• English
  • Business News
Monday, July 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Jami’an Tsaro Sun Hallaka ‘Yan Fashin Daji 67, Sun Ceto Mutum 29 A Bauchi

by Khalid Idris Doya
2 years ago
in Labarai
0
Jami’an Tsaro Sun Hallaka ‘Yan Fashin Daji 67, Sun Ceto Mutum 29 A Bauchi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Jami’an tsaron hadin guiwar sojoji, ‘yansanda, mafarauta da ‘yan banga sun samu nasarar ceto mutane 29 daga hannun masu garkuwa da mutane a gundumar Lere da ke karamar hukumar Tafawa Balewa a jihar Bauchi kwanakin baya. 

Gwamnan jihar Bauchi, Bala Muhammad, shi ne ya sanar da hakan dangane da nasarori da ayyukan jami’an tsaro a gundumar Lere ranar Litinin yayin wata ziyarar mara baya da ya kai wa jami’an tsaron, ya kara da cewa, ‘yan fashin daji su 67 ne suka sheka lahira sakamakon tunkararsu da jami’an tsaro a karkashin ‘yansandan jihar suka yi.

  • An Kama Masu Laifi 537, An Daure 250 Cikin Wata 3 A Borno
  • Gwamnatin Tarayya Za Ta Dauki Matasa Miliyan 5 Aiki A Sabon Shirin N-Power – Minista

Domin bayar da dama wajen saukaka ayyukan fatattakar masu garkuwa da mutane, gwamnan ya gargadi dukkanin wani basaraken da aka samu da mara baya ko sako-sako wa ‘yan fashin daji a masarautarsa to lallai za a dauki matakin ladabtarwa a kansa.

A cewarsa, sarakunan da suke mara baya wa masu garkuwa da mutane suna da hadari matuka a cikin al’umma fiye ma da ‘yan bindigan.

Gwamna Bala ya sanar da shirin gwamnatin jihar na daukan jami’an tsaron sa-kai na cikin gida su sama da 20,000 wadanda za su samu horo na musamman daga wajen hukumomin tsaro domin kara karfi wajen yaki da masu garkuwa da mutane da sauran matsalolin tsaro a fadin jihar Bauchi.

Labarai Masu Nasaba

Na Yi Rashin Nagartaccen Abokin Aiki, Mai Dattako, Shugaba Buhari —Jonathan

Rasuwar Buhari Babbar Asara Ce Ga Nijeriya — Obasanjo

Abdulkadir Muhammad ya nuna muhimmancin aikin hadin guiwa a tsakanin ‘yan banga, mafarauta, sarakuna da hukumomin tsaro wajen yaki da ‘yan ta’adda da ayyukan ta’addancin a fadin jihar.

A wani mataki na qarfafa guiwar jami’an tsaron sa-kai, gwamnan ya bayar da kyautar naira miliyan goma (10m) wa farauta da ‘yan banga su 200 da suka shiga aka dama da su wajen ceto mutanen da aka yi garkuwa da su.

Bugu da kari, ya kuma bayar da kyautar Babura kirar Bajaj domin karfafa musu guiwa wajen cigaba da ayyukan yaki da bata-gari, ya ce za su kara samar musu da mashinan sintiri kwanan nan.

Daga nan sai gwamnan ya yaba wa kokarin hadakar jami’an tsaron wajen cimma wannan nasarar da ma sauran nasarorin da suke samu a kan ‘yan fashin daji, ya ba su tabbacin cigaba da mara musu baya da tallafa musu da kayan aiki da kudade domin samun nasara wajen kare rayuka da dukiyar al’umman jihar.

Tun da farko, kwamishinan ‘yansandan jihar Bauchi, CP Musa Muhammed Auwal, ya nuna farin cikinsa bisa yadda ake samun aikin hadin guiwa a tsakanin hukumomin tsaron wajen yaki da matsalolin tsaro a fadin jihar.

Ya bada tabbacin hadin guiwarsu ga gwamnatin jihar da masu ruwa da tsaki hadi da al’umman jihar domin cigaba da kyautata harkokin zaman lafiya da kwanciyar hankalin al’umman jihar baki daya.

