• English
  • Business News
Friday, June 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Jadawalin Tsare-Tsaren Bikin Mika Mulki Daga Shugaba Buhari Zuwa Bola Tinubu

Gwamnatin Nijeriya ta fitar da tsarin bikin mika mulki na mako daya tsakanin Shugaba Buhari da shugaba mai jiran gado Bola Ahmad Tinubu.

by Muhammad
2 years ago
in Manyan Labarai
0
Ku Zabi Tunibu Na Yi Imani Zai Dora Daga Inda Na Tsaya — Buhari
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kafar yada labarai ta TRT Hausa, ta rawaito cewa, Gwamnatin Nijeriya ta fitar da jadawalin mako daya na bikin mika wa zababben shugaban kasar Bola Tinubu mulki ranar 29 ga watan Mayu don zama shugaban kasar na 16.

Sakataren Gwamnatin kasar kuma shugaban kwamitin mika mulki, Boss Mustapha, ya bayyana ranar Alhamis cewa za a yi shagali na mako daya zuwa 29 ga watan Mayu ranar da Shugaba Muhammadu Buhari zai mika mulki ga shugaba mai jiran gado Bola Tinubu.

  • Shirye-shiryen Saukar Buhari Mulki…
  • Gwamnatin Birtaniya Ta Taya Tunibu Murnar Lashe Zaben Shugaban Kasa

Da yake jawabi ga manema labarai a Abuja, babban birnin kasar Boss Mustapha ya ce ranar Talata, 23 ga watan Mayu 23, za a yi liyafa ta girmamawa ta soji ga shugaba mai barin gado, Muhammadu Buhari.

Ranar 24 ga watan Mayu 24 (Laraba), za a yi taron bankwana na Majalisar Ministoci a Fadar shugaban kasa da ke Abuja.

Kazalika ranar 25 ga watan Mayu (Alhamis), za a karrama Tinubu da babban lambar yabo ta GCFR da ake bai wa shugabannin kasa kadai. Har wa yau a ranar, Buhari zai karbi lambar yabo ta GCON da ake bai wa tsofaffin shugabannin kasar. A yayin bikin, Buhari zai mika takardun mika mulki ga Tinubu.

Labarai Masu Nasaba

Sarki Sanusi II Ya Soke Hawan Sallah, Ya Bayyana Dalili

Saƙon Barka Da Sallah: Tinubu Ya Baiyana Tabbacin Ci Gaban Nijeriya, Da Sauyin Tattalin Arziƙi

A ranar 26 ga watan Mayu (Juma’a), za a gabatar da lacca da sallar Juma’a a babban masallacin kasa da ke Abuja tsakanin karfe 10 na safe zuwa 1:30 na rana.

A ranar 27 ga watan Mayu (Asabar), Tsohon shugaban kasar Kenya, Uhuru Kenyatta, zai ba da lacca kan “hanyoyin zurfafa dimokuradiyya don cudanya da ci gaba”.

A ranar 28 ga watan Mayu (Lahadi), za a gudanar da taro na mabiya addinin Kirista a cibiyar kiristoci ta kasa da ke Abuja. A yammacin ranar, Shugaba Buhari zai karbi bakuncin baki da suka zo don a yi liyafar cin abincin dare a dakin taro na fadar gwamnati.

A ranar 29 ga Mayu (Litinin), Tinubu zai yi rantsuwar kama aiki a dandalin Eagle Square da ke Abuja da misalin karfe 10 na safe agogon kasar. Haka kuma za a gudanar da faretin kaddamarwa.

Sannan kuma za a gudanar da liyafar cin abincin rana bayan rantsar da shi a dakin taro na Banquet House da misalin karfe 1:30 na rana. Tinubu ne ya shirya liyafar, kuma ana sa ran shugabannin kasashen da aka gayyato da shugabannin gwamnati da manyan baki ne kawai za su halarci taron.

Kwamitin mika mulki ya ce an gayyaci shugabannin kasashe da na gwamnati da dama, kuma akasarinsu sun ba da tabbacin cewa za su halarci bikin mika mulkin Nijeriya ga Bola Tinubu.

Shugaban kwamitin, Boss Mustapha, ya ce ba zai iya bayyana adadin ko sunayen shugabannin da aka gayyata ba saboda “sha’ani na tsaro”.

Tinubu, wanda ya yi takara a jam’iyyar APC mai rike da mulki, ya samu kuri’u miliyan 8.8 kuma an ayyana shi a matsayin wanda ya lashe zaben shugaban kasar Nijeriya da aka gudanar a watan Fabrairun 2023.

Atiku Abubakar na jam’iyyar PDP ya zo na biyu da kuri’u miliyan 7, yayin da Peter Obi na jam’iyyar Labour ya zo na uku da kuri’u miliyan 6.1.

