• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

INEC Ta Bukaci Jam’iyyu Da ‘Yan Takara Su Wanzar Da Zaman Lafiya Kan Zaben Gwamnan Ondo

by Yusuf Shuaibu and Sulaiman
7 months ago
in Tambarin Dimokuradiyya
0
inec
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa (INEC) ta yi kira ga jam’iyyun siyasa, ‘yan takara, da magoya bayansu da su wanzar da zaman lafiya a zaben gwamnan Jihar Ondo da za a yi a ranar 16 ga watan Nuwamba.

 

Shugaban hukumar INEC na kasa, Farfesa Mahmood Yakubu ne ya yi wannan roko a lokacin da yake sa ido a kan taron fara shirye-shiryen zaben gwamnan Jihar Ondo na shekarar 2024, daukacin sassan jihar.

  • An Kafa Kawancen Hadin Gwiwar Taron Masanan “Global South”
  • Yadda Gwamna Nasir Idris Ya Daura Damarar Bunkasa Ilimi A Jihar Kebbi

Shugaban hukumar INEC wanda ya ce aikin fara shirye-shiryen na matsayin zakarar gwajin dafi kan tsarin zaben, ya ce idan jam’iyyu da magoya bayansu suka tabbatar da zaman lafiya zai bai wa hukumar damar gudanar da zabe na gaskiya da adalci.

 

Labarai Masu Nasaba

‘Yancin Kananan Hukumomi: Shekara Daya Da Hukuncin Kotun Koli Amma Ba A Aiwatar Ba

Ko Kwamitin Saraki Zai Iya Ceto PDP Daga Rikicin Cikin Gida?

A cewarsa, “Za mu tabbatar da cewa an bude dukkan rumfunan zabe a kan lokaci domin ka da masu kada kuri’a su zo su jira jami’an INEC da kayan zabe. Mun gwada ingancin na’urar, ba a tabbatar an tura kayayyakin zabe a kan lokaci.

 

“Muna yin iya kokarinmu a matsayin hukumar zabe da sauran su ma su yi nasu iya bakin kokarinsu, musamman jam’iyyun siyasa da ‘yan takara. Ina so in yi kira ga jam’iyyun siyasa, ‘yan takara da magoya bayansu da su tabbatar da cewa sun kiyaye zaman lafiya, wanda zai ba mu damar gudanar da zabe cikin lokacin da ya dace da kuma kammala ayyukanmu kan lokaci.

 

“Sannan kuma a sanar da al’ummar Jihar Ondo su fito kwansu da kwarkwatansu su zabi ‘yan takarar gwamnansu ranar Asabar.

 

“Ba za a samu jinkiri wajen gudanar da zaben, kuma zan zo tare da iyalina don kada kuri’armu ga dan takarar da muke son zaba,” in ji shugaban INEC.

 

Har ila yau, Adebimpe Bankole, wanda ya aka tantance a makarantar firamare ta Alagbaka, Akure a rumfar zabe ta 5, ya bayyana cewa INEC ta cancanci yabo domin ta gudanar da kashi 80 bisa 100 na wannan aikin zabe.

 

Bankole ya ce; “Na gamsu da tsarin saboda ban bata wani lokaci ba kafin a tantance in. Sai dai kuma ba zai iya ba su kashi 100 ba. Na dai ba su kashi 80 bisa 100 saboda sun yi kokari sosai. Da yardar Allah zan fito a ranar Asabar 16 ga watan Nuwamba domin in kada kuri’ata.”

 

Shugaban INEC tare da sauran jami’an hukumar, sun ziyarci Idanre, Ile-Oluji/Oke-Igbo, duka a gundumomin Ondo ta tsakiya da kuma Ondo ta Kudu a Jihar Ondo.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Xi Jinping Ya Gabatar Da Jawabi A Taron Kolin CEO Na APEC

Next Post

ICPC Za Ta Binciki Jami’an INEC Kan Almundahana A Zaben Gwamnan Edo

Related

‘Yancin Kananan Hukumomi: Shekara Daya Da Hukuncin Kotun Koli Amma Ba A Aiwatar Ba
Tambarin Dimokuradiyya

‘Yancin Kananan Hukumomi: Shekara Daya Da Hukuncin Kotun Koli Amma Ba A Aiwatar Ba

7 days ago
Ko Kwamitin Saraki Zai Iya Ceto PDP Daga Rikicin Cikin Gida?
Tambarin Dimokuradiyya

Ko Kwamitin Saraki Zai Iya Ceto PDP Daga Rikicin Cikin Gida?

2 weeks ago
Tsadar Rayuwa Da Karuwar Ta’addanci Na Ci Gaba Da Tagayyara ‘Yan Nijeriya
Tambarin Dimokuradiyya

‘Yan Adawa Na Cacakar APC A Yankin Arewa Maso Yamma Bisa Goyon Bayan Tazarcen Tinubu

2 weeks ago
Shugaban INEC Ya Yi Kira Da A Sake Fasalin Tsarin Zabe Gabanin 2027
Tambarin Dimokuradiyya

Shugaban INEC Ya Yi Kira Da A Sake Fasalin Tsarin Zabe Gabanin 2027

1 month ago
INEC
Tambarin Dimokuradiyya

Amfani Da Karfin Gwamnati Kan ‘Yan Adawa Zai Jawo Wa Tinubu Illa A 2027 – Sule Lamido

1 month ago
‘Yan Siyasa Na Gwagwarmaya Ne Kadai Wajen Neman Mukami Ba Wai Don Talakawa Ba — Bafarawa
Tambarin Dimokuradiyya

‘Yan Siyasa Na Gwagwarmaya Ne Kadai Wajen Neman Mukami Ba Wai Don Talakawa Ba — Bafarawa

1 month ago
Next Post
ICPC

ICPC Za Ta Binciki Jami’an INEC Kan Almundahana A Zaben Gwamnan Edo

LABARAI MASU NASABA

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

June 6, 2025
Daurarru

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

June 6, 2025
Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

June 6, 2025
Wutar lantarki

Fadar Shugaban Kasa Na Yunkurin Biyan Basukan Wutar Lantarki Na Naira Tiriliyan 2

June 6, 2025
Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

June 6, 2025
Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

June 6, 2025
Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4

Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4

June 6, 2025
An Kama Wadanda Ake Zargi Da Kai Wa Shugaban Kwadago Hari Ribadu

Ribadu Ya Kara Jaddada Gargadinsa Kan Biyan Kudin Fansa Ga Masu Garkuwa Da Mutane

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

June 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.