ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Irin Ministocin Da ‘Yan Nijeriya Ke Tsammani Daga Gwamnatin Tinubu

by Yusuf Shuaibu
3 years ago
Tsammani

A yayin da ya shafe makonni biyar a kan karagar mulki, Shugaba Bola Ahmed Tinubu yana da wani muhimmin babban aiki a gabansa na kafa majalisar ministoci a matsayinsa na shugaban kasa shi ne.

A yanzu haka dai, Shugaban Tinubu yana da tsawon kwanaki 30 na kafa majalisar manistocin. Majalisa ta tanadi tsawan kwanaki 60 ne ga sabon shugaban kasa da gwamnoni su kafa majalisar zartarwa, amma tsohon shugaban kasa Muhammadu Buhari ya shafe watanni shida kafin ya nada ministoci a gwamnatinsa, wanda hakan ya saba wa ka’ida na kafa majalisar ministoci.

  • Tinubu Ya Yi Garambawul Kan Dokokin Haraji
  • Muhyi Ya Aike Wa Ganduje Sammaci Kan Bidiyon Dala

Bugu da kari, al’amura sun yi yawa matuka, kuma ‘yan Nijeriya sun lura cewa rashin samun nasarar dimokuradiyya ta hanyar ingantaccen tsarin mulki na gaskiya na iya kawo cikas ga makomar kasar a matsayin dunkulalliyar kasa.

ADVERTISEMENT

A matsayinsu na manyan mambobi na majalisar ministoci da shugaban kasa zai nada kuma majalisar tarayya ta tabbatar da su sun kasance wani bangare na manufofi da tsare-tsare na zartar da hukunci da ke tafiyar da mulki yadda ya kamata.

Dole ne nadin nasu ya kasance mai cike da da’a da za su iya fidda kitse daga wuta. A wannan gaba, ana bukatar samun nagartattun mutane da za su iya taimakon shugaban kasa wajen sauke nauyin da ya rataya a wuyansa. A bisa ka’idodi sun nuna samun majalisar ministoci nagari na iya shafar makomar kowacce kasa.

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan

Amurka Ta Yi Alƙawarin Sa Ido Sosai A Zaɓen Nijeriya Na 2027

Dangane da haka ne rahotanni ke cewa Shugaba Tinubu na neman masana a ciki da wajen kasar nan domin su taimaka masa wajen samun nasarar gwamnatinsa.

A yau, akwai sassa takwas masu matukar muhimmanci da za su iya haifar da sauye-sauye na kasa ko su iya rage radadin zamantakewa da siyasa da tattalin arziki a kasar nan. Wadannan sun hada da tsaro, wutar lantarki, ilimi, kiwon lafiya, noma, aikin yi da kuma samar da muhimman ababen more rayuwa. Idan aka mayar da hankali kan wadannan muhimman bangarorin za iya kawo sauyi ga kasa.

Bayan nada manyan mukaman hafsoshin tsaro, akwai ministoci da za a nada a cikin majalisar zartarwar Tinubu. Tun da akwai jihohi 36, kowace jiha sai an samu wakilcin akalla mutum daya ko fiye da haka, yayin da wasu za su samu mukamin babban minista, wasu kuma su kasance kananan ministoci.

Ko shakka babu shugaban kasar na da ‘yancin nada majalisar ministocinsa kamar yadda tsarin mulki ya tanada. A wurin nada mukaman minista, akwai abubuwan da yaka mata shugaban kasa ya yi la’akari da su wajen dauko mutanen da suka cancanta.

Duk da cewa dole ne Shugaba Tinubu ya bi tsarin daidaito wajen nada mukamai a gwamnatin tarayya, wanda ke bukatar minista daya daga cikin jihohi 36, zai iya tankade da rairaya a tsakanin masu fasaha da ’yan siyasa. Babban abin da ake bukata wajen zaben ministocinsa shi ne, cancanta ba tare da nuna son rai ko raja’a ga jam’iyya ba.

An saba mafi yawanci ‘yan siyasa ne ake bai wa mukaman ministoci duk da cewa ana sirki da ma’aikata da kuma kwararru daga bangarori daban-daban.

A halin da kasar nan ke ciki, mafi yawancin ‘yan Nijeriya na tsammanin shugaban Tinubu ya nada ministocin da suka dace ba tare da nuna bambancin siyasa ko ta jam’iyya ba.

‘Yan Nijeriya na son ganin sauyi a kan ministocin baya domin samun nasarar gwamnati yadda ya kamata.

Tuni dai ana ta yada jita-jitar cewa wasu mutane suna ci gaba da kamun kafa tare da bayar da cin hanci domin a ba su mukaman ministoci a gwamnatin Tinubu. Hakan yana matukar tayar da jijiyar wuya, inda da yawa ke ganin cewa ya kamata shugaban kasa ya tsaya ya darje wadanda zai nada a matsayin ministoci domin samun nasarar gwamnatinsa.

Tsammani
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Amurka Ta Yi Alƙawarin Sa Ido Sosai A Zaɓen Nijeriya Na 2027
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Sautin Muryar Da Aka Fallasa Kan El-Rufai Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Ci-ma-zaunen Ƴan Siyasa Ne Ke Tunanin Yin Maguɗi A Zaɓen 2027 – Makarfi
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    An Samu Ruɗani Kan Rashin Bayyana Jerin Ƴan Takarar Jam’iyyun Siyasa Na Zaɓen 2027

MASU ALAKA

‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan
Manyan Labarai

‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan

July 15, 2026
Amurka Ta Yi Alƙawarin Sa Ido Sosai A Zaɓen Nijeriya Na 2027
Tambarin Dimokuradiyya

Amurka Ta Yi Alƙawarin Sa Ido Sosai A Zaɓen Nijeriya Na 2027

July 11, 2026
Sautin Muryar Da Aka Fallasa Kan El-Rufai Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara
Tambarin Dimokuradiyya

Sautin Muryar Da Aka Fallasa Kan El-Rufai Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara

July 11, 2026
Next Post
An Bude Taron Duniya Kan Fasahar Kwaikwayon Tunanin Dan Adam Ta AI A Shanghai

An Bude Taron Duniya Kan Fasahar Kwaikwayon Tunanin Dan Adam Ta AI A Shanghai

LABARAI MASU NASABA

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

July 15, 2026
Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

July 15, 2026
Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

July 15, 2026
Sabbin Ministoci

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026
GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

July 15, 2026
Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.