Shugaban riko na karamar hukumar Tafawa Balewa da Hakimin Lere Sama’ila Wakili da Suleiman Mohammed bi da bi sun jinjina wa gwamna Bala bisa damuwa da yake yi kan kan tsaro da tabbatar da kare rayuka da dukiyar al’umman jihar baki daya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Hazard Ya Yi Ritaya Daga Kwallon Kafa

Next Post

Dan Kwallon Nijeriya Na Cikin Hazikan ‘Yan Wasan Bundesliga Na Watan Satumba

Related

Na Yi Rashin Nagartaccen Abokin Aiki, Mai Dattako, Shugaba Buhari —Jonathan
Labarai

Na Yi Rashin Nagartaccen Abokin Aiki, Mai Dattako, Shugaba Buhari —Jonathan

6 hours ago
Rasuwar Buhari Babbar Asara Ce Ga Nijeriya — Obasanjo
Labarai

Rasuwar Buhari Babbar Asara Ce Ga Nijeriya — Obasanjo

6 hours ago
Kakakin Majalisar Wakilai, Abbas, Ya Yi Jimamin Raasuwar Buhari, Ya Ce Mutuwa Ce Da Ta Girgiza Shi
Labarai

Buhari Ɗan Kishin Ƙasa Ne — Tinubu

7 hours ago
Na Yi Rashin Nagartaccen Abokin Aiki, Mai Dattako, Shugaba Buhari —Jonathan
Labarai

Nijeriya Ta Yi Rashin Ɗan Kishin Ƙasa Mai Gaskiya Da Nagarta — Osinbajo

7 hours ago
Kakakin Majalisar Wakilai, Abbas, Ya Yi Jimamin Raasuwar Buhari, Ya Ce Mutuwa Ce Da Ta Girgiza Shi
Labarai

Kakakin Majalisar Wakilai, Abbas, Ya Yi Jimamin Raasuwar Buhari, Ya Ce Mutuwa Ce Da Ta Girgiza Shi

7 hours ago
Tsohon Shugaban Nijeriya Muhammadu Buhari Ya Rasu A Landan
Labarai

Rasuwar Buhari: Nahiyar Afirka Ta Yi Babban Rashi — Kungiyar Gwamnoni Ta Nijeriya 

8 hours ago
Next Post
Dan Kwallon Nijeriya Na Cikin Hazikan ‘Yan Wasan Bundesliga Na Watan Satumba

Dan Kwallon Nijeriya Na Cikin Hazikan 'Yan Wasan Bundesliga Na Watan Satumba

LABARAI MASU NASABA

Na Yi Rashin Nagartaccen Abokin Aiki, Mai Dattako, Shugaba Buhari —Jonathan

Na Yi Rashin Nagartaccen Abokin Aiki, Mai Dattako, Shugaba Buhari —Jonathan

July 13, 2025
Rasuwar Buhari Babbar Asara Ce Ga Nijeriya — Obasanjo

Rasuwar Buhari Babbar Asara Ce Ga Nijeriya — Obasanjo

July 13, 2025
Kakakin Majalisar Wakilai, Abbas, Ya Yi Jimamin Raasuwar Buhari, Ya Ce Mutuwa Ce Da Ta Girgiza Shi

Buhari Ɗan Kishin Ƙasa Ne — Tinubu

July 13, 2025
Na Yi Rashin Nagartaccen Abokin Aiki, Mai Dattako, Shugaba Buhari —Jonathan

Nijeriya Ta Yi Rashin Ɗan Kishin Ƙasa Mai Gaskiya Da Nagarta — Osinbajo

July 13, 2025
Kakakin Majalisar Wakilai, Abbas, Ya Yi Jimamin Raasuwar Buhari, Ya Ce Mutuwa Ce Da Ta Girgiza Shi

Kakakin Majalisar Wakilai, Abbas, Ya Yi Jimamin Raasuwar Buhari, Ya Ce Mutuwa Ce Da Ta Girgiza Shi

July 13, 2025
Tsohon Shugaban Nijeriya Muhammadu Buhari Ya Rasu A Landan

Rasuwar Buhari: Nahiyar Afirka Ta Yi Babban Rashi — Kungiyar Gwamnoni Ta Nijeriya 

July 13, 2025
Rasuwar Buhari: An Yi Rashin Ɗan Ƙasa Na Gari, Abin Koyi — Kungiyar Gwamnonin Arewa

Rasuwar Buhari: An Yi Rashin Ɗan Ƙasa Na Gari, Abin Koyi — Kungiyar Gwamnonin Arewa

July 13, 2025
Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa Barau Jibril Ya Yi Alhinin Rasuwar Buhari

Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa Barau Jibril Ya Yi Alhinin Rasuwar Buhari

July 13, 2025
Afirka Ta Kudu Na Fatan Karfafa Alakar Cinikayya Tare Da Sin Ta Hanyar Halartar Baje Kolin CISCE

Afirka Ta Kudu Na Fatan Karfafa Alakar Cinikayya Tare Da Sin Ta Hanyar Halartar Baje Kolin CISCE

July 13, 2025
Ko Yanzu Tinubu Ya Yi Rawar Gani, Kuma Yana Ƙoƙari Sosai – Buhari

Muhimman Abubuwa 10 Da Kowa Zai So Ya Sani Game Da Marigayi Shugaban Ƙasa Buhari

July 13, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.