• Leadership Hausa
Wednesday, December 6, 2023
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ina Gaskiyar Bayyanar Aljanun Aliens A Jihar Katsina?

by El-Zaharadeen Umar
8 months ago
in Rahotonni
0
Ina Gaskiyar Bayyanar Aljanun Aliens A Jihar Katsina?
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Batun bayyana wasu halittu da ake dangantawa da aljanun aliens a Jihar Katsina yana cikin abubuwan da suka dauki hankali a cikin wannan makon da ya gabata.
Kafafen sada zumunta na soshiyal midiya sun dauki zafi so sai ya yi bayyana wannan labari da masana suka ce babu wani abu mai kama da haka da ya shigo cikin kwaryar Katsina, abu ne kawai na wasu marasa kishin da hangen nesa.

Bidiyon halittar da ake yi wa lakabi da aljannun Aliens sun mamaye duk wasu shafukan sada zumunta tare da bayanin cewa wadannan Aljanu sun bayyana ne a garin Katsina, sai dai kuma babu wanda zai gaya maka ya gamsu ko kuma ya ga wanda ya gansu.

  • Ya Zuwa Karshen Maris Yawan Kudaden Musayar Ketare Da Sin Take Da Su Ya Kai Dala Biliyan 3183.9

Jama’a da dama a jihar Katsina sun sha amsa kira daga wasu jihohi da kasashe dangane da wannan lamari, sai dai mafi yawan amsar da ake baiwa masu neman karin bayani ita ce, muma a soshiyal midiya muka gani kamar yadda kuka gani.

Kamar yadda Muhammad Aminu Kabir ya bayyana cewa abinda ya da ce mutane su tuna shine a irin wannan lokacin Manzon Allah (S) ya gaya mana cewa a lokacin Azumi ana daure Aljannu, wannan kadai ya isa jama’a su gane cewa wannan abun ba gaskiya bane.

Ya kara da cewa abu na biyu kuma ga duk wanda ya kalli bidiyon zai iya ganin hannun wani Bature wanda shi ya dauki bidiyon yayin da shi kuma wanda yake magana da Hausa faifan murya ne aka dora wanda ya yi dai dai da abinda ke faruwa cikin bidiyon.

Labarai Masu Nasaba

Firimiyar Ingila: Man City Za Ta Karbi Bakuncin Liverpool A Etihad

Babban Masallacin Adogba: Sultan Da Makinde Sun Kafa Turbar Kawar Da Bambancin Kabilanci Da Na Addini A Nijeriya

“Hatta ma wata hallita ta Aliens da ake magana akanta tsawon lokaci a zahirance ma babu ita shirin fim ne na turawa, dan haka mutane suma daina sauraren wannan batun ko yada wadannan.

Ganin yadda wannan al’amari ke daukar wani sabon salo na tsoratar da jama’a musamman Katsina da ke fama da matsalolin tsaro yasa rundunar ‘Yan sanda ta jihar Katsina yin magana dangane da wannan tirka -tirka
Ba tare da bata lokaci ba kakakin rundunar ‘yan sanda na jihar Katsina CSP Gambo Isah ya karyata wannan batu da ke yawo a kafafen sada zumunta na soshiyal midiya.

Bayanin hakan na kunshe a cikin wata samarwa da rundunar ta raba wa manema labarai a Katsina inda ta ce babu kamshi gaskiya a wannan lamari.

Sanarwar ta ce an jawo hankalin rundunar ‘Yan sanda ta Jihar Katsina ne a kan wannan faifan bidiyo da ake yadawa cewa wasu aljanu sun shigo garin Katsina.

Sanarwar ta ce duk abinda aka gani acikin wannan faifan bidiyo karya ce tsagwaranta da wasu marasa kishi suka kirkira domin tayar da hankali jama’a a irin wannan lokaci.

Kamar yadda rundunar ‘Yan sanda ta ce wannan wani yunkuri ne na neman tada zaune tsaye da kuma kawo cikas a dorewar zaman lafiya da ake da shi a jihar Katsina
Kakakin rundunar ‘Yan sanda CSP Gambo Isah ya ce al’umma su yi watsi da wannan faifan bidiyo kuma tuni sun baza komar su domin damke duk wanda aka kama yana da hannu wajan kitsa wannan al’amari.

