• English
  • Business News
Sunday, August 3, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Inuwar Gamji

by CGTN Hausa and Sulaiman
8 months ago
in Ra'ayi Riga
0
Inuwar Gamji
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Yayin da shekara ta 2024 ke ban kwana, tashe-tashen hankula da fitintinu na ci gaba da kazancewa. Shi kuma tattalin arzikin duniya yana ci gaba da tangal-tangal. Matsalar tsaro kuwa, wadda ta hada da ayyukan ta’addanci ta ki ci ta ki cinyewa, ballantana tabarbarewar yanayi wanda yake haddasa ambaliya, gobarar daji da dumamar yanayi, abin ba’a magana.

 

Wannan gagarumin kalubale ya sanya kasashe masu tasowa kasa cimma muradin Majalisar Dinkin Duniya (UN) na samu ci gaba mai dorewa ya zuwa shekara ta 2030. Wasu kasashen duniya kuwa, sabo da nuna isa da gadara, sun kekashe kan tsohon tsarin da suke a kai domin kare muradunsu na son zuciya.

  • Kebbi Da Brazil Zasu Yi Haɗin Gwuiwa Kan Sarrafa Nama Ta Hanyar Zamani
  • Kebbi Da Brazil Zasu Yi Haɗin Gwuiwa Kan Sarrafa Nama Ta Hanyar Zamani

Kasar Sin, wadda tun fil azal ba ta yarda da cin zalun ba, ko nuna fin karfi domin biyan bukatunta, tana nan ba ta canza ba a kan manufarta ta gujewa tsoma baki a cikin harkokin cikin gida na kasashen da take ma’amala da su. “Cude ni in cude ka” shi ne babban tafarkin da kasar Sin take a kai a ma’amalarta da sauran kasashen duniya.

 

Labarai Masu Nasaba

Amurka: “Afirka Ba Ta Cikin Jerin Fannoni Da Muka Ba Da Fifiko A Kai”

Mai Cin Moriyar Kai Da Mai Cin Moriyar Juna

Idan ba’a manta ba dai, a watan Satumban wannan shekara ne Beijing ta shirya ta kuma aiwatar da gagarumin taron koli na hadin gwiwa tsakanin China da kasashen Afirka. A wajen taron ne, wanda ya samu halartar shugabanni da wakilan gwamnatocin kasashen Afirka su 53, har da shugaban kungiyar tarayyar Afirka, AU, aka cimma matsaya ta bai daya ta zurfafa dangantaka tsakanin China da Afirka, bisa tsarin ci gaban duniya.

 

Dukkan mahalarta taron bakinsu ya zo daya ta fuskar hada karfi domin aiwatar da tsarin daidaito, bin ka’ida da kuma bunkasa tattalin arzikin duniya, ta yadda kowa zai amfana.

 

Dalilin gagarumar nasarar taron koli na Beijing shi ne bayanin da China ta yi dalla dalla ba tare da rufa-rufa ba a kan manufarta ta kulla wannan dangantakar hadin gwiwa tsakaninta da kasashen Afirka. Hakan ya gamsar da mahalarta taron, kasancewar sun fahimci cewa kowa zai ci gajiyar wannan hadin gwiwa. Wannan ne ya ba su kwarin gwiwar sakin jiki tare da samun natsuwa da mahukuntan kasar ta China a matsayin aminai na gaskiya.

 

A watan Nuwamban da ya gabata ne, aka gudanar da taron koli na kungiyar hadin kan tattalin arziki na kasashen duniya da ake kira G20 a birnin Rio de Janeiro na kasar Brazil. Taron shi ne na farko tun lokacin da kungiyar tarayyar Afirka (AU) ta samu kasancewa mamba a cikin kungiyar biyo bayan taron kungiya ta G20 karo na 18 da aka gudanar a birnin New Delhi na India a watan satumban 2023, kungiyar AU ta samu shiga cikin kungiyar G20 a hukunce.

 

China ita ce ta yi ruwa ta yi tsaki wajen ganin kungiyar AU ta samu shiga kungiyar G20, sannan kuma ta tsaya tsayin daka wajen ganin kungiyar AU ta taka rawar gani a harkokin shugabanci na duniya.

 

Wannan shi ne ya kara jaddada kalaman shugaba Xi Jinping na kasar Sin na cewa babu yadda za’a samu ci gaba da daidaito a duniya yayin da masu hannu da shuni suke kara azurcewa, su kuma talakawa suke kara durmuyewa cikin kangin talauci.

