ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Tarayya Za Ta Dauki Matasa Miliyan 5 Aiki A Sabon Shirin N-Power – Minista

by Sadiq
3 years ago
N-Power

Gwamnatin tarayya ta bayyana cewa shirin N-Power da aka sauya wa fasalin zai samar da ayyukan yi akalla miliyan biyar ga matasa a kasar nan.

A cewar ministar harkokin jin-kai da yaki da fatara, Betta Edu, wadda ta bayyana hakan a gidan talabijin na Channels, ta ce shirin N-Power wani bangare ne na samar da tsaro da aka tsara don hana mutane fadawa cikin talauci.

  • Sarkin Kudan Ya Taya Mai Martaba Sarkin Zazzau Murnar Cika Shekara Uku A Karaga
  • Abubuwan Al’ajabi Da Abarba Ke Yi Wajen Gyaran Fata

“Muna aiki a kan matasan Nijeriya miliyan biyar masu shekaru tsakanin 18 zuwa 40 kuma za a dauki miliyan daya a kowace shekara. A kan shirin GEEP, muna aiki kan ‘yan Nijeriya miliyan 1.5,” in ji ta.

ADVERTISEMENT

Kalaman nata ya zo ne kwanaki bayan da gwamnatin tarayya ta dakatar da shirin na N-Power, wani bangare na shirin nan na ‘National Social Investment Programme (NSIP), wanda tsohon shugaban kasa Muhammadu Buhari ya kaddamar a ranar 26 ga watan Yuni, 2016, domin yaki da matsalar rashin aikin yi da matasa ke fuskanta da kuma bunkasa zamantakewar al’umma.

Sai dai a cikin shirin da aka sauya wa fasalin, ministan ta jaddada cewa shirin N-Power zai kasance ne bisa tsarin farko-farko.

LABARAI MASU NASABA

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

“Muddin kun cika ka’idojin kowane nau’i, za a ba ku dama. Don haka, ba lallai ne mu ware wa jihohi kaso ba,” in ji ministar.

Ta ce shirin da sauran shirye-shiryen shiga tsakani na gwamnati na da nufin yaki da talauci a kasar.

“Abin da ma’aikatarmu ke yi shi ne samar da hanyar kare lafiyar jama’a da ke hana wadannan mutane fadawa cikin talauci da kuma kokarin fitar da yawancinsu daga talauci.

“Mun tsara shirye-shirye daban-daban, shirye-shiryen kasa, wadanda ake sa ran za su magance matsalar talauci mai dimbin yawa. Tabbas muna da N-Power wanda ya kamata ya samar da ayyukan yi miliyan biyar a cikin shekaru biyar.

Ministar ya kara da cewa “Muna da wasu ayyuka da dama a kasa, dukkansu an yi niyya ne a fannoni daban-daban don yaki da talauci.”

MASU ALAKA

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City
Wasanni

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
Manyan Labarai

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro
Manyan Labarai

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Next Post
An Kama Masu Laifi 537, An Daure 250 Cikin Wata 3 A Borno

An Kama Masu Laifi 537, An Daure 250 Cikin Wata 3 A Borno

LABARAI MASU NASABA

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

June 4, 2026
Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

June 4, 2026
Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

June 4, 2026
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.