ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Tarayya Za Ta Dauki Matasa Miliyan 5 Aiki A Sabon Shirin N-Power – Minista

by Sadiq
3 years ago
N-Power

Gwamnatin tarayya ta bayyana cewa shirin N-Power da aka sauya wa fasalin zai samar da ayyukan yi akalla miliyan biyar ga matasa a kasar nan.

A cewar ministar harkokin jin-kai da yaki da fatara, Betta Edu, wadda ta bayyana hakan a gidan talabijin na Channels, ta ce shirin N-Power wani bangare ne na samar da tsaro da aka tsara don hana mutane fadawa cikin talauci.

  • Sarkin Kudan Ya Taya Mai Martaba Sarkin Zazzau Murnar Cika Shekara Uku A Karaga
  • Abubuwan Al’ajabi Da Abarba Ke Yi Wajen Gyaran Fata

“Muna aiki a kan matasan Nijeriya miliyan biyar masu shekaru tsakanin 18 zuwa 40 kuma za a dauki miliyan daya a kowace shekara. A kan shirin GEEP, muna aiki kan ‘yan Nijeriya miliyan 1.5,” in ji ta.

ADVERTISEMENT

Kalaman nata ya zo ne kwanaki bayan da gwamnatin tarayya ta dakatar da shirin na N-Power, wani bangare na shirin nan na ‘National Social Investment Programme (NSIP), wanda tsohon shugaban kasa Muhammadu Buhari ya kaddamar a ranar 26 ga watan Yuni, 2016, domin yaki da matsalar rashin aikin yi da matasa ke fuskanta da kuma bunkasa zamantakewar al’umma.

Sai dai a cikin shirin da aka sauya wa fasalin, ministan ta jaddada cewa shirin N-Power zai kasance ne bisa tsarin farko-farko.

LABARAI MASU NASABA

Ba Zan Iya Jure Halayen El-Rufai Ba Shi Yasa Na Fice Daga ADC – Salihu Lukman

M.A. Abubakar Ya Zaɓi Farouk Mustapha A Matsayin Mataimakinsa

“Muddin kun cika ka’idojin kowane nau’i, za a ba ku dama. Don haka, ba lallai ne mu ware wa jihohi kaso ba,” in ji ministar.

Ta ce shirin da sauran shirye-shiryen shiga tsakani na gwamnati na da nufin yaki da talauci a kasar.

“Abin da ma’aikatarmu ke yi shi ne samar da hanyar kare lafiyar jama’a da ke hana wadannan mutane fadawa cikin talauci da kuma kokarin fitar da yawancinsu daga talauci.

“Mun tsara shirye-shirye daban-daban, shirye-shiryen kasa, wadanda ake sa ran za su magance matsalar talauci mai dimbin yawa. Tabbas muna da N-Power wanda ya kamata ya samar da ayyukan yi miliyan biyar a cikin shekaru biyar.

Ministar ya kara da cewa “Muna da wasu ayyuka da dama a kasa, dukkansu an yi niyya ne a fannoni daban-daban don yaki da talauci.”

MASU ALAKA

Gwamnatin Tarayya Na Biyan Tallafin Man Fetur A Asirce – El-Rufai
Siyasa

Ba Zan Iya Jure Halayen El-Rufai Ba Shi Yasa Na Fice Daga ADC – Salihu Lukman

July 16, 2026
M.A. Abubakar Ya Zaɓi Farouk Mustapha A Matsayin  Mataimakinsa
Manyan Labarai

M.A. Abubakar Ya Zaɓi Farouk Mustapha A Matsayin Mataimakinsa

July 16, 2026
Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa
Manyan Labarai

Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa

July 16, 2026
Next Post
An Kama Masu Laifi 537, An Daure 250 Cikin Wata 3 A Borno

An Kama Masu Laifi 537, An Daure 250 Cikin Wata 3 A Borno

LABARAI MASU NASABA

An Yi Bikin Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Kafa Kungiyar Hadin Gwiwar Fasahar AI Ta Duniya A Shanghai

An Yi Bikin Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Kafa Kungiyar Hadin Gwiwar Fasahar AI Ta Duniya A Shanghai

July 16, 2026
Gwamnatin Tarayya Na Biyan Tallafin Man Fetur A Asirce – El-Rufai

Ba Zan Iya Jure Halayen El-Rufai Ba Shi Yasa Na Fice Daga ADC – Salihu Lukman

July 16, 2026
Ra’yin Sin Da Afirka Ya Zo Daya A Fannin Fasahar AI

Ra’yin Sin Da Afirka Ya Zo Daya A Fannin Fasahar AI

July 16, 2026
Duk Da Sauye-Sauyen Tattalin Arziƙi Kashi 79% Na Ƴan Nijeriya Na Cikin Talauci – Bankin Duniya

Duk Da Sauye-Sauyen Tattalin Arziƙi Kashi 79% Na Ƴan Nijeriya Na Cikin Talauci – Bankin Duniya

July 16, 2026
M.A. Abubakar Ya Zaɓi Farouk Mustapha A Matsayin  Mataimakinsa

M.A. Abubakar Ya Zaɓi Farouk Mustapha A Matsayin Mataimakinsa

July 16, 2026
Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa

Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa

July 16, 2026
Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta

Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta

July 16, 2026
Tinubu Yana Zuba Kyawawan Ayyuka A Nijeriya – Ganduje

Ganduje Ya Buƙaci A Yi Siyasar Aƙida Domin Inganta Dimokuraɗiyya A Nijeriya

July 16, 2026
Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.