• English
  • Business News
Sunday, June 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ina Gaskiyar Bayyanar Aljanun Aliens A Jihar Katsina?

by El-Zaharadeen Umar
2 years ago
in Rahotonni
0
Ina Gaskiyar Bayyanar Aljanun Aliens A Jihar Katsina?
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Batun bayyana wasu halittu da ake dangantawa da aljanun aliens a Jihar Katsina yana cikin abubuwan da suka dauki hankali a cikin wannan makon da ya gabata.
Kafafen sada zumunta na soshiyal midiya sun dauki zafi so sai ya yi bayyana wannan labari da masana suka ce babu wani abu mai kama da haka da ya shigo cikin kwaryar Katsina, abu ne kawai na wasu marasa kishin da hangen nesa.

Bidiyon halittar da ake yi wa lakabi da aljannun Aliens sun mamaye duk wasu shafukan sada zumunta tare da bayanin cewa wadannan Aljanu sun bayyana ne a garin Katsina, sai dai kuma babu wanda zai gaya maka ya gamsu ko kuma ya ga wanda ya gansu.

  • Ya Zuwa Karshen Maris Yawan Kudaden Musayar Ketare Da Sin Take Da Su Ya Kai Dala Biliyan 3183.9

Jama’a da dama a jihar Katsina sun sha amsa kira daga wasu jihohi da kasashe dangane da wannan lamari, sai dai mafi yawan amsar da ake baiwa masu neman karin bayani ita ce, muma a soshiyal midiya muka gani kamar yadda kuka gani.

Kamar yadda Muhammad Aminu Kabir ya bayyana cewa abinda ya da ce mutane su tuna shine a irin wannan lokacin Manzon Allah (S) ya gaya mana cewa a lokacin Azumi ana daure Aljannu, wannan kadai ya isa jama’a su gane cewa wannan abun ba gaskiya bane.

Ya kara da cewa abu na biyu kuma ga duk wanda ya kalli bidiyon zai iya ganin hannun wani Bature wanda shi ya dauki bidiyon yayin da shi kuma wanda yake magana da Hausa faifan murya ne aka dora wanda ya yi dai dai da abinda ke faruwa cikin bidiyon.

Labarai Masu Nasaba

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

Tsadar Rayuwa: Yadda Al’umma Suka Yi Sallah Cikin Kunci

“Hatta ma wata hallita ta Aliens da ake magana akanta tsawon lokaci a zahirance ma babu ita shirin fim ne na turawa, dan haka mutane suma daina sauraren wannan batun ko yada wadannan.

Ganin yadda wannan al’amari ke daukar wani sabon salo na tsoratar da jama’a musamman Katsina da ke fama da matsalolin tsaro yasa rundunar ‘Yan sanda ta jihar Katsina yin magana dangane da wannan tirka -tirka
Ba tare da bata lokaci ba kakakin rundunar ‘yan sanda na jihar Katsina CSP Gambo Isah ya karyata wannan batu da ke yawo a kafafen sada zumunta na soshiyal midiya.

Bayanin hakan na kunshe a cikin wata samarwa da rundunar ta raba wa manema labarai a Katsina inda ta ce babu kamshi gaskiya a wannan lamari.

Sanarwar ta ce an jawo hankalin rundunar ‘Yan sanda ta Jihar Katsina ne a kan wannan faifan bidiyo da ake yadawa cewa wasu aljanu sun shigo garin Katsina.

Sanarwar ta ce duk abinda aka gani acikin wannan faifan bidiyo karya ce tsagwaranta da wasu marasa kishi suka kirkira domin tayar da hankali jama’a a irin wannan lokaci.

Kamar yadda rundunar ‘Yan sanda ta ce wannan wani yunkuri ne na neman tada zaune tsaye da kuma kawo cikas a dorewar zaman lafiya da ake da shi a jihar Katsina
Kakakin rundunar ‘Yan sanda CSP Gambo Isah ya ce al’umma su yi watsi da wannan faifan bidiyo kuma tuni sun baza komar su domin damke duk wanda aka kama yana da hannu wajan kitsa wannan al’amari.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

NALDA Ta Samar Da Makarantun Horas Da Manoma A Ogun, Katsina, Abiya Da Borno

Next Post

Ra’ayina A Kan Yaduwar Cacar Bet9ja A Tsakanin Matasa

Related

Aliens
Rahotonni

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

19 hours ago
Tsadar Rayuwa: Yadda Al’umma Suka Yi Sallah Cikin Kunci
Rahotonni

Tsadar Rayuwa: Yadda Al’umma Suka Yi Sallah Cikin Kunci

2 days ago
Ana Fargabar Boko Haram Ta Kara Mamaye Wasu Kananan Hukumomi A Borno
Rahotonni

Ana Fargabar Boko Haram Ta Kara Mamaye Wasu Kananan Hukumomi A Borno

1 week ago
Kokarin Minista Tuggar Na Mayar Da Hijirar Masana Daga Nijeriya Zuwa Kasashen Waje Alhairi
Rahotonni

Kokarin Minista Tuggar Na Mayar Da Hijirar Masana Daga Nijeriya Zuwa Kasashen Waje Alhairi

1 week ago
Faduwar Jarrabawar JAMB Ta Tayar Da Bukatar Neman Sake Fasalin Hukumar
Rahotonni

Faduwar Jarrabawar JAMB Ta Tayar Da Bukatar Neman Sake Fasalin Hukumar

2 weeks ago
Gwamna Umar Namadi Ya Dauki Matakan Kai Jihar Jigawa Babban Matsayi
Rahotonni

Gwamna Umar Namadi Ya Dauki Matakan Kai Jihar Jigawa Babban Matsayi

2 months ago
Next Post
Ra’ayina A Kan Yaduwar Cacar Bet9ja A Tsakanin Matasa

Ra'ayina A Kan Yaduwar Cacar Bet9ja A Tsakanin Matasa

LABARAI MASU NASABA

Yadda Man Bilicin Ke Yi Wa Fatar Mutum Illa

Yadda Man Bilicin Ke Yi Wa Fatar Mutum Illa

June 8, 2025
An Daure ‘Yan Nijeriya Uku Shekaru 15 A Bisa Laifin Zamba A Indiya

An Daure ‘Yan Nijeriya Uku Shekaru 15 A Bisa Laifin Zamba A Indiya

June 8, 2025
Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

June 7, 2025
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

An Kama Magidanci A Bauchi Bisa Zargin Lalata Da Agolarsa

June 7, 2025
Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

June 7, 2025
Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

June 7, 2025
Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

June 7, 2025
Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

June 7, 2025
Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

June 7, 2025
Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

June 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.