• English
  • Business News
Friday, July 11, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Jadawalin Tsare-Tsaren Bikin Mika Mulki Daga Shugaba Buhari Zuwa Bola Tinubu

Gwamnatin Nijeriya ta fitar da tsarin bikin mika mulki na mako daya tsakanin Shugaba Buhari da shugaba mai jiran gado Bola Ahmad Tinubu.

by Muhammad
2 years ago
in Manyan Labarai
0
Ku Zabi Tunibu Na Yi Imani Zai Dora Daga Inda Na Tsaya — Buhari
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kafar yada labarai ta TRT Hausa, ta rawaito cewa, Gwamnatin Nijeriya ta fitar da jadawalin mako daya na bikin mika wa zababben shugaban kasar Bola Tinubu mulki ranar 29 ga watan Mayu don zama shugaban kasar na 16.

Sakataren Gwamnatin kasar kuma shugaban kwamitin mika mulki, Boss Mustapha, ya bayyana ranar Alhamis cewa za a yi shagali na mako daya zuwa 29 ga watan Mayu ranar da Shugaba Muhammadu Buhari zai mika mulki ga shugaba mai jiran gado Bola Tinubu.

  • Shirye-shiryen Saukar Buhari Mulki…
  • Gwamnatin Birtaniya Ta Taya Tunibu Murnar Lashe Zaben Shugaban Kasa

Da yake jawabi ga manema labarai a Abuja, babban birnin kasar Boss Mustapha ya ce ranar Talata, 23 ga watan Mayu 23, za a yi liyafa ta girmamawa ta soji ga shugaba mai barin gado, Muhammadu Buhari.

Ranar 24 ga watan Mayu 24 (Laraba), za a yi taron bankwana na Majalisar Ministoci a Fadar shugaban kasa da ke Abuja.

Kazalika ranar 25 ga watan Mayu (Alhamis), za a karrama Tinubu da babban lambar yabo ta GCFR da ake bai wa shugabannin kasa kadai. Har wa yau a ranar, Buhari zai karbi lambar yabo ta GCON da ake bai wa tsofaffin shugabannin kasar. A yayin bikin, Buhari zai mika takardun mika mulki ga Tinubu.

Labarai Masu Nasaba

‘Yan Bindiga Sun Kai Wa ‘Yansanda Hari Tare Da Kashe Wani Mutum Da Raunata Wani A Nasarawa

An Koka Kan Yadda Tsafi Da Jariran Da Aka Haifa Da Tsagaggen Lebe Ke Karuwa

A ranar 26 ga watan Mayu (Juma’a), za a gabatar da lacca da sallar Juma’a a babban masallacin kasa da ke Abuja tsakanin karfe 10 na safe zuwa 1:30 na rana.

A ranar 27 ga watan Mayu (Asabar), Tsohon shugaban kasar Kenya, Uhuru Kenyatta, zai ba da lacca kan “hanyoyin zurfafa dimokuradiyya don cudanya da ci gaba”.

A ranar 28 ga watan Mayu (Lahadi), za a gudanar da taro na mabiya addinin Kirista a cibiyar kiristoci ta kasa da ke Abuja. A yammacin ranar, Shugaba Buhari zai karbi bakuncin baki da suka zo don a yi liyafar cin abincin dare a dakin taro na fadar gwamnati.

A ranar 29 ga Mayu (Litinin), Tinubu zai yi rantsuwar kama aiki a dandalin Eagle Square da ke Abuja da misalin karfe 10 na safe agogon kasar. Haka kuma za a gudanar da faretin kaddamarwa.

Sannan kuma za a gudanar da liyafar cin abincin rana bayan rantsar da shi a dakin taro na Banquet House da misalin karfe 1:30 na rana. Tinubu ne ya shirya liyafar, kuma ana sa ran shugabannin kasashen da aka gayyato da shugabannin gwamnati da manyan baki ne kawai za su halarci taron.

Kwamitin mika mulki ya ce an gayyaci shugabannin kasashe da na gwamnati da dama, kuma akasarinsu sun ba da tabbacin cewa za su halarci bikin mika mulkin Nijeriya ga Bola Tinubu.

Shugaban kwamitin, Boss Mustapha, ya ce ba zai iya bayyana adadin ko sunayen shugabannin da aka gayyata ba saboda “sha’ani na tsaro”.

Tinubu, wanda ya yi takara a jam’iyyar APC mai rike da mulki, ya samu kuri’u miliyan 8.8 kuma an ayyana shi a matsayin wanda ya lashe zaben shugaban kasar Nijeriya da aka gudanar a watan Fabrairun 2023.

