• English
  • Business News
Sunday, November 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

INEC Ta Bukaci Jam’iyyu Da ‘Yan Takara Su Wanzar Da Zaman Lafiya Kan Zaben Gwamnan Ondo

by Yusuf Shuaibu and Sulaiman
12 months ago
inec

Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa (INEC) ta yi kira ga jam’iyyun siyasa, ‘yan takara, da magoya bayansu da su wanzar da zaman lafiya a zaben gwamnan Jihar Ondo da za a yi a ranar 16 ga watan Nuwamba.

 

Shugaban hukumar INEC na kasa, Farfesa Mahmood Yakubu ne ya yi wannan roko a lokacin da yake sa ido a kan taron fara shirye-shiryen zaben gwamnan Jihar Ondo na shekarar 2024, daukacin sassan jihar.

  • An Kafa Kawancen Hadin Gwiwar Taron Masanan “Global South”
  • Yadda Gwamna Nasir Idris Ya Daura Damarar Bunkasa Ilimi A Jihar Kebbi

Shugaban hukumar INEC wanda ya ce aikin fara shirye-shiryen na matsayin zakarar gwajin dafi kan tsarin zaben, ya ce idan jam’iyyu da magoya bayansu suka tabbatar da zaman lafiya zai bai wa hukumar damar gudanar da zabe na gaskiya da adalci.

 

LABARAI MASU NASABA

Abin Da APC Za Ta Yi Da Rinjayen Kashi Biyu Bisa Uku A Majalisar Tarayya

Manyan Kalubalen Da Sabon Shugaban INEC Zai Fuskanta

A cewarsa, “Za mu tabbatar da cewa an bude dukkan rumfunan zabe a kan lokaci domin ka da masu kada kuri’a su zo su jira jami’an INEC da kayan zabe. Mun gwada ingancin na’urar, ba a tabbatar an tura kayayyakin zabe a kan lokaci.

 

“Muna yin iya kokarinmu a matsayin hukumar zabe da sauran su ma su yi nasu iya bakin kokarinsu, musamman jam’iyyun siyasa da ‘yan takara. Ina so in yi kira ga jam’iyyun siyasa, ‘yan takara da magoya bayansu da su tabbatar da cewa sun kiyaye zaman lafiya, wanda zai ba mu damar gudanar da zabe cikin lokacin da ya dace da kuma kammala ayyukanmu kan lokaci.

 

“Sannan kuma a sanar da al’ummar Jihar Ondo su fito kwansu da kwarkwatansu su zabi ‘yan takarar gwamnansu ranar Asabar.

 

“Ba za a samu jinkiri wajen gudanar da zaben, kuma zan zo tare da iyalina don kada kuri’armu ga dan takarar da muke son zaba,” in ji shugaban INEC.

 

Har ila yau, Adebimpe Bankole, wanda ya aka tantance a makarantar firamare ta Alagbaka, Akure a rumfar zabe ta 5, ya bayyana cewa INEC ta cancanci yabo domin ta gudanar da kashi 80 bisa 100 na wannan aikin zabe.

 

Bankole ya ce; “Na gamsu da tsarin saboda ban bata wani lokaci ba kafin a tantance in. Sai dai kuma ba zai iya ba su kashi 100 ba. Na dai ba su kashi 80 bisa 100 saboda sun yi kokari sosai. Da yardar Allah zan fito a ranar Asabar 16 ga watan Nuwamba domin in kada kuri’ata.”

 

Shugaban INEC tare da sauran jami’an hukumar, sun ziyarci Idanre, Ile-Oluji/Oke-Igbo, duka a gundumomin Ondo ta tsakiya da kuma Ondo ta Kudu a Jihar Ondo.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Abin Da APC Za Ta Yi Da Rinjayen Kashi Biyu Bisa Uku A Majalisar Tarayya
Tambarin Dimokuradiyya

Abin Da APC Za Ta Yi Da Rinjayen Kashi Biyu Bisa Uku A Majalisar Tarayya

November 7, 2025
Manyan Kalubalen Da Sabon Shugaban INEC Zai Fuskanta
Tambarin Dimokuradiyya

Manyan Kalubalen Da Sabon Shugaban INEC Zai Fuskanta

October 17, 2025
peter
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Peter Obi Ya Shiga Rudani Kan Jam’iyyar Da Zai Tsaya Takara

October 17, 2025
Next Post
ICPC

ICPC Za Ta Binciki Jami’an INEC Kan Almundahana A Zaben Gwamnan Edo

LABARAI MASU NASABA

Kasar Sin Ta Fitar Da Takardar Bayani Kan Samun Ci Gaba Mai Karancin Fitar Da Hayaki

Kasar Sin Ta Fitar Da Takardar Bayani Kan Samun Ci Gaba Mai Karancin Fitar Da Hayaki

November 8, 2025
Kasar Sin Ta Sake Jaddada Cikakken Goyon Bayanta Ga Muhimmiyar Rawar Da MDD Ke Takawa A Harkokin Kasa Da Kasa 

Kasar Sin Ta Sake Jaddada Cikakken Goyon Bayanta Ga Muhimmiyar Rawar Da MDD Ke Takawa A Harkokin Kasa Da Kasa 

November 8, 2025
Turkiyya Na Karbar Bakuncin Wasu Kasashen Musulmai Game Da Makomar Gaza

Turkiyya Na Karbar Bakuncin Wasu Kasashen Musulmai Game Da Makomar Gaza

November 8, 2025
Babban Yankin Sin Da Taiwan Sun Yi Tarukan Bita Don Tunawa Da Taron Xi Da Ma Mai Tarihi

Babban Yankin Sin Da Taiwan Sun Yi Tarukan Bita Don Tunawa Da Taron Xi Da Ma Mai Tarihi

November 8, 2025
Kasashen Afirka Bakwai Da Sojojin Amurka Suka Shiga

Kasashen Afirka Bakwai Da Sojojin Amurka Suka Shiga

November 8, 2025
Firaministan Kasar Georgia: CIIE Muhimmin Dandali Ne

Firaministan Kasar Georgia: CIIE Muhimmin Dandali Ne

November 8, 2025
Yadda Aka Tsara Gudanar Da Gasar Kofin Afirka A Moroko

Yadda Aka Tsara Gudanar Da Gasar Kofin Afirka A Moroko

November 8, 2025
CMG Ya Watsa Jerin Shirye-Shirye Don Tunawa Da Cika Shekaru 80 Da Dawowar Yankin Taiwan Kasar Sin

CMG Ya Watsa Jerin Shirye-Shirye Don Tunawa Da Cika Shekaru 80 Da Dawowar Yankin Taiwan Kasar Sin

November 8, 2025
CMG Ya Gabatar Da Jerin Rahotannin Talabijin Kan Tunawa Da Cika Shekaru 80 Da Dawowar Yankin Taiwan Kasar Sin

CMG Ya Gabatar Da Jerin Rahotannin Talabijin Kan Tunawa Da Cika Shekaru 80 Da Dawowar Yankin Taiwan Kasar Sin

November 8, 2025
Xi Ya Yi Kiran Zurfafa Gyare-gyare Da Bude Kofa A Yayin Rangadin Aiki A Guangdong

Xi Ya Yi Kiran Zurfafa Gyare-gyare Da Bude Kofa A Yayin Rangadin Aiki A Guangdong

November 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.