• English
  • Business News
Thursday, September 18, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Jam’iyyatu Ansaariddeen Attajjaniyya Ta Hada Hannu Da Kungiyoyin Waje Domin Ci Gaban Al’umma

by Sulaiman
2 years ago
in Rahotonni
0
Jam’iyyatu Ansaariddeen Attajjaniyya Ta Hada Hannu Da Kungiyoyin Waje Domin Ci Gaban Al’umma
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kungiyar Jam’iyyatu Ansaariddeen Attajjaniyya (JAMAAT) ta yi hadin gwiwa da kungiyoyin kasashen waje domin ciyar da al’ummar Nijeriya dama na duniya baki daya gaba.

Kungiyar JAMAAT ta gudanar da taron hadin gwiwar ne shalkwatanta da ke 4th Abenue a Gwarinpa cikin garin Abuja, wanda ya sama halartar manyan baki ciki da wajen Nijeriya,
Da yake jawabi a wurin taron hadin gwiwar, Babban Sakataren Kungiyar JAMAAT na kasa, Alhaji Alkasim Yahaya ya bayyana cewa an gudanar da wannan taron hadin gwiwa ne domin lalubo hanyar da za a hada hannu da karfe wajen ciyar da al’ummar kasar nan gaba.

  • Kyawawan Abubuwa Da Allah Ya Yi Wa Manzon Allah (SAW) Na Girmamawa

Ya kara da cewa ya tabbatar da cewa hadin gwiwar kungiyoyin zai samar da gagarimin sauyi ga kasar nan dama al’ummar Afirka da kuma na duniya baki daya.

Ya ce, “Tabbas na san cewa a duk lokacin da ake kokarin hadin kai, to dole ne a bukaci gina gaskiya a tsakanin juna. Tarihi ya nuna cewa akwai masu bukatar shigowa kasar nan domin zuba jari ko kuma bayar da taimako, amma daga kasarshe sakamakon rashin gaskiya sai abun ya watse.

“Yadda na ga wannan gagarumin taro wanda ya hada mutane wuri guda ba tare da nuna bambancin addini ba, lallai za a samu sauyin da ake bukata. Yana da matukar muhimmanci mu wanzar da gaskiya a tsakaninmu, saboda mu kasance jakadu na kwarai. Domin ta haka ne kadai za mu iya gudanar da abubuwa yadda ake bukata.

Labarai Masu Nasaba

Yadda Ahlul Faidhati Mai Diwani Group Suka Yi Maulidin Cikar Annabi (SAW) Shekara 1,500 Da Haihuwa 

Abin Fargaba Ne Yadda Bashin Nijeriya Ya Haura Tiriliyan 149 – Shugaban Majalisar Wakilai 

“Mun san cewa a wasu daga cikinmu sun fi wasu, amma mun kasance tare ne domin masu karfi su tallafa wa masu rauni ta yadda za a samu al’umma nagari.

Talaka na bukatar kiwon lafiya, abinci da sauran abubuwa masu yawa wanda idan har bai same su ba, to ba zai taba samun natsuwa ba. Mun dai samu mummunar tarihi ne na bullowar muyagun laifuka kamar irin sun kungiyoyi masu tayar da kayar baya da da ‘yan bindiga da dai sauran muyagun laifukan da mu taba ganin irinsu ba a cikin kasar nan sakamakon rashin tallafa wa al’umma.

“Dole ne mu fahimci abubuwan da suke faruwa domin mu cimma burikanmu na taimakon al’umma. Mun hadu ne a nan saboda mu yi aiki kafada da kafada cikin gaskiya da rikon amana domin kanmu. A bangaren wannan kungiya, za mu ci gaba da yin aiki domin tantance yankunan da suka fi bukatar taimako. Za mu tabbatar da cewa duk abin da muka tattara zai kai ga mutanen da ake bukata, domin za a dunga daukan bayanen abubuwan da muka yi ta yadda duniya za ta ga abun da muka yi.

Haka kuma ya ce duk da matsalolin al’umma suna da yawan gaske, amma za a fara bayar da tallafin ne ta bangaren kiwon lafiya, saboda yana yin muhallin da al’umma ke raywa a ciki.

