• English
  • Business News
Thursday, October 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Jagoranci Nagari: Kungiyar Lauyoyi Ta Karrama Gwamnan Zamfara Da Lambar Yabo

bySulaiman
9 months ago
Zamfara

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal ya jaddada cewa tabbatar da doka da oda na buƙatar ƙwarewa ta fasaha, jajircewa da kuma gaskiya da riƙon amana.

 

Gwamna Lawal ya kasance babban baƙo a wajen taron shari’a na shekara-shekara ta 2024 da Ƙungiyar Lauyoyi ta Ƙasa (NBA) reshen Gusau ta shirya.

  • Saudiyya Ta Ware Dala Biliyan 100 Don Sabunta Masallatan Harami
  • Sin Da AU Sun Cimma Nasarori A Fannonin Diflomasiyya Da Tattalin Arziki

A wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan, Sulaiman Bala Idris, ya fitar, ta bayyana cewa a yayin taron, gwamna Lawal ya samu lambar yabo ta karramawa a matsayin babban abin tunawa kuma mutum mai tasiri ga al’ummar jihar Zamfara.

 

LABARAI MASU NASABA

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

Ya ƙara da cewa, shugaban NBA reshen Gusau Mu’azu Shehu Ahmad Esq ne ya ba gwamnan lambar yabon.

 

A nasa jawabin, Gwamna Lawal ya sake nanata cewa taro kamar na NBA yana ƙara ƙwarin gwiwa ga ƙwararrun lauya don musayar ra’ayoyi da inganta samar da adalci, dimokuraɗiyya, da bin doka.

 

Ya ce, “Taken taron na bana shi ne; “Tabbatar da Doka: Ginshiƙin Ci gaban Dimokraɗiyya”. Yana nuna da irin rawar da fannin shari’a ke takawa wajen tsara al’ummarmu ta hanyar tabbatar da kyawawan ɗabi’u, adalci da riƙon amana.

 

“Ina da yaƙinin cewa za mu iya ƙarfafa ginshiƙin dimokuraɗiyyar mu da kuma ginshiƙin wanzuwar mu a matsayin al’umma ta hanyar sadaukar da kai ga bin doka da oda.

 

“A halin da ake ciki, ina yaba wa Ƙungiyar Lauyoyin Nijeriya reshen Gusau, bisa namijin ƙoƙarin da suke yi na tabbatar da adalci da bin doka da oda. Haƙiƙa sadaukarwar da kuka yi ga wannan aiki mai daraja abin a yaba ne kuma abin koyi ne.

 

“Ina kira gare ku da ku ci gaba da nuan halin ƙwarai na ma’aikatan shari’a don tabbatar da cewa kun kasance ginshiƙin fata ga talakawa da duk masu neman adalci.

 

“Na yaba wa ƙoƙarin lauyoyi wajen ganin an yi adalci ba tare da nuna son kai ba cikin gaggawa, har a lokutan da ake fuskantar ƙalubale. Tsayuwarku ta kasance ƙwarin gwiwa kuma ta zama abin tunatarwa cewa adalci shi ne ginshiƙin kowace al’umma mai wayewa.

 

“Gwamnatin jihar Zamfara ta tsaya tsayin daka wajen dawo da zaman lafiya da kwanciyar hankali. Muna aiki tuƙuru don magance matsalolin rashin tsaro da samar da yanayin da al’ummarmu za su zauna ba tare da tsoro ba.

 

“Ina kuma so in jaddada muhimmancin ilimin shari’a wajen ƙarfafa tsarin adalcinmu.

 

“Tsarin ilimin shari’a yana buƙatar karatu da haƙiƙa. Ina roƙon ku da ku riƙa amfanar juna wajen da horo da ilimin da ku ka samu, kamar wannan taro na makon shari’a, don kasancewa a sahun gaba wajen aiki da doka.

 

“A wannan lokaci, ina miƙa godiya ta ga waɗanda suka shirya wannan babbar lambar yabo a gare ni. Jajircewar da na yi na yaƙar rashin tsaro, da bin doka da oda, da gina ababen more rayuwa abin a yaba ne matuƙa.

 

“Ba abin alfahari ba ne kawai, a’a, shaida ce ga namijin ƙoƙarin da duk waɗanda suka yi aiki tare da ni suka yi wajen gina jihar Zamfara mai tsaro, da adalci, da wadata cikin watanni 20 da suka gabata.

 

“A ƙarshe, yayin da nake yaba wa Ƙungiyar Lauyoyi ta Nijeriya reshen Gusau, kan yadda suka saba shirya wannan taron na shekara-shekara, cikin alfahari nake bayyana buɗe makon taron shari’a na 2024. Ina addu’ar shawarwarinku su kasance masu ma’ana da tasiri. Allah Ta’ala Ya yi mana jagora a cikin ayyukanmu baki ɗaya”.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace
Labarai

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Tinubu
Manyan Labarai

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa
Labarai

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Next Post
Sabon Albishir Ga Masu Kawo Ziyara Ko Yada Zango A Birnin Beijing Na Kasar Sin

Sabon Albishir Ga Masu Kawo Ziyara Ko Yada Zango A Birnin Beijing Na Kasar Sin

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

October 8, 2025
Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

October 8, 2025
Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

October 8, 2025
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

October 8, 2025
Tinubu

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

October 8, 2025
Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

October 8, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Go to mobile version