• English
  • Business News
Friday, November 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Jami’an Tsaro Sun Hallaka ‘Yan Fashin Daji 67, Sun Ceto Mutum 29 A Bauchi

by Khalid Idris Doya
2 years ago
Bauchi

Jami’an tsaron hadin guiwar sojoji, ‘yansanda, mafarauta da ‘yan banga sun samu nasarar ceto mutane 29 daga hannun masu garkuwa da mutane a gundumar Lere da ke karamar hukumar Tafawa Balewa a jihar Bauchi kwanakin baya. 

Gwamnan jihar Bauchi, Bala Muhammad, shi ne ya sanar da hakan dangane da nasarori da ayyukan jami’an tsaro a gundumar Lere ranar Litinin yayin wata ziyarar mara baya da ya kai wa jami’an tsaron, ya kara da cewa, ‘yan fashin daji su 67 ne suka sheka lahira sakamakon tunkararsu da jami’an tsaro a karkashin ‘yansandan jihar suka yi.

  • An Kama Masu Laifi 537, An Daure 250 Cikin Wata 3 A Borno
  • Gwamnatin Tarayya Za Ta Dauki Matasa Miliyan 5 Aiki A Sabon Shirin N-Power – Minista

Domin bayar da dama wajen saukaka ayyukan fatattakar masu garkuwa da mutane, gwamnan ya gargadi dukkanin wani basaraken da aka samu da mara baya ko sako-sako wa ‘yan fashin daji a masarautarsa to lallai za a dauki matakin ladabtarwa a kansa.

A cewarsa, sarakunan da suke mara baya wa masu garkuwa da mutane suna da hadari matuka a cikin al’umma fiye ma da ‘yan bindigan.

Gwamna Bala ya sanar da shirin gwamnatin jihar na daukan jami’an tsaron sa-kai na cikin gida su sama da 20,000 wadanda za su samu horo na musamman daga wajen hukumomin tsaro domin kara karfi wajen yaki da masu garkuwa da mutane da sauran matsalolin tsaro a fadin jihar Bauchi.

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Amince da Gina Sabbin Gidaje Ga Alƙalai, Da Samar Da Ruwa A  FCT

Amurka Ta Yi Barazanar Ƙwace Kadarorin Ƙungiyoyin Makiyaya A Nijeriya 

Abdulkadir Muhammad ya nuna muhimmancin aikin hadin guiwa a tsakanin ‘yan banga, mafarauta, sarakuna da hukumomin tsaro wajen yaki da ‘yan ta’adda da ayyukan ta’addancin a fadin jihar.

A wani mataki na qarfafa guiwar jami’an tsaron sa-kai, gwamnan ya bayar da kyautar naira miliyan goma (10m) wa farauta da ‘yan banga su 200 da suka shiga aka dama da su wajen ceto mutanen da aka yi garkuwa da su.

Bugu da kari, ya kuma bayar da kyautar Babura kirar Bajaj domin karfafa musu guiwa wajen cigaba da ayyukan yaki da bata-gari, ya ce za su kara samar musu da mashinan sintiri kwanan nan.

Daga nan sai gwamnan ya yaba wa kokarin hadakar jami’an tsaron wajen cimma wannan nasarar da ma sauran nasarorin da suke samu a kan ‘yan fashin daji, ya ba su tabbacin cigaba da mara musu baya da tallafa musu da kayan aiki da kudade domin samun nasara wajen kare rayuka da dukiyar al’umman jihar.

Tun da farko, kwamishinan ‘yansandan jihar Bauchi, CP Musa Muhammed Auwal, ya nuna farin cikinsa bisa yadda ake samun aikin hadin guiwa a tsakanin hukumomin tsaron wajen yaki da matsalolin tsaro a fadin jihar.

Ya bada tabbacin hadin guiwarsu ga gwamnatin jihar da masu ruwa da tsaki hadi da al’umman jihar domin cigaba da kyautata harkokin zaman lafiya da kwanciyar hankalin al’umman jihar baki daya.

