nuna kwarin guiwar cewa zai samu nasarar a kotun sauraren kararrakin zabe.

Abubakar ya ce a zaben da aka gudanar shi ne ya samu nasara kuma yana da tulin hujjojin da za su gabatar a gaban kotun sauraron kararrakin zabe da hakan zai kai a dawo masa da wadanda suka zabe shi kujerar.

  • Ranar Ma’aikata: NLC Ta Bukaci Daidaita Albashin Ma’aikata A Kebbi
  • NAFDAC Ta Haramta Shigo Da Indomie Saboda Zargin Sanya Ciwon Daji

A hirarsa da ‘yan jarida bayan dawowarsa daga tafiya a ranar Litinin a Bauchi, Sadique ya ce, sashin shari’a a kasar nan yanzu ya ingantu don haka yana da cikakken kwarin guiwar za su wanzar da adalci da gaskiya a tsakani.

“Nasara a hannun Allah ya ke. Mun tabbatar zalumci aka yi kuma da izinin Allah, Allah zai kwato hakkin jama’a. Sannan mun tabbatar yanayin shari’a na Nijeriya na da kyau don mutane ne adilai wadanda za su tabbatar da gaskiya.”

A cewarsa, “Muna godiya wa Allah (SWT) wanda ya ba mu dama muka dawo bayan mun fara wannan gwagwarmayar da muka sanya a gaba na tabbatar da cewa an kwato hakkin jama’a an maida musu.

Labarai Masu Nasaba

Zulum Ya Yaba Wa Sojoji Kan Kashe Babban Kwamandan ISWAP Abu Fatima

‘Yansanda A Kano Sun GargaÉ—i Sarki Sanusi II Kan Fitowa Hawan Sallah

“Wannan gwagwarmayar mun dauke shi kuma da izinin Allah, Allah zai ba mu nasara a kai.”

Ya gode wa jama’a bisa addu’o’in da ya ce sun yi masa musamman a lokacin azumi da kuma fatan alkairi da suke masa, kana ya kuma jinjina wa kokarin jam’iyyar APC da ta yi kuma take musu. Sai ya nemi masoya da magoya bayansa da su cigaba da kasance masu bin doka da oda har zuwa lokacin da kotu za ya saurari kararsa.

Abubakar ya tabbatar da cewa za su ci gaba da neman hakkinsu babu dare ko rana jar sai sun tabbatar sun kwace mulki, “Ina da kwarin guiwar Allah zai kwato wa jama’a hakkinsu domin Allah ya san abun da ya faru a lokacin zaben nan kuma mun tabbatar matakan da muka dauka za su fito da abubuwan da ake nema na ganin an kwato hakkin jama’a an dawo da shi.

“Na tabbatar da jama’anmu ba su bukatar cigaba da tsarin da ba a biyan albashi, tsarin da yara ke karatu a kasa alhalin ana nan ana gina manya-manyan ofisoshi na biliyoyi wanda ba shi ne ya dami al’umma ba.

“Saboda haka ganin yadda mutane suka ba mu hadin kai a ziyarar da muka kai kananan hukumomi muka ga ya wajaba a kanmu mu cigaba da wannan gwagwarmayar har sai mun tabbatar an kwato hakkin jama’a.”

Idan za ku tuna dai a zaben da aka fafata na 2023 da jam’iyyun siyasa daban-daban guda 14 suka shiga aka fafata da su, sakamakon ya nuna cewa Gwamnan da ke kan kujerar Bala Muhammad na jam’iyyar PDP ya samu nasarar tazarce da kuri’u 525, 280 yayin da abokin hamayyarsa na kusa-kusa Sadique Baba Abubakar ya tashi da kuri’u 432, 272 kamar yadda INEC ta shelanta. To sai dai Abubakar ya kalubanci sakamakon a gaban kotu.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: APCBauchiKotuPDPSiddiqueZaben Gwamna
ShareTweetSendShare
Previous Post

Ranar Ma’aikata: NLC Ta Bukaci Daidaita Albashin Ma’aikata A Kebbi

Next Post

Dalibin Islamiyya Ya Gina Gadar Miliyan 12.8 A Ogun

Related

Ambaliya: Gwamna Zulum Ya Kaddamar Da Rabon Kayan Agaji A Borno
Manyan Labarai

Zulum Ya Yaba Wa Sojoji Kan Kashe Babban Kwamandan ISWAP Abu Fatima

2 hours ago
Sanusi
Manyan Labarai

‘Yansanda A Kano Sun GargaÉ—i Sarki Sanusi II Kan Fitowa Hawan Sallah

13 hours ago
Sallah: Gwamnatin Kebbi Ta Raba Naira Miliyan 337 Ga Mata 11,229 
Labarai

