• English
  • Business News
Saturday, September 20, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

INEC Ta Bukaci Jam’iyyu Da ‘Yan Takara Su Wanzar Da Zaman Lafiya Kan Zaben Gwamnan Ondo

by Yusuf Shuaibu and Sulaiman
10 months ago
in Tambarin Dimokuradiyya
0
inec
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa (INEC) ta yi kira ga jam’iyyun siyasa, ‘yan takara, da magoya bayansu da su wanzar da zaman lafiya a zaben gwamnan Jihar Ondo da za a yi a ranar 16 ga watan Nuwamba.

 

Shugaban hukumar INEC na kasa, Farfesa Mahmood Yakubu ne ya yi wannan roko a lokacin da yake sa ido a kan taron fara shirye-shiryen zaben gwamnan Jihar Ondo na shekarar 2024, daukacin sassan jihar.

  • An Kafa Kawancen Hadin Gwiwar Taron Masanan “Global South”
  • Yadda Gwamna Nasir Idris Ya Daura Damarar Bunkasa Ilimi A Jihar Kebbi

Shugaban hukumar INEC wanda ya ce aikin fara shirye-shiryen na matsayin zakarar gwajin dafi kan tsarin zaben, ya ce idan jam’iyyu da magoya bayansu suka tabbatar da zaman lafiya zai bai wa hukumar damar gudanar da zabe na gaskiya da adalci.

 

Labarai Masu Nasaba

Rudani Ya Kunno Kai Yayin Da INEC Ta Ki Amincewa Da Shugabancin ADC

‘Yan Nijeriya Suna Shan Wahala A Lokacin Da Gwamnatin Tinubu Ta Fi Damuwa Da Aljihunta – Sule Lamido

A cewarsa, “Za mu tabbatar da cewa an bude dukkan rumfunan zabe a kan lokaci domin ka da masu kada kuri’a su zo su jira jami’an INEC da kayan zabe. Mun gwada ingancin na’urar, ba a tabbatar an tura kayayyakin zabe a kan lokaci.

 

“Muna yin iya kokarinmu a matsayin hukumar zabe da sauran su ma su yi nasu iya bakin kokarinsu, musamman jam’iyyun siyasa da ‘yan takara. Ina so in yi kira ga jam’iyyun siyasa, ‘yan takara da magoya bayansu da su tabbatar da cewa sun kiyaye zaman lafiya, wanda zai ba mu damar gudanar da zabe cikin lokacin da ya dace da kuma kammala ayyukanmu kan lokaci.

 

“Sannan kuma a sanar da al’ummar Jihar Ondo su fito kwansu da kwarkwatansu su zabi ‘yan takarar gwamnansu ranar Asabar.

 

“Ba za a samu jinkiri wajen gudanar da zaben, kuma zan zo tare da iyalina don kada kuri’armu ga dan takarar da muke son zaba,” in ji shugaban INEC.

 

Har ila yau, Adebimpe Bankole, wanda ya aka tantance a makarantar firamare ta Alagbaka, Akure a rumfar zabe ta 5, ya bayyana cewa INEC ta cancanci yabo domin ta gudanar da kashi 80 bisa 100 na wannan aikin zabe.

 

Bankole ya ce; “Na gamsu da tsarin saboda ban bata wani lokaci ba kafin a tantance in. Sai dai kuma ba zai iya ba su kashi 100 ba. Na dai ba su kashi 80 bisa 100 saboda sun yi kokari sosai. Da yardar Allah zan fito a ranar Asabar 16 ga watan Nuwamba domin in kada kuri’ata.”

 

Shugaban INEC tare da sauran jami’an hukumar, sun ziyarci Idanre, Ile-Oluji/Oke-Igbo, duka a gundumomin Ondo ta tsakiya da kuma Ondo ta Kudu a Jihar Ondo.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Xi Jinping Ya Gabatar Da Jawabi A Taron Kolin CEO Na APEC

Next Post

ICPC Za Ta Binciki Jami’an INEC Kan Almundahana A Zaben Gwamnan Edo

Related

Fursunoni Ba Za Su Samu Damar Kada Kuri’a Ba A Zaben 2023 – INEC
Tambarin Dimokuradiyya

Rudani Ya Kunno Kai Yayin Da INEC Ta Ki Amincewa Da Shugabancin ADC

2 weeks ago
‘Yan Nijeriya Suna Shan Wahala A Lokacin Da Gwamnatin Tinubu Ta Fi Damuwa Da Aljihunta – Sule Lamido
Tambarin Dimokuradiyya