Shugaban riko na karamar hukumar Tafawa Balewa da Hakimin Lere Sama’ila Wakili da Suleiman Mohammed bi da bi sun jinjina wa gwamna Bala bisa damuwa da yake yi kan kan tsaro da tabbatar da kare rayuka da dukiyar al’umman jihar baki daya.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Gwamnatin Tarayya Ta Amince da Gina Sabbin Gidaje Ga Alƙalai, Da Samar Da Ruwa A  FCT
Manyan Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Amince da Gina Sabbin Gidaje Ga Alƙalai, Da Samar Da Ruwa A  FCT

November 6, 2025
Amurka Ta Yi Barazanar Ƙwace Kadarorin Ƙungiyoyin Makiyaya A Nijeriya 
Manyan Labarai

Amurka Ta Yi Barazanar Ƙwace Kadarorin Ƙungiyoyin Makiyaya A Nijeriya 

November 6, 2025
Gwamnatin tarayya
Labarai

Ta’addanci Ba Zai Yi Nasara Ba A Ƙasarmu — Tinubu

November 6, 2025
Next Post
Dan Kwallon Nijeriya Na Cikin Hazikan ‘Yan Wasan Bundesliga Na Watan Satumba

Dan Kwallon Nijeriya Na Cikin Hazikan 'Yan Wasan Bundesliga Na Watan Satumba

LABARAI MASU NASABA

An Yi Taron Kaddamar Da Tsarin Kawancen Kafafen Watsa Labarun Kasashe Masu Tasowa Da Dandalin Yada Labarai Na Bidiyo Karo Na 13 A Xi’an

An Yi Taron Kaddamar Da Tsarin Kawancen Kafafen Watsa Labarun Kasashe Masu Tasowa Da Dandalin Yada Labarai Na Bidiyo Karo Na 13 A Xi’an

November 6, 2025
CMG Ya Kaddamar Da Wasu Tashoshin Talabijin Uku A Dandalin FAST

CMG Ya Kaddamar Da Wasu Tashoshin Talabijin Uku A Dandalin FAST

November 6, 2025
Baje Kolin CIIE Ya Bayar Da Tabbaci Ga Duniya

Baje Kolin CIIE Ya Bayar Da Tabbaci Ga Duniya

November 6, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Amince da Gina Sabbin Gidaje Ga Alƙalai, Da Samar Da Ruwa A  FCT

Gwamnatin Tarayya Ta Amince da Gina Sabbin Gidaje Ga Alƙalai, Da Samar Da Ruwa A  FCT

November 6, 2025
Manufofin Sin Na Yaki Da Sauyin Yanayi: Gani Ya Kori Ji

Manufofin Sin Na Yaki Da Sauyin Yanayi: Gani Ya Kori Ji

November 6, 2025
Shugaba Xi Ya Jaddada Bukatar Gina Ingantaccen Yankin Ciniki Cikin ’Yanci Na Tashar Ruwa Ta Hainan

Shugaba Xi Ya Jaddada Bukatar Gina Ingantaccen Yankin Ciniki Cikin ’Yanci Na Tashar Ruwa Ta Hainan

November 6, 2025
Amurka Ta Yi Barazanar Ƙwace Kadarorin Ƙungiyoyin Makiyaya A Nijeriya 

Amurka Ta Yi Barazanar Ƙwace Kadarorin Ƙungiyoyin Makiyaya A Nijeriya 

November 6, 2025
A Karon Farko An Gabatar Da Ka’idar Kasa Da Kasa Ta Fasahar 5G Mai Amfani Ga Masana’antu

A Karon Farko An Gabatar Da Ka’idar Kasa Da Kasa Ta Fasahar 5G Mai Amfani Ga Masana’antu

November 6, 2025
Gwamnatin tarayya

Ta’addanci Ba Zai Yi Nasara Ba A Ƙasarmu — Tinubu

November 6, 2025
Bikin Baje Kolin CIIE: Da Abokin Daka Ake Shan Gari

Bikin Baje Kolin CIIE: Da Abokin Daka Ake Shan Gari

November 6, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.