ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, July 17, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Jami’an Tsaro Sun Hallaka ‘Yan Fashin Daji 67, Sun Ceto Mutum 29 A Bauchi

by Khalid Idris Doya
3 years ago
Bauchi

Jami’an tsaron hadin guiwar sojoji, ‘yansanda, mafarauta da ‘yan banga sun samu nasarar ceto mutane 29 daga hannun masu garkuwa da mutane a gundumar Lere da ke karamar hukumar Tafawa Balewa a jihar Bauchi kwanakin baya. 

Gwamnan jihar Bauchi, Bala Muhammad, shi ne ya sanar da hakan dangane da nasarori da ayyukan jami’an tsaro a gundumar Lere ranar Litinin yayin wata ziyarar mara baya da ya kai wa jami’an tsaron, ya kara da cewa, ‘yan fashin daji su 67 ne suka sheka lahira sakamakon tunkararsu da jami’an tsaro a karkashin ‘yansandan jihar suka yi.

  • An Kama Masu Laifi 537, An Daure 250 Cikin Wata 3 A Borno
  • Gwamnatin Tarayya Za Ta Dauki Matasa Miliyan 5 Aiki A Sabon Shirin N-Power – Minista

Domin bayar da dama wajen saukaka ayyukan fatattakar masu garkuwa da mutane, gwamnan ya gargadi dukkanin wani basaraken da aka samu da mara baya ko sako-sako wa ‘yan fashin daji a masarautarsa to lallai za a dauki matakin ladabtarwa a kansa.

ADVERTISEMENT

A cewarsa, sarakunan da suke mara baya wa masu garkuwa da mutane suna da hadari matuka a cikin al’umma fiye ma da ‘yan bindigan.

Gwamna Bala ya sanar da shirin gwamnatin jihar na daukan jami’an tsaron sa-kai na cikin gida su sama da 20,000 wadanda za su samu horo na musamman daga wajen hukumomin tsaro domin kara karfi wajen yaki da masu garkuwa da mutane da sauran matsalolin tsaro a fadin jihar Bauchi.

LABARAI MASU NASABA

Zaben Fidda Gwani Da Ake Takaddama:APC Ta Dauki Matakan Kauce Wa Shari’o’in Kotu

Sake Daukar Shettima Da Tinubu Ya Yi Zai Kara Karfafa APC A Zaben 2027 –Farfesa Yerima

Abdulkadir Muhammad ya nuna muhimmancin aikin hadin guiwa a tsakanin ‘yan banga, mafarauta, sarakuna da hukumomin tsaro wajen yaki da ‘yan ta’adda da ayyukan ta’addancin a fadin jihar.

A wani mataki na qarfafa guiwar jami’an tsaron sa-kai, gwamnan ya bayar da kyautar naira miliyan goma (10m) wa farauta da ‘yan banga su 200 da suka shiga aka dama da su wajen ceto mutanen da aka yi garkuwa da su.

Bugu da kari, ya kuma bayar da kyautar Babura kirar Bajaj domin karfafa musu guiwa wajen cigaba da ayyukan yaki da bata-gari, ya ce za su kara samar musu da mashinan sintiri kwanan nan.

Daga nan sai gwamnan ya yaba wa kokarin hadakar jami’an tsaron wajen cimma wannan nasarar da ma sauran nasarorin da suke samu a kan ‘yan fashin daji, ya ba su tabbacin cigaba da mara musu baya da tallafa musu da kayan aiki da kudade domin samun nasara wajen kare rayuka da dukiyar al’umman jihar.

Tun da farko, kwamishinan ‘yansandan jihar Bauchi, CP Musa Muhammed Auwal, ya nuna farin cikinsa bisa yadda ake samun aikin hadin guiwa a tsakanin hukumomin tsaron wajen yaki da matsalolin tsaro a fadin jihar.

Ya bada tabbacin hadin guiwarsu ga gwamnatin jihar da masu ruwa da tsaki hadi da al’umman jihar domin cigaba da kyautata harkokin zaman lafiya da kwanciyar hankalin al’umman jihar baki daya.

Shugaban riko na karamar hukumar Tafawa Balewa da Hakimin Lere Sama’ila Wakili da Suleiman Mohammed bi da bi sun jinjina wa gwamna Bala bisa damuwa da yake yi kan kan tsaro da tabbatar da kare rayuka da dukiyar al’umman jihar baki daya.

