• English
  • Business News
Wednesday, June 4, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Iyaye 34 Suka Yi Wa ‘Ya’yansu 48 Fyade Cikin Shekara 2

by Sabo Ahmad
3 years ago
in Kotu Da Ɗansanda
0
Iyaye 34 Suka Yi Wa ‘Ya’yansu 48 Fyade Cikin Shekara 2
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Labarai Masu Nasaba

‘Yansanda Sun Gurfanar Da Lauya A Abuja A Kotu Bisa Tuhumarsa Da Aikata Sojan Gona

Wasu ‘Yan Ta’adda Dauke Da Makamai Sun Harbi Limamin Katolika A Binuwe

Rahotanni sun tabbatar da cewa, a cikin shekara biyu da suka wuce,iyaye 34 ne suka yi wa ‘ya’yan cikinsu 48 fyade, a cikin wasu bayanai da jaridar ‘Daily Trust’ ta ranar Lahadi ta tattara.

Wannan lamarin ya faru ne a cikin jihohi 13.

  • ‘Muna Kira A Samar Da Jami’an Tsaro Na Yankin Arewacin Nijeriya’
  • Da Dumi-Dumi: Jami’an Tsaro Sun Kai Samame Gidan Tukur Mamu

Jihar Legas ita ke kan gaba da mutum 11 sai Ondo 5, sai Ekiti 4, sai Kwara 3, sai Ogun ita ma 3, sannan sai Abiya da Anambura da Kano da Delta da Osun da Katsina da Edo da kuma Kuros Riba wadanda kuma kowannensu ke da daya.
Kamar yadda kididdigar ta nuan,daga cikin matsalolin 46 da suka faru, daya daga cikinsu jaririya ce, hudu kuma ‘yan kananan yara ne,sauran kuma kananan ‘yan mata guda 15.
Labari na baya-bayan nan da aka samu shi ne, a cikin watan Agusta, 2022, shi ne, na wani mai gadi mai kimanin shekara 55, mai suna Arowolo Ayodeji, ya yi wa ‘yarsa mai kimanin shekara 19 fyade a garin Ipoti da ke jihar Ekiti.
Da aka tambayi mahaifin yarinyar ko mai ya sa ya yi wannan danyrn aik? Sai ya ce, sharrin Shaidan ne, “Ba aikina ba ne.”
Mai magana da yawun jami’an tsaro na Sibil Difens (NSCDC) Olasunkanmi Ayeni, ya bayyana cewa, mutumin ya fara tursasa wa yarinyar tun tana ‘yar shekara bakwai.
“Wato zuwa yanzu ya shafe shekara biyu yana aikata wannan laifin ke nan,” In ji Mista Ayeni.
Ranar 19, ga watan Fabarairu 2022, haka kuma wani mutum mai shekara 28, mai suna Audu Dare, wanda ya yi wa ‘yarsa fyade mai shekara 6, wanda hakan ya yi sanadiyyar mutuwarta, sakamakon haka aka tsare shi a Ado Ekiti.
Matar da Dare ya ci gaba da bibiya wata mai suna Eniola Aina, wadda ta ce sun taba yin aure a shekarun baya, kuma har ma sun haifi da namiji amma sai suka rabu, shekara hudu da suka wuce sakamakon wasu munanan halayensa.
“Bayan rabuwarmu, wata rana, sai ya zo gidana da ke garin Ilawe Ekiti ya ce, zai karbi ‘yarsa, ni kuma na ce, ba zan ba shi ba, sai ya dawo da misalin karfe 12 na dare ya sace ta”.
“Bayan ‘yan kwanaki kadan sai yarinya ta fara kukan ciwon kai sannan kuma ta ce mafitsararta na yi mata zafi. Nan da nan aka kai ta wani asibiti da ke kusa da su, a nan ne ta gaya min cewa, babanta ya yi mata fyade wanda kuma hakan ta yi sanadiyyar mutuwarta.”
Haka kuma a wani makamancin wannan an kama wani mutum mai ‘ya’ya shida, mai suna Sunday Julius, yana lalata da kananan ‘ya’yansa guda hudu, daya mai shekara bakwai da mai shekara 10 da wata mai shekara 11 da kuma wata mai shekara15, a jihar Legas.
Julius, ya ce yana zaune da iyalansa ne a wata unguwa da ake kira Alimosho da ke jihar, kuma matarsa ta sha kama shi da yaran.
“Mun yi aure a shekara ta 2007 kuma mun haifi ‘ya’ya shida tare”.
“Yarmu ta farko mai kimanin shekara 15, ta sha gaya min cewa, da zarar sun kwanta da daddare sai ya lallabo wajen da take kwanciya,ya fara amfani da ita”.
“Haka yake binmu, mu hudu daya bayan daya, idan muka ki ya tursasa mana dole”.