‘Yan Nijeriya Suna Shan Wahala A Lokacin Da Gwamnatin Tinubu Ta Fi Damuwa Da Aljihunta – Sule Lamido

2 weeks ago
Daraktoci Da Jami’an FCT 7 Na Fuskantar Tuhume-tuhume Kan Badakar Fili
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Idan Kana Son Tarwatsa PDP, To Ka Dawo Da Peter Obi – Wike

2 weeks ago
ADC Ta Bukaci Tinubu Ya Kafa Dokar Ta Baci A Katsina Da Zamfara Kan Rashin Tsaro
Tambarin Dimokuradiyya

ADC Ta Bukaci Tinubu Ya Kafa Dokar Ta Baci A Katsina Da Zamfara Kan Rashin Tsaro

3 weeks ago
katin zabe
Tambarin Dimokuradiyya

INEC Ta Bayyana Damuwarta Kan Katunan Zabe 360,000 Da Ba A Karba Ba A Kano

3 weeks ago
Jam’iyyar PDP Ta Janye Daga Shiga Zaɓen Ƙananan Hukumomi A Kebbi
Tambarin Dimokuradiyya

Shugabannin PDP Sun Shiga Dimuwa Yayin Da APC Ke Zawarcin Wasu Gwamnoninsu

3 weeks ago
Next Post
ICPC

ICPC Za Ta Binciki Jami’an INEC Kan Almundahana A Zaben Gwamnan Edo

LABARAI MASU NASABA

Peng Liyuan Ta Halarci Bikin Mika Lambobin Yabo A Fannin Raya Ilimin Yara Mata Da Mata Na Hukumar UNESCO 

Peng Liyuan Ta Halarci Bikin Mika Lambobin Yabo A Fannin Raya Ilimin Yara Mata Da Mata Na Hukumar UNESCO 

September 20, 2025
Mun Kawo Ƙarshen Dogon Layin Mai Na Shekara 50 A Nijeriya – Matatar Dangote

Mun Kawo Ƙarshen Dogon Layin Mai Na Shekara 50 A Nijeriya – Matatar Dangote

September 20, 2025
Sin Da Amurka Na Iya Cimma Manyan Nasara Tare In Ji Shugaba Xi

Sin Da Amurka Na Iya Cimma Manyan Nasara Tare In Ji Shugaba Xi

September 20, 2025
Ta Yaya Zan Yi Tattalin Mijina?

Ta Yaya Zan Yi Tattalin Mijina?

September 20, 2025
Ajali: Wasu Ƴan Ƙauye Sun Gujewa Ƴan Bindiga Sun Nutse A Ruwa

Ajali: Wasu Ƴan Ƙauye Sun Gujewa Ƴan Bindiga Sun Nutse A Ruwa

September 20, 2025
Tinubu Ya Halarci Ɗaurin Auren Ɗan Yari, Ya Kai Ziyara Gidan Tsohon Shugaban Ƙasa Buhari

Tinubu Ya Halarci Ɗaurin Auren Ɗan Yari, Ya Kai Ziyara Gidan Tsohon Shugaban Ƙasa Buhari

September 20, 2025
Sabon Kakin Ƴansanda Ya Ziyarci Cibiyar Ƙungiyar Ƴan Jarida A FCT

Sabon Kakin Ƴansanda Ya Ziyarci Cibiyar Ƙungiyar Ƴan Jarida A FCT

September 20, 2025
Nijeriya Na Asarar Dala Biliyan 10.5 Sakamakon Rashin Cin Gajiyar Kashin Dabbobi

Nijeriya Na Asarar Dala Biliyan 10.5 Sakamakon Rashin Cin Gajiyar Kashin Dabbobi

September 20, 2025
Makarantun Da Ba Ƙwararrun Malamai Za Su Rasa Zama Cibiyar Rubuta Jarrabawar NECO

Makarantun Da Ba Ƙwararrun Malamai Za Su Rasa Zama Cibiyar Rubuta Jarrabawar NECO

September 20, 2025
Magoya Bayan Aiyedatiwa Sun Ɓarke Da Sowa Bayan Nasara A Kotun Ƙoli

Magoya Bayan Aiyedatiwa Sun Ɓarke Da Sowa Bayan Nasara A Kotun Ƙoli

September 20, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.