• English
  • Business News
Monday, June 30, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Irin Ministocin Da ‘Yan Nijeriya Ke Tsammani Daga Gwamnatin Tinubu

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
in Tambarin Dimokuradiyya
0
Irin Ministocin Da ‘Yan Nijeriya Ke Tsammani Daga Gwamnatin Tinubu
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A yayin da ya shafe makonni biyar a kan karagar mulki, Shugaba Bola Ahmed Tinubu yana da wani muhimmin babban aiki a gabansa na kafa majalisar ministoci a matsayinsa na shugaban kasa shi ne.

A yanzu haka dai, Shugaban Tinubu yana da tsawon kwanaki 30 na kafa majalisar manistocin. Majalisa ta tanadi tsawan kwanaki 60 ne ga sabon shugaban kasa da gwamnoni su kafa majalisar zartarwa, amma tsohon shugaban kasa Muhammadu Buhari ya shafe watanni shida kafin ya nada ministoci a gwamnatinsa, wanda hakan ya saba wa ka’ida na kafa majalisar ministoci.

  • Tinubu Ya Yi Garambawul Kan Dokokin Haraji
  • Muhyi Ya Aike Wa Ganduje Sammaci Kan Bidiyon Dala

Bugu da kari, al’amura sun yi yawa matuka, kuma ‘yan Nijeriya sun lura cewa rashin samun nasarar dimokuradiyya ta hanyar ingantaccen tsarin mulki na gaskiya na iya kawo cikas ga makomar kasar a matsayin dunkulalliyar kasa.

A matsayinsu na manyan mambobi na majalisar ministoci da shugaban kasa zai nada kuma majalisar tarayya ta tabbatar da su sun kasance wani bangare na manufofi da tsare-tsare na zartar da hukunci da ke tafiyar da mulki yadda ya kamata.

Dole ne nadin nasu ya kasance mai cike da da’a da za su iya fidda kitse daga wuta. A wannan gaba, ana bukatar samun nagartattun mutane da za su iya taimakon shugaban kasa wajen sauke nauyin da ya rataya a wuyansa. A bisa ka’idodi sun nuna samun majalisar ministoci nagari na iya shafar makomar kowacce kasa.

Labarai Masu Nasaba

Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin Fadar Shugaban Kasa Da Peter Obi Kan Tallafin Mai

Sauya Sheka Ya Sa APC Ta Samu Gagarumin Rinjaye A Majalisun Tarayya

Dangane da haka ne rahotanni ke cewa Shugaba Tinubu na neman masana a ciki da wajen kasar nan domin su taimaka masa wajen samun nasarar gwamnatinsa.

A yau, akwai sassa takwas masu matukar muhimmanci da za su iya haifar da sauye-sauye na kasa ko su iya rage radadin zamantakewa da siyasa da tattalin arziki a kasar nan. Wadannan sun hada da tsaro, wutar lantarki, ilimi, kiwon lafiya, noma, aikin yi da kuma samar da muhimman ababen more rayuwa. Idan aka mayar da hankali kan wadannan muhimman bangarorin za iya kawo sauyi ga kasa.

Bayan nada manyan mukaman hafsoshin tsaro, akwai ministoci da za a nada a cikin majalisar zartarwar Tinubu. Tun da akwai jihohi 36, kowace jiha sai an samu wakilcin akalla mutum daya ko fiye da haka, yayin da wasu za su samu mukamin babban minista, wasu kuma su kasance kananan ministoci.

Ko shakka babu shugaban kasar na da ‘yancin nada majalisar ministocinsa kamar yadda tsarin mulki ya tanada. A wurin nada mukaman minista, akwai abubuwan da yaka mata shugaban kasa ya yi la’akari da su wajen dauko mutanen da suka cancanta.

Duk da cewa dole ne Shugaba Tinubu ya bi tsarin daidaito wajen nada mukamai a gwamnatin tarayya, wanda ke bukatar minista daya daga cikin jihohi 36, zai iya tankade da rairaya a tsakanin masu fasaha da ’yan siyasa. Babban abin da ake bukata wajen zaben ministocinsa shi ne, cancanta ba tare da nuna son rai ko raja’a ga jam’iyya ba.

An saba mafi yawanci ‘yan siyasa ne ake bai wa mukaman ministoci duk da cewa ana sirki da ma’aikata da kuma kwararru daga bangarori daban-daban.

A halin da kasar nan ke ciki, mafi yawancin ‘yan Nijeriya na tsammanin shugaban Tinubu ya nada ministocin da suka dace ba tare da nuna bambancin siyasa ko ta jam’iyya ba.

‘Yan Nijeriya na son ganin sauyi a kan ministocin baya domin samun nasarar gwamnati yadda ya kamata.

