• English
  • Business News
Saturday, July 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Tarayya Za Ta Dauki Matasa Miliyan 5 Aiki A Sabon Shirin N-Power – Minista

by Sadiq
2 years ago
in Manyan Labarai
0
Gwamnatin Tarayya Za Ta Dauki Matasa Miliyan 5 Aiki A Sabon Shirin N-Power – Minista
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnatin tarayya ta bayyana cewa shirin N-Power da aka sauya wa fasalin zai samar da ayyukan yi akalla miliyan biyar ga matasa a kasar nan.

A cewar ministar harkokin jin-kai da yaki da fatara, Betta Edu, wadda ta bayyana hakan a gidan talabijin na Channels, ta ce shirin N-Power wani bangare ne na samar da tsaro da aka tsara don hana mutane fadawa cikin talauci.

  • Sarkin Kudan Ya Taya Mai Martaba Sarkin Zazzau Murnar Cika Shekara Uku A Karaga
  • Abubuwan Al’ajabi Da Abarba Ke Yi Wajen Gyaran Fata

“Muna aiki a kan matasan Nijeriya miliyan biyar masu shekaru tsakanin 18 zuwa 40 kuma za a dauki miliyan daya a kowace shekara. A kan shirin GEEP, muna aiki kan ‘yan Nijeriya miliyan 1.5,” in ji ta.

Kalaman nata ya zo ne kwanaki bayan da gwamnatin tarayya ta dakatar da shirin na N-Power, wani bangare na shirin nan na ‘National Social Investment Programme (NSIP), wanda tsohon shugaban kasa Muhammadu Buhari ya kaddamar a ranar 26 ga watan Yuni, 2016, domin yaki da matsalar rashin aikin yi da matasa ke fuskanta da kuma bunkasa zamantakewar al’umma.

Sai dai a cikin shirin da aka sauya wa fasalin, ministan ta jaddada cewa shirin N-Power zai kasance ne bisa tsarin farko-farko.

Labarai Masu Nasaba

Kwankwaso Ba Zai Sake Yi Mana Takarar Shugabancin Ƙasa Ba A Zaɓen 2027 Ba – NNPP

Gwamna Ademola Adeleke Ya Ƙaryata Jita-Jitar Sauya Sheƙa Daga PDP Zuwa APC

“Muddin kun cika ka’idojin kowane nau’i, za a ba ku dama. Don haka, ba lallai ne mu ware wa jihohi kaso ba,” in ji ministar.

Ta ce shirin da sauran shirye-shiryen shiga tsakani na gwamnati na da nufin yaki da talauci a kasar.

“Abin da ma’aikatarmu ke yi shi ne samar da hanyar kare lafiyar jama’a da ke hana wadannan mutane fadawa cikin talauci da kuma kokarin fitar da yawancinsu daga talauci.

“Mun tsara shirye-shirye daban-daban, shirye-shiryen kasa, wadanda ake sa ran za su magance matsalar talauci mai dimbin yawa. Tabbas muna da N-Power wanda ya kamata ya samar da ayyukan yi miliyan biyar a cikin shekaru biyar.

Ministar ya kara da cewa “Muna da wasu ayyuka da dama a kasa, dukkansu an yi niyya ne a fannoni daban-daban don yaki da talauci.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AikiEduMatasaMinistaN-PowerTalauci
ShareTweetSendShare
Previous Post

Kotu Ta Kori Sylva Dan Takarar Gwamnan APC A Bayelsa

Next Post

An Kama Masu Laifi 537, An Daure 250 Cikin Wata 3 A Borno

Related

Kwankwaso Ba Zai Sake Yi Mana Takarar Shugabancin Ƙasa Ba A Zaɓen 2027 Ba – NNPP
Manyan Labarai

Kwankwaso Ba Zai Sake Yi Mana Takarar Shugabancin Ƙasa Ba A Zaɓen 2027 Ba – NNPP

4 hours ago
Gwamna Ademola Adeleke Ya Ƙaryata Jita-Jitar Sauya Sheƙa Daga PDP Zuwa APC
Manyan Labarai

Gwamna Ademola Adeleke Ya Ƙaryata Jita-Jitar Sauya Sheƙa Daga PDP Zuwa APC

8 hours ago
‘Yansanda Sun Kama Barayi 15, Sun Kwato Motocin Sata 20 A Kano
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Kama ’Yan Bindiga 17 Tare Da Kashe 3 A Abuja

1 day ago
Kotu Ta Umarci Majalisar Dattijan Nijeriya Da Ta Gaggauta Janye Dakatarwar Da Ta Yi Wa Natasha
Manyan Labarai

Kotu Ta Umarci Majalisar Dattijan Nijeriya Da Ta Gaggauta Janye Dakatarwar Da Ta Yi Wa Natasha

1 day ago
Zanga-zangar ‘Yan Gudun Hijira Na Yelewata ‘Yar Manuniya Ce Ga Daukar Matakan Da Suka Dace
Manyan Labarai

Zanga-zangar ‘Yan Gudun Hijira Na Yelewata ‘Yar Manuniya Ce Ga Daukar Matakan Da Suka Dace

1 day ago
‘Yan Nijeriya Na Kewar Buhari Saboda Azabar Da Suke Fuskanta A Hannun Tinubu – Amaechi
Manyan Labarai

‘Yan Nijeriya Na Kewar Buhari Saboda Azabar Da Suke Fuskanta A Hannun Tinubu – Amaechi

1 day ago
Next Post
An Kama Masu Laifi 537, An Daure 250 Cikin Wata 3 A Borno

An Kama Masu Laifi 537, An Daure 250 Cikin Wata 3 A Borno

LABARAI MASU NASABA

Sin Da Faransa Sun Amince Da Ingiza Cudanyar Mabanbantan Sassa Tare Da Samar Da Karin Tabbaci Ga Duniya

Sin Da Faransa Sun Amince Da Ingiza Cudanyar Mabanbantan Sassa Tare Da Samar Da Karin Tabbaci Ga Duniya

July 5, 2025
Bukatar Ma’aurata Su Rika Bayyana Wa Junansu Gaskiyar Yanayin Samunsu

Bukatar Ma’aurata Su Rika Bayyana Wa Junansu Gaskiyar Yanayin Samunsu

July 5, 2025
Yadda Ake Gasasshen Biredi (Sandwich)

Yadda Ake Gasasshen Biredi (Sandwich)

July 5, 2025
Gyaran Jiki Da Kyawun Fata (5)

Gyaran Jiki Da Kyawun Fata (5)

July 5, 2025
ALGON Ta Taya Gwamnan Sani Murnar Samun Lambar Yabo Ta Kasa

ALGON Ta Taya Gwamnan Sani Murnar Samun Lambar Yabo Ta Kasa

July 5, 2025
Kwankwaso Ba Zai Sake Yi Mana Takarar Shugabancin Ƙasa Ba A Zaɓen 2027 Ba – NNPP

Kwankwaso Ba Zai Sake Yi Mana Takarar Shugabancin Ƙasa Ba A Zaɓen 2027 Ba – NNPP

July 5, 2025
Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu

Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu

July 5, 2025
Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (8)

Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (8)

July 5, 2025
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

An Kama Matashin Da Ya Yi Garkuwa Da Abokinsa Tare Da Karbar Kudin Fansa

July 5, 2025
Gwamna Ademola Adeleke Ya Ƙaryata Jita-Jitar Sauya Sheƙa Daga PDP Zuwa APC

Gwamna Ademola Adeleke Ya Ƙaryata Jita-Jitar Sauya Sheƙa Daga PDP Zuwa APC

July 5, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.