“Ya kan shigo dakin namu ne cikin tsakiyar dare yayin da muke cikin bacci. Yana kuma tsorata su da zarar ya ga alamar ba za su yar da ba. Muna kwanta tare da dare ya yi, sai ya kashe wuta, ya lallaba ya tafi inda yarinyarmu mai shekara 10 ke kwana, ya je ya sadu da ita.
Sai da gari ya waye, na gaya masa cewa, na gan shi yana lalata da yarinyata, ya ce, karya nake yi masa. Saboda haka kwana hudu sai na daina yin girki sai ya yi fushi har yana dukana,” matar mai shekara 36, wadda ke sasayar da magungunan gargajiya ta ce ita Bayarabiya ce.
Babbar ‘yar mutumin mai shekara 15, wadda a halin yanzu take sakandire, ita ta tona asiri, wadda ta ce babanta yana saduwa da ita duk loacin da ta dawo gida daga makaranta. Ta ce, “Ina son in tube kayana lokacin da baban yake shigo wa. Domin yana kwantar da ni a gado, yana saduwa da ni”.
“Lokacin da yake saduwa da ni, sai kanwa ta, sai nan da nan ya daga ni. Sai take tambaya menene yake faruwa sai na yi mata. Ita kuma sai ta gaya wa babarmu. Sai babarmu ta ce, ai ni ce da laifi da ban gaya mat aba tun da wuri. Sai na ce mata ni ina jin tsoron gaya mata ne, domin baban nawa ya ce in na gaya miki zai kashe ni.”
Ashe ni ban san akwai wasu ‘yan uwan wannan yarinyar guda biyu da yake saduwa da su ba, daya mai shekara 7 da kuma mai shekara 11 wadanda suka ce babansu na tursasa musu har sai sun sadu da shi da daddare kuma ya ja musu kunne cewa, kada su sake su gaya wa wani. Daya daga cikinsu mai kimanin shekara 10 ta ce “Babana yana tursasa mini da daddare.”
Da aka tambaye su mai ya sa ba su fada ba tuntuni, sai suka ce, baban nasu ne ya ce, kada su kuskura su fada wa kowa.
Haka kuma a wata makamanciyar wannan da ta faru a garin Ile-Oluji da ke jihar Ondo, an kama wani dansanda mai suna Sunday Udoh, mai shekara 38, yana kokarin tursasa wa ‘yarsa ta zubar da cikin da ya yi mata.
Jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yansandan jihar Ondo Funmilayo Odunlami, ya bayyana haka, sannan kuma ya tabbatar da cewa, tuni sun kama wanda ake zargin, kuma yanzu haka yana garkame a hedikwatar ‘yansanda da ke Ile-Oluji, wanda kuma ya nuna inda aka zubar da cikin.
“Lokacin da ake bincike an gano cewa, matar wanda ake zargin wadda aka sakaya sunanta ta bukaci a zubar da cikin ‘yartatata mai kimanin shekara 15 wadda ta samu daga mahaifinta.
“Yanzu haka dai an mika wannan bincike zuwa sashin binciken manyan laifuka da ke Akure,” in ji shi.
Mako guda kafin wannan lokaci ‘yansanda a jihar sun kama wani uba mai kimanin shekara 27 mai suna Adeniyi Adeleke, bisa zargin yi wa ‘yarsa fyade mai kimanin shekara 10.
Haka kuma ‘yansanda sun nuna Mista Adeleke da wani mai shekara 46 mai suna Jimoh Rafiu wadanda suka yi wa yarinya mai shekara shida fyade.
Sannan ta nuna mikin da daya daga cikinsu ya yi mata lokacin da yake kokarin saduwa da ita.
Mahaifiyar yarinyar ta ce, duk lokacin da ta dawo daga wajen aiki, sai kawai mijin nata ya cire wa ‘yarsa kayan jikinta, ya ce, yana bukatar ya sadu da ita.
Bayan da ta fara jin ciwon mara da kafafrwanta sai ta gaya wa babarta, sai babartata, ta je wajrn mijin nata, sakamakon jin wannan labara.
Daga nan sai ta kai kara gurin dattawan gari inda suka kira shi, suka gurfanar da shi, a nan ya yi alkawarin cewa, ba zai sake yin haka ba.
Bayan ‘yan kwanaki, sai yarinyar ta samu sauki, daga nan ne sai uwar yarinyar ta kai kara ofishin ‘yansanda da ke Jimoh.
A nan ma Jimoh ya tabbatar da aikata laifin da ake zarginsa da shi, na yi wa matarsa fyade lokacin da ya sha giya. Mutane da yawa sun yi mamakin yadda wannan mutum ya fada tarkon shaidan.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: BincikeFyadeIyayeMataRahotoYara
ShareTweetSendShare
Previous Post

