Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home RIGAR 'YANCI

Jam’iyyar PDP Ta Yi Sabbabin Shugabanni A Karamar Hukumar Lere

by Muhammad
December 2, 2020
in RIGAR 'YANCI
2 min read
Lere
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Daga Isah Ahmed

 

samndaads

Wakilai masu zabe, na ‘yayan jam’iyyar PDP, daga mazabu 11 na Karamar Hukumar Lere, da ke jihar Kaduna, sun gudanar da zaben sababbin shugabannin da zasu ja ragamar shugabancin jam’iyyar, a karamar hukumar a garin Saminaka, a karshen makon da ya gabata.

Sababbin shugabannin da aka zaba, sun hada da Muhammad Lawal Aliyu a matsayin Shugaba, da Jafaru Waziri Mataimakin shugaba da Musa Chitta Sakatare da Surajo Sani Mataimakin sakatare da Dogara Hakuri Shugaban matasa da Iyami Adamu Shugabar Mata da Ahmed Hamza Jami’in watsa labarai da Ummar Abdu Mataimakin jami’in watsa labarai da Abdulwahab Sulaiman Sakataren tsare tsare da Turaki Shawara Sakataren kudi da Hayatu Ibrahim mai binciken kudi da Dauda S. Umar Ma’ajiyi da Bello Jafaru Mai bayar da shawara kan harkokin shari’a.

Da ya ke jawabi bayan kammala zaben, Mataimakin shugaban jam’iyyar PDP na jihar Kaduna, Alhaji Ibrahim Lawal Nuhu Kayarda ya taya sababbin shugabannin, murnar nasarar da suka samu.

Ya yi fatar wannan nasara zata kawo wa jam’iyyar nasara, a karamar hukumar a zabubbuka masu zuwa.

Ya yi kira ga al’ummar karamar su zauna lafiya, kuma su cigaba da zamantakewa kamar yadda a ka saba.

Shi ma a nasa jawabin, Dan majalisar wakilai ta ta tarayya Mai wakiltar mazabar Lere, Alhaji Muhammad Lawal Rabi’u ya yi kira ga shugabannin da aka zaba, su rungumi kowa da kowa.

“Dole ne ku tsaya ku ga yadda zaku hada kan ‘yayan wannan jam’iyya, a karamar hukumar Lere. Domin jam’iyyar ta sami nasara a dukkan zabubbukan da za a gudanar nan gaba.Kuma ina kira ga dukkan magoya bayan jam’iyyar PDP na Najeriya, mu hada kai mu yi hakuri da juna. Domin sai mun hada kai, mun yi hakuri da juna, sanna ne zamu sami nasarar karbar, gwamnatin kasar nan.”

A nasa jawabin, Sabon Shugaban jam’iyyar ta PDP na Karamar Hukumar ta Lere, Muhammad Lawal Aliyu Saminaka ya yi godiyz ga Allah, kan wannan nasara da ya samu, kuma ya yi godiya ga dukkan wadanda suka bada gudunmawa, wajen ganin an sami wannan nasara.

Ya yi kira ga wadanda suka yi takara, su zo su hada kai domin su sami nasara a wannan jam’iyya, a dukkan zabubbuka masu zuwa.

SendShareTweetShare
Previous Post

Madakin Lokoja, Ali Autan Yaya, Ya Kwanta Dama

Next Post

Barayin Waya Sun Yi Wa Wani Matashi Yankan Rago A Kano

RelatedPosts

Ebonyi

Kwamishinan ’Yan Sandan Ebonyi Ya Kama Hadiman Gwamnan Jihar Biyu Da Shugaban Karamar Hukuma

by Muhammad
18 hours ago
0

Daga Rabiu Ali Indabawa, Rundunar 'yan sanda ta kama wasu...

Direbobi

Bakwai Sun Mutu Da Yawa Sun Jikkata A Rikicin Shugabancin Kungiyar Direbobi

by Muhammad
18 hours ago
0

Daga Rabiu Ali Indabawa, A kalla mutane bakwai ne suka...

Takalmi

Mata Ta Rafka Wa Mijinta Tsinin Dunduniyar Takalmi Ya Mutu

by Muhammad
18 hours ago
0

Daga Rabiu Ali Indabawa, Wata mata da ba a bayyana...

Next Post
Barayin waya

Barayin Waya Sun Yi Wa Wani Matashi Yankan Rago A Kano

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

Leadership Epaper
ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version