• English
  • Business News
Sunday, June 29, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Jadawalin Tsare-Tsaren Bikin Mika Mulki Daga Shugaba Buhari Zuwa Bola Tinubu

Gwamnatin Nijeriya ta fitar da tsarin bikin mika mulki na mako daya tsakanin Shugaba Buhari da shugaba mai jiran gado Bola Ahmad Tinubu.

by Muhammad
2 years ago
in Manyan Labarai
0
Ku Zabi Tunibu Na Yi Imani Zai Dora Daga Inda Na Tsaya — Buhari
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kafar yada labarai ta TRT Hausa, ta rawaito cewa, Gwamnatin Nijeriya ta fitar da jadawalin mako daya na bikin mika wa zababben shugaban kasar Bola Tinubu mulki ranar 29 ga watan Mayu don zama shugaban kasar na 16.

Sakataren Gwamnatin kasar kuma shugaban kwamitin mika mulki, Boss Mustapha, ya bayyana ranar Alhamis cewa za a yi shagali na mako daya zuwa 29 ga watan Mayu ranar da Shugaba Muhammadu Buhari zai mika mulki ga shugaba mai jiran gado Bola Tinubu.

  • Shirye-shiryen Saukar Buhari Mulki…
  • Gwamnatin Birtaniya Ta Taya Tunibu Murnar Lashe Zaben Shugaban Kasa

Da yake jawabi ga manema labarai a Abuja, babban birnin kasar Boss Mustapha ya ce ranar Talata, 23 ga watan Mayu 23, za a yi liyafa ta girmamawa ta soji ga shugaba mai barin gado, Muhammadu Buhari.

Ranar 24 ga watan Mayu 24 (Laraba), za a yi taron bankwana na Majalisar Ministoci a Fadar shugaban kasa da ke Abuja.

Kazalika ranar 25 ga watan Mayu (Alhamis), za a karrama Tinubu da babban lambar yabo ta GCFR da ake bai wa shugabannin kasa kadai. Har wa yau a ranar, Buhari zai karbi lambar yabo ta GCON da ake bai wa tsofaffin shugabannin kasar. A yayin bikin, Buhari zai mika takardun mika mulki ga Tinubu.

Labarai Masu Nasaba

Tinubu Ya Isa Saint Lucia Domin Ziyarar Aiki

Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

A ranar 26 ga watan Mayu (Juma’a), za a gabatar da lacca da sallar Juma’a a babban masallacin kasa da ke Abuja tsakanin karfe 10 na safe zuwa 1:30 na rana.

A ranar 27 ga watan Mayu (Asabar), Tsohon shugaban kasar Kenya, Uhuru Kenyatta, zai ba da lacca kan “hanyoyin zurfafa dimokuradiyya don cudanya da ci gaba”.

A ranar 28 ga watan Mayu (Lahadi), za a gudanar da taro na mabiya addinin Kirista a cibiyar kiristoci ta kasa da ke Abuja. A yammacin ranar, Shugaba Buhari zai karbi bakuncin baki da suka zo don a yi liyafar cin abincin dare a dakin taro na fadar gwamnati.

A ranar 29 ga Mayu (Litinin), Tinubu zai yi rantsuwar kama aiki a dandalin Eagle Square da ke Abuja da misalin karfe 10 na safe agogon kasar. Haka kuma za a gudanar da faretin kaddamarwa.

Sannan kuma za a gudanar da liyafar cin abincin rana bayan rantsar da shi a dakin taro na Banquet House da misalin karfe 1:30 na rana. Tinubu ne ya shirya liyafar, kuma ana sa ran shugabannin kasashen da aka gayyato da shugabannin gwamnati da manyan baki ne kawai za su halarci taron.

Kwamitin mika mulki ya ce an gayyaci shugabannin kasashe da na gwamnati da dama, kuma akasarinsu sun ba da tabbacin cewa za su halarci bikin mika mulkin Nijeriya ga Bola Tinubu.

Shugaban kwamitin, Boss Mustapha, ya ce ba zai iya bayyana adadin ko sunayen shugabannin da aka gayyata ba saboda “sha’ani na tsaro”.

Tinubu, wanda ya yi takara a jam’iyyar APC mai rike da mulki, ya samu kuri’u miliyan 8.8 kuma an ayyana shi a matsayin wanda ya lashe zaben shugaban kasar Nijeriya da aka gudanar a watan Fabrairun 2023.