Zabar Musulmi Da Musulmi Da APC Ta Yi Ba Illa Ba Ce -Hon. Auwalu Ladan Garba

Next Post

Yadda Na Zama Babbar Lauya A Kotun Birtaniya —Munayah Hassan

Related

‘Yan Sanda Sun Kama Mutum 2 Kan Zargin Jefe Wani Direba Har Lahira A Ondo
Kotu Da Ɗansanda

‘Yansanda Sun Gurfanar Da Lauya A Abuja A Kotu Bisa Tuhumarsa Da Aikata Sojan Gona

4 days ago
Wasu ‘Yan Ta’adda Dauke Da Makamai Sun Harbi Limamin Katolika A Binuwe
Kotu Da Ɗansanda

Wasu ‘Yan Ta’adda Dauke Da Makamai Sun Harbi Limamin Katolika A Binuwe

4 days ago
Yaki Da Miyagun Kwayoyi: Kamfanin LEADERSHIP Da NDLEA Sun Kulla Kawance
Kotu Da Ɗansanda

NDLEA Ta Kama Wani Mutum Mai Shekaru 75 Da Laifin Safarar Muggan Kwayoyi

2 months ago
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba
Kotu Da Ɗansanda

‘Yansanda Sun Kama Mutum 245 Da Miyagun Kwayoyi Da Makamai A Abuja

3 months ago
‘Yansanda A Legas Sun Kama Mutum 35 Da Ake Zargi Da Fashi Cikin Mako Guda
Kotu Da Ɗansanda

‘Yansanda A Legas Sun Kama Mutum 35 Da Ake Zargi Da Fashi Cikin Mako Guda

3 months ago
A Kama Wani Likitan Bogi A Neja
Kotu Da Ɗansanda

‘Yansanda Na Farautar Wadanda Suka Kashe Dalibi A Katsina

3 months ago
Next Post
Yadda Na Zama Babbar Lauya A Kotun Birtaniya —Munayah Hassan

Yadda Na Zama Babbar Lauya A Kotun Birtaniya —Munayah Hassan

LABARAI MASU NASABA

DSS

DSS Da Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga 45 A Neja

June 4, 2025
Gwamna Bago Ya Amince Da Biyan Karin Albashin Naira 20,000 Ga Ma’aikata 

Yanzu-yanzu: Gwamnatin Neja Ta Soke Hawan Sallah Sakamakon Ambaliyar Ruwan Mokwa

June 4, 2025
katsina

Gwamnan Katsina Ya Bukaci Hadin Gwiwa Da ‘Yan Kasuwa Domin Cigaban Jihar

June 4, 2025
Ambaliya: Gwamna Zulum Ya Kaddamar Da Rabon Kayan Agaji A Borno

Zulum Ya Yaba Wa Sojoji Kan Kashe Babban Kwamandan ISWAP Abu Fatima

June 4, 2025
Manufar Bude Kofa Ta Shaida Niyyar Sin Ta Ingiza Dunkulewar Duniya

Manufar Bude Kofa Ta Shaida Niyyar Sin Ta Ingiza Dunkulewar Duniya

June 3, 2025
Kocin Inter Milan Simone Inzaghi Ya Bar Kungiyar Kwanaki Biyu Bayan Rashin Nasara A Hannun PSG

Kocin Inter Milan Simone Inzaghi Ya Bar Kungiyar Kwanaki Biyu Bayan Rashin Nasara A Hannun PSG

June 3, 2025
Sin Ta Yi Fatali Da Ikirarin Amurka Cewa Ta Karya Yarjejeniyar Tattaunawar Geneva

Sin Ta Yi Fatali Da Ikirarin Amurka Cewa Ta Karya Yarjejeniyar Tattaunawar Geneva

June 3, 2025
Karuwar Darajar Sana’ar Samar Da Kayan Laturoni Da Dangoginsu a Sin Cikin Watanni 4 Na Farkon Bana Ya Karu Da 11.3% 

Karuwar Darajar Sana’ar Samar Da Kayan Laturoni Da Dangoginsu a Sin Cikin Watanni 4 Na Farkon Bana Ya Karu Da 11.3% 

June 3, 2025
Sanusi

‘Yansanda A Kano Sun Gargaɗi Sarki Sanusi II Kan Fitowa Hawan Sallah

June 3, 2025
Masani Kwadifwa: Kasar Sin Ce Mai Kare Tabbatuwar Adalci A Duniya

Masani Kwadifwa: Kasar Sin Ce Mai Kare Tabbatuwar Adalci A Duniya

June 3, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.