Sallah: Gwamnatin Kebbi Ta Raba Naira Miliyan 337 Ga Mata 11,229 

16 hours ago
Yanzu-yanzu: JUSUN Ta Dakatar Da Yajin Aikin Da Fara A Faɗin Ƙasa Baki Ɗaya
Manyan Labarai

Yanzu-yanzu: JUSUN Ta Dakatar Da Yajin Aikin Da Fara A Faɗin Ƙasa Baki Ɗaya

16 hours ago
Mataimakin Kakakin Majalisar Dokokin Ondo Da Shugaban Masu Rinjaye Sun Yi Murabus
Manyan Labarai

Mataimakin Kakakin Majalisar Dokokin Ondo Da Shugaban Masu Rinjaye Sun Yi Murabus

19 hours ago
Shehu Sani Ya Buƙaci Shugabannin Arewa Su Mara Wa Tinubu Baya Ya Yi Shekaru 8 A Kan Mulki
Manyan Labarai

Shehu Sani Ya Buƙaci Shugabannin Arewa Su Mara Wa Tinubu Baya Ya Yi Shekaru 8 A Kan Mulki

22 hours ago
Next Post
Dalibin Islamiyya Ya Gina Gadar Miliyan 12.8 A Ogun

Dalibin Islamiyya Ya Gina Gadar Miliyan 12.8 A Ogun

LABARAI MASU NASABA

Ambaliya: Gwamna Zulum Ya Kaddamar Da Rabon Kayan Agaji A Borno

Zulum Ya Yaba Wa Sojoji Kan Kashe Babban Kwamandan ISWAP Abu Fatima

June 4, 2025
Manufar Bude Kofa Ta Shaida Niyyar Sin Ta Ingiza Dunkulewar Duniya

Manufar Bude Kofa Ta Shaida Niyyar Sin Ta Ingiza Dunkulewar Duniya

June 3, 2025
Kocin Inter Milan Simone Inzaghi Ya Bar Kungiyar Kwanaki Biyu Bayan Rashin Nasara A Hannun PSG

Kocin Inter Milan Simone Inzaghi Ya Bar Kungiyar Kwanaki Biyu Bayan Rashin Nasara A Hannun PSG

June 3, 2025
Sin Ta Yi Fatali Da Ikirarin Amurka Cewa Ta Karya Yarjejeniyar Tattaunawar Geneva

Sin Ta Yi Fatali Da Ikirarin Amurka Cewa Ta Karya Yarjejeniyar Tattaunawar Geneva

June 3, 2025
Karuwar Darajar Sana’ar Samar Da Kayan Laturoni Da Dangoginsu a Sin Cikin Watanni 4 Na Farkon Bana Ya Karu Da 11.3% 

Karuwar Darajar Sana’ar Samar Da Kayan Laturoni Da Dangoginsu a Sin Cikin Watanni 4 Na Farkon Bana Ya Karu Da 11.3% 

June 3, 2025
Sanusi

‘Yansanda A Kano Sun GargaÉ—i Sarki Sanusi II Kan Fitowa Hawan Sallah

June 3, 2025
Masani Kwadifwa: Kasar Sin Ce Mai Kare Tabbatuwar Adalci A Duniya

Masani Kwadifwa: Kasar Sin Ce Mai Kare Tabbatuwar Adalci A Duniya

June 3, 2025
An Samu Karuwar Kaso 2.7 Na Yawan Tafiye-Tafiye Zuwa Ketare Yayin Hutun Bikin Dragon Boat Na Kasar Sin

An Samu Karuwar Kaso 2.7 Na Yawan Tafiye-Tafiye Zuwa Ketare Yayin Hutun Bikin Dragon Boat Na Kasar Sin

June 3, 2025
Sallah: Gwamnatin Kebbi Ta Raba Naira Miliyan 337 Ga Mata 11,229 

Sallah: Gwamnatin Kebbi Ta Raba Naira Miliyan 337 Ga Mata 11,229 

June 3, 2025
Yanzu-yanzu: JUSUN Ta Dakatar Da Yajin Aikin Da Fara A Faɗin Ƙasa Baki Ɗaya

Yanzu-yanzu: JUSUN Ta Dakatar Da Yajin Aikin Da Fara A Faɗin Ƙasa Baki Ɗaya

June 3, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.