• English
  • Business News
Thursday, October 16, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ina Gaskiyar Bayyanar Aljanun Aliens A Jihar Katsina?

by El-Zaharadeen Umar
3 years ago
Aliens

Batun bayyana wasu halittu da ake dangantawa da aljanun aliens a Jihar Katsina yana cikin abubuwan da suka dauki hankali a cikin wannan makon da ya gabata.
Kafafen sada zumunta na soshiyal midiya sun dauki zafi so sai ya yi bayyana wannan labari da masana suka ce babu wani abu mai kama da haka da ya shigo cikin kwaryar Katsina, abu ne kawai na wasu marasa kishin da hangen nesa.

Bidiyon halittar da ake yi wa lakabi da aljannun Aliens sun mamaye duk wasu shafukan sada zumunta tare da bayanin cewa wadannan Aljanu sun bayyana ne a garin Katsina, sai dai kuma babu wanda zai gaya maka ya gamsu ko kuma ya ga wanda ya gansu.

  • Ya Zuwa Karshen Maris Yawan Kudaden Musayar Ketare Da Sin Take Da Su Ya Kai Dala Biliyan 3183.9

Jama’a da dama a jihar Katsina sun sha amsa kira daga wasu jihohi da kasashe dangane da wannan lamari, sai dai mafi yawan amsar da ake baiwa masu neman karin bayani ita ce, muma a soshiyal midiya muka gani kamar yadda kuka gani.

Kamar yadda Muhammad Aminu Kabir ya bayyana cewa abinda ya da ce mutane su tuna shine a irin wannan lokacin Manzon Allah (S) ya gaya mana cewa a lokacin Azumi ana daure Aljannu, wannan kadai ya isa jama’a su gane cewa wannan abun ba gaskiya bane.

Ya kara da cewa abu na biyu kuma ga duk wanda ya kalli bidiyon zai iya ganin hannun wani Bature wanda shi ya dauki bidiyon yayin da shi kuma wanda yake magana da Hausa faifan murya ne aka dora wanda ya yi dai dai da abinda ke faruwa cikin bidiyon.

LABARAI MASU NASABA

Masana Sun Bayyana Yadda Za A Magance Ficewar Kamfanoni Da Masana’antu Daga Nijeriya

Ranar Malamai Ta Duniya: Rashin Kulawa Ke Sa Malamai Barin Aiki

“Hatta ma wata hallita ta Aliens da ake magana akanta tsawon lokaci a zahirance ma babu ita shirin fim ne na turawa, dan haka mutane suma daina sauraren wannan batun ko yada wadannan.

Ganin yadda wannan al’amari ke daukar wani sabon salo na tsoratar da jama’a musamman Katsina da ke fama da matsalolin tsaro yasa rundunar ‘Yan sanda ta jihar Katsina yin magana dangane da wannan tirka -tirka
Ba tare da bata lokaci ba kakakin rundunar ‘yan sanda na jihar Katsina CSP Gambo Isah ya karyata wannan batu da ke yawo a kafafen sada zumunta na soshiyal midiya.

Bayanin hakan na kunshe a cikin wata samarwa da rundunar ta raba wa manema labarai a Katsina inda ta ce babu kamshi gaskiya a wannan lamari.

Sanarwar ta ce an jawo hankalin rundunar ‘Yan sanda ta Jihar Katsina ne a kan wannan faifan bidiyo da ake yadawa cewa wasu aljanu sun shigo garin Katsina.

Sanarwar ta ce duk abinda aka gani acikin wannan faifan bidiyo karya ce tsagwaranta da wasu marasa kishi suka kirkira domin tayar da hankali jama’a a irin wannan lokaci.

