ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 5, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Jadawalin Tsare-Tsaren Bikin Mika Mulki Daga Shugaba Buhari Zuwa Bola Tinubu

Gwamnatin Nijeriya ta fitar da tsarin bikin mika mulki na mako daya tsakanin Shugaba Buhari da shugaba mai jiran gado Bola Ahmad Tinubu.

by Muhammad
3 years ago
Buhari

Kafar yada labarai ta TRT Hausa, ta rawaito cewa, Gwamnatin Nijeriya ta fitar da jadawalin mako daya na bikin mika wa zababben shugaban kasar Bola Tinubu mulki ranar 29 ga watan Mayu don zama shugaban kasar na 16.

Sakataren Gwamnatin kasar kuma shugaban kwamitin mika mulki, Boss Mustapha, ya bayyana ranar Alhamis cewa za a yi shagali na mako daya zuwa 29 ga watan Mayu ranar da Shugaba Muhammadu Buhari zai mika mulki ga shugaba mai jiran gado Bola Tinubu.

  • Shirye-shiryen Saukar Buhari Mulki…
  • Gwamnatin Birtaniya Ta Taya Tunibu Murnar Lashe Zaben Shugaban Kasa

Da yake jawabi ga manema labarai a Abuja, babban birnin kasar Boss Mustapha ya ce ranar Talata, 23 ga watan Mayu 23, za a yi liyafa ta girmamawa ta soji ga shugaba mai barin gado, Muhammadu Buhari.

ADVERTISEMENT

Ranar 24 ga watan Mayu 24 (Laraba), za a yi taron bankwana na Majalisar Ministoci a Fadar shugaban kasa da ke Abuja.

Kazalika ranar 25 ga watan Mayu (Alhamis), za a karrama Tinubu da babban lambar yabo ta GCFR da ake bai wa shugabannin kasa kadai. Har wa yau a ranar, Buhari zai karbi lambar yabo ta GCON da ake bai wa tsofaffin shugabannin kasar. A yayin bikin, Buhari zai mika takardun mika mulki ga Tinubu.

LABARAI MASU NASABA

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

A ranar 26 ga watan Mayu (Juma’a), za a gabatar da lacca da sallar Juma’a a babban masallacin kasa da ke Abuja tsakanin karfe 10 na safe zuwa 1:30 na rana.

A ranar 27 ga watan Mayu (Asabar), Tsohon shugaban kasar Kenya, Uhuru Kenyatta, zai ba da lacca kan “hanyoyin zurfafa dimokuradiyya don cudanya da ci gaba”.

A ranar 28 ga watan Mayu (Lahadi), za a gudanar da taro na mabiya addinin Kirista a cibiyar kiristoci ta kasa da ke Abuja. A yammacin ranar, Shugaba Buhari zai karbi bakuncin baki da suka zo don a yi liyafar cin abincin dare a dakin taro na fadar gwamnati.

A ranar 29 ga Mayu (Litinin), Tinubu zai yi rantsuwar kama aiki a dandalin Eagle Square da ke Abuja da misalin karfe 10 na safe agogon kasar. Haka kuma za a gudanar da faretin kaddamarwa.

Sannan kuma za a gudanar da liyafar cin abincin rana bayan rantsar da shi a dakin taro na Banquet House da misalin karfe 1:30 na rana. Tinubu ne ya shirya liyafar, kuma ana sa ran shugabannin kasashen da aka gayyato da shugabannin gwamnati da manyan baki ne kawai za su halarci taron.

Kwamitin mika mulki ya ce an gayyaci shugabannin kasashe da na gwamnati da dama, kuma akasarinsu sun ba da tabbacin cewa za su halarci bikin mika mulkin Nijeriya ga Bola Tinubu.

Shugaban kwamitin, Boss Mustapha, ya ce ba zai iya bayyana adadin ko sunayen shugabannin da aka gayyata ba saboda “sha’ani na tsaro”.

Tinubu, wanda ya yi takara a jam’iyyar APC mai rike da mulki, ya samu kuri’u miliyan 8.8 kuma an ayyana shi a matsayin wanda ya lashe zaben shugaban kasar Nijeriya da aka gudanar a watan Fabrairun 2023.

Atiku Abubakar na jam’iyyar PDP ya zo na biyu da kuri’u miliyan 7, yayin da Peter Obi na jam’iyyar Labour ya zo na uku da kuri’u miliyan 6.1.

Atiku da Obi sun yi wasti da sakamakon zaben, kuma sun shigar da kara a gaban kotun zabe, suna kalubalantar nasarar da Tinubu ya samu.

Buhari
Muhammad
+ postsBio
  • Muhammad
    Cikin Shekaru 28, Kudiri Ƙasa Da 10 Sanatocin Zamfara Ta Arewa Suka Gabatar A Majalisa – Shinkafi
  • Muhammad
    2027: NNPP Ta Yi Wa Korarrun Mambobinta Afuwa, Ta Yi Alƙawarin Basu Tikitin Kai-tsaye
  • Muhammad
    Musulunci Na Fuskantar Barazana A Karƙashin Mulkin Tinubu — Datti Baba-Ahmed
  • Muhammad
    Kwankwaso Tamkar Tsuntsu Ne A Siyasa Da Yake Sauya Sheƙa Daga Nan Zuwa Can – Ganduje

MASU ALAKA

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi
Manyan Labarai

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City
Wasanni

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
Manyan Labarai

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Next Post
Shugabancin Majalisa Ta 10: Hannun Agogo Na Neman Koma Wa APC Baya

Shugabancin Majalisa Ta 10: Hannun Agogo Na Neman Koma Wa APC Baya

LABARAI MASU NASABA

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

June 4, 2026
Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.