Atiku da Obi sun yi wasti da sakamakon zaben, kuma sun shigar da kara a gaban kotun zabe, suna kalubalantar nasarar da Tinubu ya samu.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: BuhariTunibu
ShareTweetSendShare
Previous Post

NSCDC Ta Cafke Mutum 9 Kan Zargin Satar Sinadarin Ruwa A Zamfara

Next Post

Shugabancin Majalisa Ta 10: Hannun Agogo Na Neman Koma Wa APC Baya

Related

Sarki Sanusi II Ya Soke Hawan Sallah, Ya Bayyana Dalili
Manyan Labarai

Sarki Sanusi II Ya Soke Hawan Sallah, Ya Bayyana Dalili

1 hour ago
Saƙon Barka Da Sallah: Tinubu Ya Baiyana Tabbacin Ci Gaban Nijeriya, Da Sauyin Tattalin Arziƙi
Manyan Labarai

Saƙon Barka Da Sallah: Tinubu Ya Baiyana Tabbacin Ci Gaban Nijeriya, Da Sauyin Tattalin Arziƙi

3 hours ago
Abubuwan Da Ba A Fada Ba Game Da Mummunar Ambaliyar Ruwan Mokwa
Manyan Labarai

Abubuwan Da Ba A Fada Ba Game Da Mummunar Ambaliyar Ruwan Mokwa

4 hours ago
Hukumar kashe gobara
Manyan Labarai

An Samu Asarar Dukiya ta Miliyan ₦273, Tare Da Mutuwar Mutum 5 A Kano – Hukuma

18 hours ago
Kashinku Ya Bushe: Sojoji Sun Lashi Takobin Kawo Ƙarshen ‘Yan Ta’adda A Zamfara Da Katsina 
Manyan Labarai

Kashinku Ya Bushe: Sojoji Sun Lashi Takobin Kawo Ƙarshen ‘Yan Ta’adda A Zamfara Da Katsina 

24 hours ago
An Kashe Wani, Wasu Sun Jikkata A Rikicin Manoma Da Makiyaya A Neja
Manyan Labarai

An Kashe Wani, Wasu Sun Jikkata A Rikicin Manoma Da Makiyaya A Neja

1 day ago
Next Post
Shugabancin Majalisa Ta 10: Hannun Agogo Na Neman Koma Wa APC Baya

Shugabancin Majalisa Ta 10: Hannun Agogo Na Neman Koma Wa APC Baya

LABARAI MASU NASABA

Ministan Tsaro

Ministan Tsaro Ya Yi Gargadin Sake Dawowar Boko Haram Na Barazana Ga Nijeriya

June 6, 2025
Sarki Sanusi II Ya Soke Hawan Sallah, Ya Bayyana Dalili

Sarki Sanusi II Ya Soke Hawan Sallah, Ya Bayyana Dalili

June 6, 2025
Yadda Manzon Allah (SAW) Ya Yi Aikin Hajji (3)

Yadda Manzon Allah (SAW) Ya Yi Aikin Hajji (3)

June 6, 2025
Ambaliyar Ruwa A Mokwa: Kauyuka 1,249 A Jihohi 30 Na Cikin Hadari — Gwamnatin Tarayya

Ambaliyar Ruwa A Mokwa: Kauyuka 1,249 A Jihohi 30 Na Cikin Hadari — Gwamnatin Tarayya

June 6, 2025
Saƙon Barka Da Sallah: Tinubu Ya Baiyana Tabbacin Ci Gaban Nijeriya, Da Sauyin Tattalin Arziƙi

Saƙon Barka Da Sallah: Tinubu Ya Baiyana Tabbacin Ci Gaban Nijeriya, Da Sauyin Tattalin Arziƙi

June 6, 2025
Abubuwan Da Ba A Fada Ba Game Da Mummunar Ambaliyar Ruwan Mokwa

Abubuwan Da Ba A Fada Ba Game Da Mummunar Ambaliyar Ruwan Mokwa

June 6, 2025
Shugabannin Sin Da Amurka Sun Tattauna Ta Wayar Tarho

Shugabannin Sin Da Amurka Sun Tattauna Ta Wayar Tarho

June 6, 2025
Xi Da Trump Sun Tattauna Ta Wayar Tarho

Xi Da Trump Sun Tattauna Ta Wayar Tarho

June 5, 2025
Kasar Sin Ta Bukaci Amurka Ta Yi Watsi Da Amfani Da Batun Tsaron Kasa Barkatai

Kasar Sin Ta Bukaci Amurka Ta Yi Watsi Da Amfani Da Batun Tsaron Kasa Barkatai

June 5, 2025
Wani Matashi Dan Shekara 33 Ya Rasu Bayan Ya Fada Wata Tsohuwar Rijiya A Kano

Wani Matashi Dan Shekara 33 Ya Rasu Bayan Ya Fada Wata Tsohuwar Rijiya A Kano

June 5, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.