ShareTweetSendShare
Previous Post

NALDA Ta Samar Da Makarantun Horas Da Manoma A Ogun, Katsina, Abiya Da Borno

Next Post

Ra’ayina A Kan Yaduwar Cacar Bet9ja A Tsakanin Matasa

Related

Firimiyar Ingila: Man City Za Ta Karbi Bakuncin Liverpool A Etihad
Rahotonni

Firimiyar Ingila: Man City Za Ta Karbi Bakuncin Liverpool A Etihad

2 weeks ago
Babban Masallacin Adogba: Sultan Da Makinde Sun Kafa Turbar Kawar Da Bambancin Kabilanci Da Na Addini A Nijeriya
Rahotonni

Babban Masallacin Adogba: Sultan Da Makinde Sun Kafa Turbar Kawar Da Bambancin Kabilanci Da Na Addini A Nijeriya

2 weeks ago
‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutane 1,127, Sun Sace 518 A Watan Oktoba – Rahoto
Rahotonni

‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutane 1,127, Sun Sace 518 A Watan Oktoba – Rahoto

3 weeks ago
Abubuwan Da Ke Saurin Kashe Soyayya A Zuciyar Maigida
Rahotonni

Abubuwan Da Ke Saurin Kashe Soyayya A Zuciyar Maigida

1 month ago
Manyan Ayyukan Da Ke Gaban Sabon Gwamnan Babban Bankin Nijeriya
Rahotonni

Tsarin Canji Na Bai-daya Hanya Ce Ta Tsaftace Kasuwar Shinku

1 month ago
Yadda NPA Ta Bunkasa Hanyoyin Tara Kudaden Shiga Da Inganta Fitar Da Kaya Waje
Rahotonni

Yadda NPA Ta Bunkasa Hanyoyin Tara Kudaden Shiga Da Inganta Fitar Da Kaya Waje

1 month ago
Next Post
Ra’ayina A Kan Yaduwar Cacar Bet9ja A Tsakanin Matasa

Ra'ayina A Kan Yaduwar Cacar Bet9ja A Tsakanin Matasa

LABARAI MASU NASABA

An Bayyana Rawar Da Kasar Sin Ta Taka Kan Sauyin Yanayi Yayin Taron COP28

An Bayyana Rawar Da Kasar Sin Ta Taka Kan Sauyin Yanayi Yayin Taron COP28

December 5, 2023
Taron COP28: Ba Sharholiya Ce Ta Kai Tinubu Da Tawagarsa Dubai ba – Ministan Yada Labarai 

Taron COP28: Ba Sharholiya Ce Ta Kai Tinubu Da Tawagarsa Dubai ba – Ministan Yada Labarai 

December 5, 2023
Kungiyar Jam’iyyatu Ansariddeen Attajjaniyya Ta Gindaya Sharudda 5 Bisa Kisan Masu Maulidi A Kaduna 

Kungiyar Jam’iyyatu Ansariddeen Attajjaniyya Ta Gindaya Sharudda 5 Bisa Kisan Masu Maulidi A Kaduna 

December 5, 2023
Sin Ta Sake Zama Memba A Rukunin A A Kungiyar IMO

Sin Ta Sake Zama Memba A Rukunin A A Kungiyar IMO

December 5, 2023
Wang Yi Ya Halarci Bikin Bude Taron Karawa Juna Sani Na Tunawa Da Cika Shekaru 75 Da Wallafa Sanarwa Kan Hakkin Dan Adam Na Duniya

Wang Yi Ya Halarci Bikin Bude Taron Karawa Juna Sani Na Tunawa Da Cika Shekaru 75 Da Wallafa Sanarwa Kan Hakkin Dan Adam Na Duniya

December 5, 2023
Kasar Sin: Yawan Kunshin Kayayyaki Da Aka Isar A Kasar Ya Kafa Wani Sabon Tarihi

Kasar Sin: Yawan Kunshin Kayayyaki Da Aka Isar A Kasar Ya Kafa Wani Sabon Tarihi

December 5, 2023
Sin Ta Yi Amfani Da Rokar CERES-1 Y9 Wajen Harba Sabbin Taurarin Dan Adam 

Sin Ta Yi Amfani Da Rokar CERES-1 Y9 Wajen Harba Sabbin Taurarin Dan Adam 

December 5, 2023
Babban Hafsan Sojin Kasa Ya Ziyarci Wurin Da Aka Kai Harin Bam A Kaduna Da Asibitin Da Ake Kula Da Masu Raunin

Babban Hafsan Sojin Kasa Ya Ziyarci Wurin Da Aka Kai Harin Bam A Kaduna Da Asibitin Da Ake Kula Da Masu Raunin

December 5, 2023
Jami’in Diflomasiyyar Falasdinu: PA Ta Godewa Kasar Sin Bisa Aikewa Da Agaji Ga ’Yan Gaza Cikin Sa’o’in Bukata

Jami’in Diflomasiyyar Falasdinu: PA Ta Godewa Kasar Sin Bisa Aikewa Da Agaji Ga ’Yan Gaza Cikin Sa’o’in Bukata

December 5, 2023
Sheikh Dahiru Bauchi Ya Bukaci A Gudanar Da Bincike Kan Kisan Masu Maulidi A Kaduna

Sheikh Dahiru Bauchi Ya Bukaci A Gudanar Da Bincike Kan Kisan Masu Maulidi A Kaduna

December 5, 2023
Advertise with us

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.