 


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Dubban Mutane Sun Halarci Taron Mata Network A Kano

Next Post

Gwamnan Zamfara Ya Rantsar Da Sabon Kwamishina Tare Da Yin Garambawul Ga Muƙarrabansa

Related

Amurka: “Afirka Ba Ta Cikin Jerin Fannoni Da Muka Ba Da Fifiko A Kai”
Ra'ayi Riga

Amurka: “Afirka Ba Ta Cikin Jerin Fannoni Da Muka Ba Da Fifiko A Kai”

3 days ago
Mai Cin Moriyar Kai Da Mai Cin Moriyar Juna
Ra'ayi Riga

Mai Cin Moriyar Kai Da Mai Cin Moriyar Juna

5 days ago
Bai Kamata a Rika Kai wa Fararen Hula Hari Ba!
Ra'ayi Riga

Bai Kamata a Rika Kai wa Fararen Hula Hari Ba!

1 week ago
Tursasawa Kasashen Afirka Karbar Bakin Haure Daga Amerika Kuskure Ne
Ra'ayi Riga

Tursasawa Kasashen Afirka Karbar Bakin Haure Daga Amerika Kuskure Ne

2 weeks ago
Wace Kasa Ce Take Son Zama “Kasa Ta Uku Mai Tsaro” A Wurin Amurka?
Ra'ayi Riga

Wace Kasa Ce Take Son Zama “Kasa Ta Uku Mai Tsaro” A Wurin Amurka?

2 weeks ago
Lai Ching-Te Bai Cancanci Zama Jagoran Yankin Taiwan Ba
Ra'ayi Riga

Lai Ching-Te Bai Cancanci Zama Jagoran Yankin Taiwan Ba

2 weeks ago
Next Post
Gwamnan Zamfara Ya Rantsar Da Sabon Kwamishina Tare Da Yin Garambawul Ga Muƙarrabansa

Gwamnan Zamfara Ya Rantsar Da Sabon Kwamishina Tare Da Yin Garambawul Ga Muƙarrabansa

LABARAI MASU NASABA

Sanata Buba Ya ƙaryata Jita-jitar Cewa Majalisa Ta Amince da ƙirƙiro Sabbin Jihohi 12

Sanata Buba Ya ƙaryata Jita-jitar Cewa Majalisa Ta Amince da ƙirƙiro Sabbin Jihohi 12

August 2, 2025
Menene Sirrin Nasarar Ƴan Wasan Nijeriya Mata A Ƙwallon Ƙafa?

Menene Sirrin Nasarar Ƴan Wasan Nijeriya Mata A Ƙwallon Ƙafa?

August 2, 2025
Kashi 40 Na Ƙananan Yara A Nijeriya Ke Fuskantar Barazanar Yunwa — Rahoto

Etsu Nupe Ya Jaddada Buƙatar Sama Wa Sarakunan Gargajiya Gurbi A Tsarin Mulki

August 2, 2025
Babban Bankin Sin Ya Yi Alkawarin Ba Da Goyon Baya Ga Kirkire-Kirkire Da Sayayya

Babban Bankin Sin Ya Yi Alkawarin Ba Da Goyon Baya Ga Kirkire-Kirkire Da Sayayya

August 2, 2025
Fim Na Kisan Kiyashin Nanjing Ya Mamaye Kasuwar Fina-Finan Sin Bisa Samun Kudin Shiga Yuan Biliyan Daya

Fim Na Kisan Kiyashin Nanjing Ya Mamaye Kasuwar Fina-Finan Sin Bisa Samun Kudin Shiga Yuan Biliyan Daya

August 2, 2025
Kashi 40 Na Ƙananan Yara A Nijeriya Ke Fuskantar Barazanar Yunwa — Rahoto

Kashi 40 Na Ƙananan Yara A Nijeriya Ke Fuskantar Barazanar Yunwa — Rahoto

August 2, 2025
Yadda Kwamishinan Kano Ya Karɓi Dala $30,000 Domin Yin Belin Dilan Ƙwaya A Kotu – Rahoto

Yadda Kwamishinan Kano Ya Karɓi Dala $30,000 Domin Yin Belin Dilan Ƙwaya A Kotu – Rahoto

August 2, 2025
Babban Jami’in MDD: Kokarin Sin A Fannin Samun Ci Gaba Mai Dorewa Na Da Matukar Alfanu Ga Yanayin Duniya

Babban Jami’in MDD: Kokarin Sin A Fannin Samun Ci Gaba Mai Dorewa Na Da Matukar Alfanu Ga Yanayin Duniya

August 2, 2025
An Dawo Da Wutar Lantarki A Dukkan Kauyukan Da Aka Tafka Ruwa Da Iska A Beijing

An Dawo Da Wutar Lantarki A Dukkan Kauyukan Da Aka Tafka Ruwa Da Iska A Beijing

August 2, 2025
Ma’aikatan Jinya Sun Janye Yajin Aiki Bayan Gwamnatin Tarayya Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu 

Ma’aikatan Jinya Sun Janye Yajin Aiki Bayan Gwamnatin Tarayya Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu 

August 2, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.