Tun da farko, mataimakin sakataren kungiyar JAMAAT na kasa, Murtala Abdul-Rahman ya kawo tarihin kungiyar a takaice. Ya ce kungiya ce da take gudanar da ayyukanta a dukkan fadin duniya wanda take da rassa a kasarshe daban-daban da ke fadin duniya.
Ya ce jagoran Darikan Tijjaniyya, Sheik Ibrahim Inyass ne ya kirkiro kungiyar domin inganta rayuwar al’umma da ke rayuwa a ban kasa.

Mataimakin sakataren ya ce kungiyar tana kokarin habaka kowani fanni, amma tafi mayar da hankali ne wajen ilmantar da al’umma, sai kuma bangaren kiwon lafiya ta yadda take taimakawo ciki har da gina asibitoci da samar da kayayyakin aiki a bangaren kiwon lafiya da kuma bayar da tallafi ga bangaren.

A cewarsa, kungiyar tana kokarin kawar da talauci a cikin al’umma ta hanyar bayar da taimakon tallafin kudaden sana’a da samar da cibiyoyin koyon sana’o’i.

Ya ce kungiyar tana taimaka wa wadanda ibtila’i ya rutsa da su kamar na ambaliyar ruwa ko ‘yan gudun hijira, wanda take samar musu da abinci da kiwon lafiya da dai sauransu.

Mataimakin sakataren ya ce kungiyar tana tallafa wa mata wajen ganin sun dogara da kansu, wanda ya hada da tallafa musu wajen koyon sana’o’in hannu da kuma kare hakkinsu.

Ya ce kungiyar tana karfafa zumunci a tsakanin Musulmai da wadanda ba Musulmai ba domin samun fahimtar juna da zai kawo ci gaban al’umma, wanda take daukan nauyin shirya taron kara wa juna sani a tsakanin addinai a nan cikin gina Nijeriya da kuma kasashen ketare.

A cewarsa, kungiyar tana mayar da hankali kan habaka rayuwar matasa, wanda take samar da horo a tsakanin matasa domin inganta rayuwarsu. Ya ce kungiyar tana kai ziyara a gidagen yari domin tallafa wa dauraru, sannan tana shirya taron ciyarwa ga al’umma da kuma shirya gasa iri-iri a tsakanin matasa.

Da take mayar da jawabi a wurin taron hadin gwiwar, daya daga cikin ‘ya’yan kungiyar Rayuwa Da Zurfi, Iyabo Samuel ta bayyana cewa idan Allah ya yarda za a cimma abin ake bukata. Ta ce suna aiki ne kafada da kafada da sauran kungiyoyi da ke Dubai da Amurka wajen tallafa wa al’umma.

A cewarta, a kowani lokaci daga yanzu za su kawo na’urorir duba lafiyar mutane guda 37 da za a rarraba a dukkan jihohin Nijeriya ciki har da Abuja, sannan kuma kungiyar Rayuwa da Zurfi ne za ta ci gaba da kulawa da na’urorin.

Ta ce za su yi aiki kafada da kafada da kungiyar JAMAAT wajen taimakon al’umma, sannan suna bukatar hadin kai kowa da kowa domin inganta rayuwar al’ummar Nijeriya. Ta ce Allah ya albarkaci Nijeriya da arziki mai yawa, amma babu jagoranci mai kyau wanda hakan ne ya je fa al’ummar kasar cikin mawuyacin halai. Ta ce wannan ne ya sa suka mayar da hankali kan sake gina rayuwar mutane a Nijeriya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Darikar TijjaniyyaTijjaniyya
ShareTweetSendShare
Previous Post

Karancin Masara: Sana’ar Kiwon Kaji Ta Fiye Da Dala Biliyan 4 Na Cikin Garari

Next Post

Munakisar Turawan Yamma A Juyin Mulkin Nijar –Farfesa Dikwa

Related

Ahlul Faidhati Mai Diwani Group
Rahotonni

Yadda Ahlul Faidhati Mai Diwani Group Suka Yi Maulidin Cikar Annabi (SAW) Shekara 1,500 Da Haihuwa 

