ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, September 11, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Tarayya Za Ta Dauki Matasa Miliyan 5 Aiki A Sabon Shirin N-Power – Minista

by Sadiq
3 years ago
N-Power

Gwamnatin tarayya ta bayyana cewa shirin N-Power da aka sauya wa fasalin zai samar da ayyukan yi akalla miliyan biyar ga matasa a kasar nan.

A cewar ministar harkokin jin-kai da yaki da fatara, Betta Edu, wadda ta bayyana hakan a gidan talabijin na Channels, ta ce shirin N-Power wani bangare ne na samar da tsaro da aka tsara don hana mutane fadawa cikin talauci.

  • Sarkin Kudan Ya Taya Mai Martaba Sarkin Zazzau Murnar Cika Shekara Uku A Karaga
  • Abubuwan Al’ajabi Da Abarba Ke Yi Wajen Gyaran Fata

“Muna aiki a kan matasan Nijeriya miliyan biyar masu shekaru tsakanin 18 zuwa 40 kuma za a dauki miliyan daya a kowace shekara. A kan shirin GEEP, muna aiki kan ‘yan Nijeriya miliyan 1.5,” in ji ta.

ADVERTISEMENT

Kalaman nata ya zo ne kwanaki bayan da gwamnatin tarayya ta dakatar da shirin na N-Power, wani bangare na shirin nan na ‘National Social Investment Programme (NSIP), wanda tsohon shugaban kasa Muhammadu Buhari ya kaddamar a ranar 26 ga watan Yuni, 2016, domin yaki da matsalar rashin aikin yi da matasa ke fuskanta da kuma bunkasa zamantakewar al’umma.

Sai dai a cikin shirin da aka sauya wa fasalin, ministan ta jaddada cewa shirin N-Power zai kasance ne bisa tsarin farko-farko.

LABARAI MASU NASABA

Sakkwato: Al’ummar Tambuwal Sun Yi Zanga-Zanga Kan Taɓarɓarewar Tsaro

Idan Atiku Ya Janye, Za Mu Kula Da Shi Bayan Mun Yi Nasara – Kwankwaso

“Muddin kun cika ka’idojin kowane nau’i, za a ba ku dama. Don haka, ba lallai ne mu ware wa jihohi kaso ba,” in ji ministar.

Ta ce shirin da sauran shirye-shiryen shiga tsakani na gwamnati na da nufin yaki da talauci a kasar.

“Abin da ma’aikatarmu ke yi shi ne samar da hanyar kare lafiyar jama’a da ke hana wadannan mutane fadawa cikin talauci da kuma kokarin fitar da yawancinsu daga talauci.

“Mun tsara shirye-shirye daban-daban, shirye-shiryen kasa, wadanda ake sa ran za su magance matsalar talauci mai dimbin yawa. Tabbas muna da N-Power wanda ya kamata ya samar da ayyukan yi miliyan biyar a cikin shekaru biyar.

Ministar ya kara da cewa “Muna da wasu ayyuka da dama a kasa, dukkansu an yi niyya ne a fannoni daban-daban don yaki da talauci.”

MASU ALAKA

Sakkwato: Al’ummar Tambuwal Sun Yi Zanga-Zanga Kan Taɓarɓarewar Tsaro
Manyan Labarai

Sakkwato: Al’ummar Tambuwal Sun Yi Zanga-Zanga Kan Taɓarɓarewar Tsaro

September 11, 2026
N-Power
Manyan Labarai

Idan Atiku Ya Janye, Za Mu Kula Da Shi Bayan Mun Yi Nasara – Kwankwaso

September 11, 2026
N-Power
Manyan Labarai

ASUU Ta Yi Barazanar Shiga Yajin Aiki Na Ƙasa Gaba Ɗaya

September 11, 2026
Next Post
An Kama Masu Laifi 537, An Daure 250 Cikin Wata 3 A Borno

An Kama Masu Laifi 537, An Daure 250 Cikin Wata 3 A Borno

LABARAI MASU NASABA

Hadin Gwiwar Hada-Hadar Ba Da Hidima Tsakanin Sin Da Afirka Na Karfafa Karfin Afirka

Hadin Gwiwar Hada-Hadar Ba Da Hidima Tsakanin Sin Da Afirka Na Karfafa Karfin Afirka

September 11, 2026
Zaben 2027: Jam’iyyun Siyasa Sun Bayyana Shirinsu Yayin Da INEC Ta Fitar Da Jawalin Zabe

Dalilan Da Ya Sa Jam’iyyun Siyasa Suka Jinkirta Ƙaddamar Da Kwamitin Yaƙin Neman Zaɓen

September 11, 2026
Nazarin CGTN: Kungiyar BRICS Tana Kara Taka Rawar Gani A Harkokin Duniya

Nazarin CGTN: Kungiyar BRICS Tana Kara Taka Rawar Gani A Harkokin Duniya

September 11, 2026
Za A Ci ’Yan Siyasa Masu Kalaman Ɓatanci Tarar Miliyan 10 Da Ɗaurin Watanni 12 — INEC

2027: A Karon Farko INEC Za Ta Ƙaddamar Da Na’urar Bibiyar Zaɓen Nijeriya

September 11, 2026
Me Ya Sa Kamfanonin Amurka Ke Kyautata Zato Ga Sabuwar Damar Sin?

Me Ya Sa Kamfanonin Amurka Ke Kyautata Zato Ga Sabuwar Damar Sin?

September 11, 2026
Gwarzuwar Ma’aikaciyar Gwamnati Ta Shekarar 2026  Mrs Zubaida Umar

Gwarzuwar Ma’aikaciyar Gwamnati Ta Shekarar 2026 Mrs Zubaida Umar

September 11, 2026
Sin Ta Kafa Manufar Shiga Sahun Manyan Kasashen Dake Da Karfi A Harkar Kera Motoci A Duniya Nan Da Shekarar 2030

Sin Ta Kafa Manufar Shiga Sahun Manyan Kasashen Dake Da Karfi A Harkar Kera Motoci A Duniya Nan Da Shekarar 2030

September 11, 2026
Sakkwato: Al’ummar Tambuwal Sun Yi Zanga-Zanga Kan Taɓarɓarewar Tsaro

Sakkwato: Al’ummar Tambuwal Sun Yi Zanga-Zanga Kan Taɓarɓarewar Tsaro

September 11, 2026
Sanata yari

Gwarzon Ɗan Siyasa Na Shekarar 2026 Sanata Abdul’Aziz Abubakar Yari

September 11, 2026
Kasar Sin Za Ta Taimaka Wajen Bunkasa Wadatar Makamashi Da Ci Gaba Mai Dorewa A Duniya

Kasar Sin Za Ta Taimaka Wajen Bunkasa Wadatar Makamashi Da Ci Gaba Mai Dorewa A Duniya

September 11, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.