Atiku Abubakar na jam’iyyar PDP ya zo na biyu da kuri’u miliyan 7, yayin da Peter Obi na jam’iyyar Labour ya zo na uku da kuri’u miliyan 6.1.

Atiku da Obi sun yi wasti da sakamakon zaben, kuma sun shigar da kara a gaban kotun zabe, suna kalubalantar nasarar da Tinubu ya samu.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: BuhariTunibu
ShareTweetSendShare
Previous Post

NSCDC Ta Cafke Mutum 9 Kan Zargin Satar Sinadarin Ruwa A Zamfara

Next Post

Shugabancin Majalisa Ta 10: Hannun Agogo Na Neman Koma Wa APC Baya

Related

Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga Tare Da Kwato Makamai A Jihar Filato
Manyan Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kai Wa ‘Yansanda Hari Tare Da Kashe Wani Mutum Da Raunata Wani A Nasarawa

15 minutes ago
An Koka Kan Yadda Tsafi Da Jariran Da Aka Haifa Da Tsagaggen Lebe Ke Karuwa
Manyan Labarai

An Koka Kan Yadda Tsafi Da Jariran Da Aka Haifa Da Tsagaggen Lebe Ke Karuwa

31 minutes ago
Rikicin Masarautar Kano Ya Kara Zafafa
Manyan Labarai

Rikicin Masarautar Kano Ya Kara Zafafa

5 hours ago
Yunkurin Magance Matsalar Tsaro Da Rigingimu A Arewa…
Manyan Labarai

Akwai Bukatar Hada Kai Da Aiki Tare Tsakanin Hukumomin Tsaro

6 hours ago
Ƴan Bindiga Sun Yi Wa Jami’an NSCDC Ƙwantan Ɓauna A Binuwe
Manyan Labarai

Ƴan Bindiga Sun Yi Wa Jami’an NSCDC Ƙwantan Ɓauna A Binuwe

16 hours ago
Kotun Ƙoli Ta Tabbatar Da Okpebholo A Matsayin Zaɓaɓɓen Gwamnan Edo
Da ɗumi-ɗuminsa

Kotun Ƙoli Ta Tabbatar Da Okpebholo A Matsayin Zaɓaɓɓen Gwamnan Edo

1 day ago
Next Post
Shugabancin Majalisa Ta 10: Hannun Agogo Na Neman Koma Wa APC Baya

Shugabancin Majalisa Ta 10: Hannun Agogo Na Neman Koma Wa APC Baya

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga Tare Da Kwato Makamai A Jihar Filato

‘Yan Bindiga Sun Kai Wa ‘Yansanda Hari Tare Da Kashe Wani Mutum Da Raunata Wani A Nasarawa

July 11, 2025
Goron Sallah

GORON JUMA’A

July 11, 2025
An Koka Kan Yadda Tsafi Da Jariran Da Aka Haifa Da Tsagaggen Lebe Ke Karuwa

An Koka Kan Yadda Tsafi Da Jariran Da Aka Haifa Da Tsagaggen Lebe Ke Karuwa

July 11, 2025
Bafarawa Ya Kaddamar Da Kungiyar Hada Kan Arewa Da Samar Da Zaman lafiya A Kaduna 

Bafarawa Ya Kaddamar Da Kungiyar Hada Kan Arewa Da Samar Da Zaman lafiya A Kaduna 

July 11, 2025
Hadarin Da Ke Kunshe Da Jin Bangare Daya Na Labari

Hadarin Da Ke Kunshe Da Jin Bangare Daya Na Labari

July 11, 2025
NPA Ta Yi Wa Ma’aikatanta 1,500 Karin Girma

NPA Ta Yi Wa Ma’aikatanta 1,500 Karin Girma

July 11, 2025
Shirin Sabunta Fata Na Tinubu Yana Samar da Damarmakin Cigaba — Minista

Shirin Sabunta Fata Na Tinubu Yana Samar da Damarmakin Cigaba — Minista

July 11, 2025
NPA Ta Tarbi Babban Jirgin ‘Ruwa MB Ocean Dragon’ Don Bunkasa Ayyukanta

NPA Ta Tarbi Babban Jirgin ‘Ruwa MB Ocean Dragon’ Don Bunkasa Ayyukanta

July 11, 2025
Rikicin Masarautar Kano Ya Kara Zafafa

Rikicin Masarautar Kano Ya Kara Zafafa

July 11, 2025
Yunkurin Magance Matsalar Tsaro Da Rigingimu A Arewa…

Akwai Bukatar Hada Kai Da Aiki Tare Tsakanin Hukumomin Tsaro

July 11, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.