6 days ago
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace
Rahotonni

Abin Fargaba Ne Yadda Bashin Nijeriya Ya Haura Tiriliyan 149 – Shugaban Majalisar Wakilai 

1 week ago
Arewa
Rahotonni

Matsalar Tsaro: Gwamnonin Arewa Sun Bullo Da Sabbin Matakan Yaki Da Ta’addanci

2 weeks ago
'Yan Bindiga
Rahotonni

Sulhu Da ‘Yan Bindiga Ya Fara Haifar Da Da Mai Ido A Katsina

2 weeks ago
Gidauniyar ‘Ya’yan Sarakunan Arewa Sun Marawa Sarkin Musulmi A Matsayin Shugaban Majalisar Sarakuna
Rahotonni

Babban Taron Lauyoyi Na Kasa: Sarkin Musulmi Ya Gargadi Alkalai Kan Tabbatar Da Adalci

3 weeks ago
Sin Ta Fara Amfani Da Tauraron Dan Adam Wajen Duba Manyan Hanyoyin Wutar Lantarki A Karo Na Farko
Rahotonni

Cire Tallafin Wutar Lantarki Zai Kara Kuntata Rayuwar ‘Yan Nijeriya – Kungiyar Kwadago

3 weeks ago
Next Post
Munakisar Turawan Yamma A Juyin Mulkin Nijar –Farfesa Dikwa

Munakisar Turawan Yamma A Juyin Mulkin Nijar –Farfesa Dikwa

LABARAI MASU NASABA

An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

’Yansanda Sun Kama Sojan Gona Da Motocin Sata 3 A Jigawa

September 18, 2025
Yadda Muka Zama Bayin ‘Yan Bindiga -Mazaunin Wani Kauye

’Yan Bindiga Sun Sako Ma’aurata A Katsina Bayan Karɓar N50m A Matsayin Kuɗin Fansa

September 18, 2025
Yadda Ribas Ta Yi Cikar Ƙwari Yayin Da Gwamna Fubara Ya Koma Ofis

Yadda Ribas Ta Yi Cikar Ƙwari Yayin Da Gwamna Fubara Ya Koma Ofis

September 18, 2025
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

September 18, 2025
’Yansanda Sun Kama Mutane 9 Kan Yin Ƙaryar Sace Su A Jihar Neja

’Yansanda Sun Kama Mutane 9 Kan Yin Ƙaryar Sace Su A Jihar Neja

September 18, 2025
Sojoji Sun Kama Ƙasurgumin Ɗan Bindiga, Sun Kashe Shugaban IPOB

Sojoji Sun Cafke Babban Kwamandan IPOB

September 18, 2025
Ya Kamata A Kiyaye Nasarorin Da Aka Cimma A Shawarwarin Sin Da Amurka 

Ya Kamata A Kiyaye Nasarorin Da Aka Cimma A Shawarwarin Sin Da Amurka 

September 17, 2025
Yawan Kadarorin Kamfanoni Mallakar Gwamnatin Sin Ya Wuce Yuan Triliyan 90 a Lokacin Shirin Raya Kasa Na 14 Na Shekaru 5 

Yawan Kadarorin Kamfanoni Mallakar Gwamnatin Sin Ya Wuce Yuan Triliyan 90 a Lokacin Shirin Raya Kasa Na 14 Na Shekaru 5 

September 17, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Dawo Da Karatun Tarihi A Makarantu

Gwamnatin Tarayya Ta Dawo Da Karatun Tarihi A Makarantu

September 17, 2025
Yakin Haraji Da Cinikayya Ba Zai Gurgunta Fifikon Da Sin Ke Da Shi A Fannin Raya Masana’antun Sarrafa Hajoji Da Kasar Ta Gina A Tsawon Lokaci Ba

Yakin Haraji Da Cinikayya Ba Zai Gurgunta Fifikon Da Sin Ke Da Shi A Fannin Raya Masana’antun Sarrafa Hajoji Da Kasar Ta Gina A Tsawon Lokaci Ba

September 17, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.