Kamar yadda rundunar ‘Yan sanda ta ce wannan wani yunkuri ne na neman tada zaune tsaye da kuma kawo cikas a dorewar zaman lafiya da ake da shi a jihar Katsina
Kakakin rundunar ‘Yan sanda CSP Gambo Isah ya ce al’umma su yi watsi da wannan faifan bidiyo kuma tuni sun baza komar su domin damke duk wanda aka kama yana da hannu wajan kitsa wannan al’amari.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Masana Sun Bayyana Yadda Za A Magance Ficewar Kamfanoni Da Masana’antu Daga Nijeriya
Rahotonni

Masana Sun Bayyana Yadda Za A Magance Ficewar Kamfanoni Da Masana’antu Daga Nijeriya

October 11, 2025
Ranar Malamai Ta Duniya: Rashin Kulawa Ke Sa Malamai Barin Aiki
Rahotonni

Ranar Malamai Ta Duniya: Rashin Kulawa Ke Sa Malamai Barin Aiki

October 11, 2025
Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce
Manyan Labarai

Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

October 4, 2025
Next Post
Ra’ayina A Kan Yaduwar Cacar Bet9ja A Tsakanin Matasa

Ra'ayina A Kan Yaduwar Cacar Bet9ja A Tsakanin Matasa

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Za Ta Tallafa Wa Fursunoni Bayan Kammala Zaman Kurkuku

Gwamnatin Tarayya Za Ta Tallafa Wa Fursunoni Bayan Kammala Zaman Kurkuku

October 16, 2025
Amupitan Ya Isa Majalisar Dattawa Domin Tantance Shi A Matsayin Sabon Shugaban INEC

Amupitan Ya Isa Majalisar Dattawa Domin Tantance Shi A Matsayin Sabon Shugaban INEC

October 16, 2025
Majalisar Dattawa Ta Fara Tantance Amupitan A Matsayin Sabon Shugaban INEC

Majalisar Dattawa Ta Fara Tantance Amupitan A Matsayin Sabon Shugaban INEC

October 16, 2025
An Dakatar Da Tashi Da Saukar Jirage A Kenya Don Karɓar Gawar Raila Odinga

An Dakatar Da Tashi Da Saukar Jirage A Kenya Don Karɓar Gawar Raila Odinga

October 16, 2025
Gwamnan Edo Ya Umarci Kwamishinoni Su Riƙa Sanya Hular Tinubu

Gwamnan Edo Ya Umarci Kwamishinoni Su Riƙa Sanya Hular Tinubu

October 16, 2025
Baba-Ahmed Ya Zargi El-Rufai Da APC Kan Haifar Da Rashin Tsaro Don Neman Mulki

Baba-Ahmed Ya Zargi El-Rufai Da APC Kan Haifar Da Rashin Tsaro Don Neman Mulki

October 16, 2025
Jami’an FRSC Sun Mayar Da N6.2m Da Suka Tsinta Bayan Aukuwar Hatsarin Mota A Katsina

Jami’an FRSC Sun Mayar Da N6.2m Da Suka Tsinta Bayan Aukuwar Hatsarin Mota A Katsina

October 16, 2025
An Kashe Mutum 13 A Wasu Sabbin Hare-Hare A Ƙauyukan Filato

An Kashe Mutum 13 A Wasu Sabbin Hare-Hare A Ƙauyukan Filato

October 16, 2025
Sauya Sheƙa: Diri Da Wasu Na Guje Wa Matsalolin Da Suka Ƙirƙiro – Dickson

Sauya Sheƙa: Diri Da Wasu Na Guje Wa Matsalolin Da Suka Ƙirƙiro – Dickson

October 16, 2025
Sashen Cinikayyar Kamfanonin Sarrafa Hajoji Na Sin Ya Bunkasa Da Kaso 4.7 Bisa Dari Cikin Watanni Tara Na Farkon Shekarar Nan

Sashen Cinikayyar Kamfanonin Sarrafa Hajoji Na Sin Ya Bunkasa Da Kaso 4.7 Bisa Dari Cikin Watanni Tara Na Farkon Shekarar Nan

October 15, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.