ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Irin Ministocin Da ‘Yan Nijeriya Ke Tsammani Daga Gwamnatin Tinubu

by Yusuf Shuaibu
3 years ago
Tsammani

A yayin da ya shafe makonni biyar a kan karagar mulki, Shugaba Bola Ahmed Tinubu yana da wani muhimmin babban aiki a gabansa na kafa majalisar ministoci a matsayinsa na shugaban kasa shi ne.

A yanzu haka dai, Shugaban Tinubu yana da tsawon kwanaki 30 na kafa majalisar manistocin. Majalisa ta tanadi tsawan kwanaki 60 ne ga sabon shugaban kasa da gwamnoni su kafa majalisar zartarwa, amma tsohon shugaban kasa Muhammadu Buhari ya shafe watanni shida kafin ya nada ministoci a gwamnatinsa, wanda hakan ya saba wa ka’ida na kafa majalisar ministoci.

  • Tinubu Ya Yi Garambawul Kan Dokokin Haraji
  • Muhyi Ya Aike Wa Ganduje Sammaci Kan Bidiyon Dala

Bugu da kari, al’amura sun yi yawa matuka, kuma ‘yan Nijeriya sun lura cewa rashin samun nasarar dimokuradiyya ta hanyar ingantaccen tsarin mulki na gaskiya na iya kawo cikas ga makomar kasar a matsayin dunkulalliyar kasa.

ADVERTISEMENT

A matsayinsu na manyan mambobi na majalisar ministoci da shugaban kasa zai nada kuma majalisar tarayya ta tabbatar da su sun kasance wani bangare na manufofi da tsare-tsare na zartar da hukunci da ke tafiyar da mulki yadda ya kamata.

Dole ne nadin nasu ya kasance mai cike da da’a da za su iya fidda kitse daga wuta. A wannan gaba, ana bukatar samun nagartattun mutane da za su iya taimakon shugaban kasa wajen sauke nauyin da ya rataya a wuyansa. A bisa ka’idodi sun nuna samun majalisar ministoci nagari na iya shafar makomar kowacce kasa.

LABARAI MASU NASABA

Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku

2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa

Dangane da haka ne rahotanni ke cewa Shugaba Tinubu na neman masana a ciki da wajen kasar nan domin su taimaka masa wajen samun nasarar gwamnatinsa.

A yau, akwai sassa takwas masu matukar muhimmanci da za su iya haifar da sauye-sauye na kasa ko su iya rage radadin zamantakewa da siyasa da tattalin arziki a kasar nan. Wadannan sun hada da tsaro, wutar lantarki, ilimi, kiwon lafiya, noma, aikin yi da kuma samar da muhimman ababen more rayuwa. Idan aka mayar da hankali kan wadannan muhimman bangarorin za iya kawo sauyi ga kasa.

Bayan nada manyan mukaman hafsoshin tsaro, akwai ministoci da za a nada a cikin majalisar zartarwar Tinubu. Tun da akwai jihohi 36, kowace jiha sai an samu wakilcin akalla mutum daya ko fiye da haka, yayin da wasu za su samu mukamin babban minista, wasu kuma su kasance kananan ministoci.

Ko shakka babu shugaban kasar na da ‘yancin nada majalisar ministocinsa kamar yadda tsarin mulki ya tanada. A wurin nada mukaman minista, akwai abubuwan da yaka mata shugaban kasa ya yi la’akari da su wajen dauko mutanen da suka cancanta.

Duk da cewa dole ne Shugaba Tinubu ya bi tsarin daidaito wajen nada mukamai a gwamnatin tarayya, wanda ke bukatar minista daya daga cikin jihohi 36, zai iya tankade da rairaya a tsakanin masu fasaha da ’yan siyasa. Babban abin da ake bukata wajen zaben ministocinsa shi ne, cancanta ba tare da nuna son rai ko raja’a ga jam’iyya ba.

An saba mafi yawanci ‘yan siyasa ne ake bai wa mukaman ministoci duk da cewa ana sirki da ma’aikata da kuma kwararru daga bangarori daban-daban.

A halin da kasar nan ke ciki, mafi yawancin ‘yan Nijeriya na tsammanin shugaban Tinubu ya nada ministocin da suka dace ba tare da nuna bambancin siyasa ko ta jam’iyya ba.

‘Yan Nijeriya na son ganin sauyi a kan ministocin baya domin samun nasarar gwamnati yadda ya kamata.

Tuni dai ana ta yada jita-jitar cewa wasu mutane suna ci gaba da kamun kafa tare da bayar da cin hanci domin a ba su mukaman ministoci a gwamnatin Tinubu. Hakan yana matukar tayar da jijiyar wuya, inda da yawa ke ganin cewa ya kamata shugaban kasa ya tsaya ya darje wadanda zai nada a matsayin ministoci domin samun nasarar gwamnatinsa.

Tsammani
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Rashin Tsaro Na Barazana Ga Zaben 2027 —Rahotanni
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?

MASU ALAKA

Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku
Tambarin Dimokuradiyya

Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku

June 19, 2026
2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa

June 12, 2026
Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?
Tambarin Dimokuradiyya

Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?

June 12, 2026
Next Post
An Bude Taron Duniya Kan Fasahar Kwaikwayon Tunanin Dan Adam Ta AI A Shanghai

An Bude Taron Duniya Kan Fasahar Kwaikwayon Tunanin Dan Adam Ta AI A Shanghai

LABARAI MASU NASABA

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

June 25, 2026
Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa’ — Atiku

June 25, 2026
Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.