ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Jami’an Tsaro Sun Hallaka ‘Yan Fashin Daji 67, Sun Ceto Mutum 29 A Bauchi

by Khalid Idris Doya
3 years ago
Bauchi

Jami’an tsaron hadin guiwar sojoji, ‘yansanda, mafarauta da ‘yan banga sun samu nasarar ceto mutane 29 daga hannun masu garkuwa da mutane a gundumar Lere da ke karamar hukumar Tafawa Balewa a jihar Bauchi kwanakin baya. 

Gwamnan jihar Bauchi, Bala Muhammad, shi ne ya sanar da hakan dangane da nasarori da ayyukan jami’an tsaro a gundumar Lere ranar Litinin yayin wata ziyarar mara baya da ya kai wa jami’an tsaron, ya kara da cewa, ‘yan fashin daji su 67 ne suka sheka lahira sakamakon tunkararsu da jami’an tsaro a karkashin ‘yansandan jihar suka yi.

  • An Kama Masu Laifi 537, An Daure 250 Cikin Wata 3 A Borno
  • Gwamnatin Tarayya Za Ta Dauki Matasa Miliyan 5 Aiki A Sabon Shirin N-Power – Minista

Domin bayar da dama wajen saukaka ayyukan fatattakar masu garkuwa da mutane, gwamnan ya gargadi dukkanin wani basaraken da aka samu da mara baya ko sako-sako wa ‘yan fashin daji a masarautarsa to lallai za a dauki matakin ladabtarwa a kansa.

ADVERTISEMENT

A cewarsa, sarakunan da suke mara baya wa masu garkuwa da mutane suna da hadari matuka a cikin al’umma fiye ma da ‘yan bindigan.

Gwamna Bala ya sanar da shirin gwamnatin jihar na daukan jami’an tsaron sa-kai na cikin gida su sama da 20,000 wadanda za su samu horo na musamman daga wajen hukumomin tsaro domin kara karfi wajen yaki da masu garkuwa da mutane da sauran matsalolin tsaro a fadin jihar Bauchi.

LABARAI MASU NASABA

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

Abdulkadir Muhammad ya nuna muhimmancin aikin hadin guiwa a tsakanin ‘yan banga, mafarauta, sarakuna da hukumomin tsaro wajen yaki da ‘yan ta’adda da ayyukan ta’addancin a fadin jihar.

A wani mataki na qarfafa guiwar jami’an tsaron sa-kai, gwamnan ya bayar da kyautar naira miliyan goma (10m) wa farauta da ‘yan banga su 200 da suka shiga aka dama da su wajen ceto mutanen da aka yi garkuwa da su.

Bugu da kari, ya kuma bayar da kyautar Babura kirar Bajaj domin karfafa musu guiwa wajen cigaba da ayyukan yaki da bata-gari, ya ce za su kara samar musu da mashinan sintiri kwanan nan.

Daga nan sai gwamnan ya yaba wa kokarin hadakar jami’an tsaron wajen cimma wannan nasarar da ma sauran nasarorin da suke samu a kan ‘yan fashin daji, ya ba su tabbacin cigaba da mara musu baya da tallafa musu da kayan aiki da kudade domin samun nasara wajen kare rayuka da dukiyar al’umman jihar.

Tun da farko, kwamishinan ‘yansandan jihar Bauchi, CP Musa Muhammed Auwal, ya nuna farin cikinsa bisa yadda ake samun aikin hadin guiwa a tsakanin hukumomin tsaron wajen yaki da matsalolin tsaro a fadin jihar.

Ya bada tabbacin hadin guiwarsu ga gwamnatin jihar da masu ruwa da tsaki hadi da al’umman jihar domin cigaba da kyautata harkokin zaman lafiya da kwanciyar hankalin al’umman jihar baki daya.

Shugaban riko na karamar hukumar Tafawa Balewa da Hakimin Lere Sama’ila Wakili da Suleiman Mohammed bi da bi sun jinjina wa gwamna Bala bisa damuwa da yake yi kan kan tsaro da tabbatar da kare rayuka da dukiyar al’umman jihar baki daya.

Bauchi
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Zaɓen Fidda Gwani Na Gwamna: Ba Za Mu Lamunci Kaƙaba Mana Ɗan Takara A Bauchi Ba – Mambobin APC
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Sanata Buba Ya Janye Daga Takarar Fidda Gwani Ta Gwamnan APC A Bauchi, Ya Zargi Cewa ‘Ɗauki Ɗaura Ake Yi Ba Zaɓe Ba”
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Shugaban Kwamitin Yaɗa Labarai Na Aikin Hajjin Bana Na Bauchi Ya Rasu A Saudiyya
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Na Bar Harƙoƙin Siyasa Gaba Ɗaya – Ɗan Takarar Gwamnan Bauchi, Air Marshal Saddique Baba

MASU ALAKA

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City
Wasanni

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed
Labarai

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada
Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Next Post
Dan Kwallon Nijeriya Na Cikin Hazikan ‘Yan Wasan Bundesliga Na Watan Satumba

Dan Kwallon Nijeriya Na Cikin Hazikan 'Yan Wasan Bundesliga Na Watan Satumba

LABARAI MASU NASABA

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

June 4, 2026
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.