Atiku Abubakar na jam’iyyar PDP ya zo na biyu da kuri’u miliyan 7, yayin da Peter Obi na jam’iyyar Labour ya zo na uku da kuri’u miliyan 6.1.

Atiku da Obi sun yi wasti da sakamakon zaben, kuma sun shigar da kara a gaban kotun zabe, suna kalubalantar nasarar da Tinubu ya samu.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: BuhariTunibu
ShareTweetSendShare
Previous Post

NSCDC Ta Cafke Mutum 9 Kan Zargin Satar Sinadarin Ruwa A Zamfara

Next Post

Shugabancin Majalisa Ta 10: Hannun Agogo Na Neman Koma Wa APC Baya

Related

Tinubu Ya Isa Saint Lucia Domin Ziyarar Aiki
Manyan Labarai

Tinubu Ya Isa Saint Lucia Domin Ziyarar Aiki

2 hours ago
Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa
Manyan Labarai

Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

16 hours ago
An Kai Wa Magoya Bayan Atiku Hari A Gombe
Manyan Labarai

Rasuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Afirka – Atiku

18 hours ago
Rasuwar Ɗantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya –  Shugaban ƘasaTinubu
Manyan Labarai

Rasuwar Ɗantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya –  Shugaban ƘasaTinubu

20 hours ago
Bam Ya Kashe Mutane 4, Ya Jikkata 21 A Yobe
Manyan Labarai

Bam Ya Kashe Mutane 4, Ya Jikkata 21 A Yobe

21 hours ago
Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Demokuradiyyar Nijeriya Daga Rugujewa
Manyan Labarai

Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Demokuradiyyar Nijeriya Daga Rugujewa

21 hours ago
Next Post
Shugabancin Majalisa Ta 10: Hannun Agogo Na Neman Koma Wa APC Baya

Shugabancin Majalisa Ta 10: Hannun Agogo Na Neman Koma Wa APC Baya

LABARAI MASU NASABA

Tinubu Ya Isa Saint Lucia Domin Ziyarar Aiki

Tinubu Ya Isa Saint Lucia Domin Ziyarar Aiki

June 29, 2025
Kasar Sin Ta Sake Ware Yuan Miliyan 100 Domin Tallafawa Lardin Guizhou Dake Fama Da Ambaliya 

Kasar Sin Ta Sake Ware Yuan Miliyan 100 Domin Tallafawa Lardin Guizhou Dake Fama Da Ambaliya 

June 28, 2025
An Kaddamar Da Aikin Hadin-Gwiwar Kafafen Yada Labaran Sin Da Kasashen Waje Wajen Watsa Labarai Game Da Jihar Xizang Ta Kasar Sin

An Kaddamar Da Aikin Hadin-Gwiwar Kafafen Yada Labaran Sin Da Kasashen Waje Wajen Watsa Labarai Game Da Jihar Xizang Ta Kasar Sin

June 28, 2025
Jakadun Kasa Da Kasa Sun Bayyana Muhimmancin Hadin Gwiwa Wajen Amfani Da Makamashin Nukiliya Ta Hanyar Lumana

Jakadun Kasa Da Kasa Sun Bayyana Muhimmancin Hadin Gwiwa Wajen Amfani Da Makamashin Nukiliya Ta Hanyar Lumana

June 28, 2025
Kokarin Zamanantar Da Sin Da Afrika Na Kara Karfafa

Kokarin Zamanantar Da Sin Da Afrika Na Kara Karfafa

June 28, 2025
Bashin Da Ake Bin Nijeriya Ya Kai Tiriliyan 46.25

Za A Ci Gaba Da Tunawa Da Aminu Ɗantata A Ɓangaren Taimakon Jama’a — Buhari

June 28, 2025
Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

June 28, 2025
Hukumar NPA Na Son Tara Kuɗaɗen Shiga Naira Tiriliyan 1.2 A 2025

Hukumar NPA Na Son Tara Kuɗaɗen Shiga Naira Tiriliyan 1.2 A 2025

June 28, 2025
An Horas Da Kwararrun Ma’aikata Sama Da Dubu 500 Karkashin Hadin Gwiwar Sin Da Sassan Kasa Da Kasa A Fannin Inganta Kwarewar Ma’aikata

An Horas Da Kwararrun Ma’aikata Sama Da Dubu 500 Karkashin Hadin Gwiwar Sin Da Sassan Kasa Da Kasa A Fannin Inganta Kwarewar Ma’aikata

June 28, 2025
Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (3)

Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (3)

June 28, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.