Tuni dai ana ta yada jita-jitar cewa wasu mutane suna ci gaba da kamun kafa tare da bayar da cin hanci domin a ba su mukaman ministoci a gwamnatin Tinubu. Hakan yana matukar tayar da jijiyar wuya, inda da yawa ke ganin cewa ya kamata shugaban kasa ya tsaya ya darje wadanda zai nada a matsayin ministoci domin samun nasarar gwamnatinsa.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: MinistociTinubuTsammani
ShareTweetSendShare
Previous Post

Hare Haren Bindiga Sun Rushe Bikin Murnar Ranar Samun ‘Yancin Kan Amurka

Next Post

An Bude Taron Duniya Kan Fasahar Kwaikwayon Tunanin Dan Adam Ta AI A Shanghai

Related

Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin Fadar Shugaban Kasa Da Peter Obi Kan Tallafin Mai
Tambarin Dimokuradiyya

Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin Fadar Shugaban Kasa Da Peter Obi Kan Tallafin Mai

2 weeks ago
APC
Tambarin Dimokuradiyya

Sauya Sheka Ya Sa APC Ta Samu Gagarumin Rinjaye A Majalisun Tarayya

2 weeks ago
Adawa
Tambarin Dimokuradiyya

Yadda Rarrabuwar Kawunan Jam’iyyu Zai Iya Sauya Alkiblar Zaben 2027

3 weeks ago
‘Yancin Kananan Hukumomi: Shekara Daya Da Hukuncin Kotun Koli Amma Ba A Aiwatar Ba
Tambarin Dimokuradiyya

‘Yancin Kananan Hukumomi: Shekara Daya Da Hukuncin Kotun Koli Amma Ba A Aiwatar Ba

1 month ago
Ko Kwamitin Saraki Zai Iya Ceto PDP Daga Rikicin Cikin Gida?
Tambarin Dimokuradiyya

Ko Kwamitin Saraki Zai Iya Ceto PDP Daga Rikicin Cikin Gida?

1 month ago
Tsadar Rayuwa Da Karuwar Ta’addanci Na Ci Gaba Da Tagayyara ‘Yan Nijeriya
Tambarin Dimokuradiyya

‘Yan Adawa Na Cacakar APC A Yankin Arewa Maso Yamma Bisa Goyon Bayan Tazarcen Tinubu

1 month ago
Next Post
An Bude Taron Duniya Kan Fasahar Kwaikwayon Tunanin Dan Adam Ta AI A Shanghai

An Bude Taron Duniya Kan Fasahar Kwaikwayon Tunanin Dan Adam Ta AI A Shanghai

LABARAI MASU NASABA

Gwamna Yusuf Ya Jagoranci Tawagar Kano Zuwa Jana’izar Marigayi Aminu Dantata A Madina

Gwamna Yusuf Ya Jagoranci Tawagar Kano Zuwa Jana’izar Marigayi Aminu Dantata A Madina

June 30, 2025
Sojoji Sun Kashe Shugaban Ƴan Ta’adda Mai Dada

Sojoji Sun Kashe Shugaban Ƴan Ta’adda Mai Dada

June 29, 2025
Sharrin Ƴan Adawa Ne, Gwamnati Ta Ƙaryata Labarin Cire SGF Akume 

Sharrin Ƴan Adawa Ne, Gwamnati Ta Ƙaryata Labarin Cire SGF Akume 

June 29, 2025
An Sauya Sunan Makarantar Wasanni Don Girmama Ƴan Kano Da Suka Yi Hatsari

An Sauya Sunan Makarantar Wasanni Don Girmama Ƴan Kano Da Suka Yi Hatsari

June 29, 2025
Babbar Mota Ta Afka Cikin Kasuwa A Taraba, Mutane Da Yawa Sun Mutu

Babbar Mota Ta Afka Cikin Kasuwa A Taraba, Mutane Da Yawa Sun Mutu

June 29, 2025
Shugaban Majalisar Dokokin Jama’ar Kasar Mexico: Tunanin Raya Al’umma Mai Kyakkyawar Makoma Ga Dukkan Bil’adama Da Shugaba Xi Jinping Ya Gabatar Ya Kayatar

Shugaban Majalisar Dokokin Jama’ar Kasar Mexico: Tunanin Raya Al’umma Mai Kyakkyawar Makoma Ga Dukkan Bil’adama Da Shugaba Xi Jinping Ya Gabatar Ya Kayatar

June 29, 2025
Sin Na Adawa Da Duk Wata Yarjejeniyar Haraji Da Ka Iya Illata Moriyarta

Sin Na Adawa Da Duk Wata Yarjejeniyar Haraji Da Ka Iya Illata Moriyarta

June 29, 2025
2027: Ƴan Adawa Na Ƙara Ƙaimin Kawar Da Tinubu

2027: Ƴan Adawa Na Ƙara Ƙaimin Kawar Da Tinubu

June 29, 2025
Yadda Yaƙin Iran Da Isra’ila Zai Iya Shafar Zamantakewa Da Tattalin Arziƙin Nijeriya

Yadda Yaƙin Iran Da Isra’ila Zai Iya Shafar Zamantakewa Da Tattalin Arziƙin Nijeriya

June 29, 2025
Ƙwallon Mata: Rivers United Ta Doke Nasarawa Amazons A Wasan Ƙarshe Na Kofin Shugaban Ƙasa

Ƙwallon Mata: Rivers United Ta Doke Nasarawa Amazons A Wasan Ƙarshe Na Kofin Shugaban Ƙasa

June 29, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.