Bauchi
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Gwamna Bala Ya Rushe Kwamitin Gudanarwar Wikki Tourists Bayan Rashin Nasararta A Gasar NPFL
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    M.A. Abubakar Ya Zaɓi Farouk Mustapha A Matsayin Mataimakinsa
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    ATBU Ta Janye Filin Ginin Masallaci Da Ta Bai wa TIMSAN, Ta Amince Kowa Ya Yi Addininsa Yadda Ya Fahimta
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ɗan Majalisar Dokokin Bauchi, Hon. Wanzam, Ya Rasu

MASU ALAKA

Zaben Fidda Gwani Da Ake Takaddama:APC Ta Dauki Matakan Kauce Wa Shari’o’in Kotu
Rahotonni

Zaben Fidda Gwani Da Ake Takaddama:APC Ta Dauki Matakan Kauce Wa Shari’o’in Kotu

July 17, 2026
Sake Daukar Shettima Da Tinubu Ya Yi Zai Kara Karfafa APC A Zaben 2027 –Farfesa Yerima
Labarai

Sake Daukar Shettima Da Tinubu Ya Yi Zai Kara Karfafa APC A Zaben 2027 –Farfesa Yerima

July 17, 2026
Gasar Kofin Duniya: Da Ƙarfinmu Muka Kawo Matakin Da Muke Yanzu – Messi
Manyan Labarai

Gasar Kofin Duniya: Da Ƙarfinmu Muka Kawo Matakin Da Muke Yanzu – Messi

July 17, 2026
Next Post
Dan Kwallon Nijeriya Na Cikin Hazikan ‘Yan Wasan Bundesliga Na Watan Satumba

Dan Kwallon Nijeriya Na Cikin Hazikan 'Yan Wasan Bundesliga Na Watan Satumba

LABARAI MASU NASABA

Zaben Fidda Gwani Da Ake Takaddama:APC Ta Dauki Matakan Kauce Wa Shari’o’in Kotu

Zaben Fidda Gwani Da Ake Takaddama:APC Ta Dauki Matakan Kauce Wa Shari’o’in Kotu

July 17, 2026
Sin Ta Mika Sabuwar Manhajar Gargadin Gaggawa Ta MAZU Ga Djibouti

Sin Ta Mika Sabuwar Manhajar Gargadin Gaggawa Ta MAZU Ga Djibouti

July 17, 2026
Sake Daukar Shettima Da Tinubu Ya Yi Zai Kara Karfafa APC A Zaben 2027 –Farfesa Yerima

Sake Daukar Shettima Da Tinubu Ya Yi Zai Kara Karfafa APC A Zaben 2027 –Farfesa Yerima

July 17, 2026
Kwamitin Ba Da Shawara Kan Hadin Gwiwar Kasa Da Kasa Na Dandalin BRI Ya Yi Taronsa Na 2026

Kwamitin Ba Da Shawara Kan Hadin Gwiwar Kasa Da Kasa Na Dandalin BRI Ya Yi Taronsa Na 2026

July 17, 2026
Wang Huning Ya Ziyarci Koriya Ta Arewa

Wang Huning Ya Ziyarci Koriya Ta Arewa

July 17, 2026
Yawan Mu’amalar Kudi Tsakanin Mazauna Sin Da ’Yan Kasashen Waje Ya Hau Wani Sabon Matsayi A Tarihi

Yawan Mu’amalar Kudi Tsakanin Mazauna Sin Da ’Yan Kasashen Waje Ya Hau Wani Sabon Matsayi A Tarihi

July 17, 2026
Gasar Kofin Duniya: Da Ƙarfinmu Muka Kawo Matakin Da Muke Yanzu – Messi

Gasar Kofin Duniya: Da Ƙarfinmu Muka Kawo Matakin Da Muke Yanzu – Messi

July 17, 2026
Matatar Man Dangote Ta Dawo Sayar Da Fetur A Dala

Matatar Man Dangote Ta Dawo Sayar Da Fetur A Dala

July 17, 2026
Xi Jinping Ya Halarci Bikin Bude Babban Taron AI Na Duniya Na 2026 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Xi Jinping Ya Halarci Bikin Bude Babban Taron AI Na Duniya Na 2026 Tare Da Gabatar Da Jawabi

July 17, 2026
Falalar Salatut Tasbihi

Falalar Salatut Tasbihi

July 17, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.