• English
  • Business News
Wednesday, July 2, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Jam’iyyatu Ansaariddeen Attajjaniyya Ta Hada Hannu Da Kungiyoyin Waje Domin Ci Gaban Al’umma

by Sulaiman
2 years ago
in Rahotonni
0
Jam’iyyatu Ansaariddeen Attajjaniyya Ta Hada Hannu Da Kungiyoyin Waje Domin Ci Gaban Al’umma
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kungiyar Jam’iyyatu Ansaariddeen Attajjaniyya (JAMAAT) ta yi hadin gwiwa da kungiyoyin kasashen waje domin ciyar da al’ummar Nijeriya dama na duniya baki daya gaba.

Kungiyar JAMAAT ta gudanar da taron hadin gwiwar ne shalkwatanta da ke 4th Abenue a Gwarinpa cikin garin Abuja, wanda ya sama halartar manyan baki ciki da wajen Nijeriya,
Da yake jawabi a wurin taron hadin gwiwar, Babban Sakataren Kungiyar JAMAAT na kasa, Alhaji Alkasim Yahaya ya bayyana cewa an gudanar da wannan taron hadin gwiwa ne domin lalubo hanyar da za a hada hannu da karfe wajen ciyar da al’ummar kasar nan gaba.

  • Kyawawan Abubuwa Da Allah Ya Yi Wa Manzon Allah (SAW) Na Girmamawa

Ya kara da cewa ya tabbatar da cewa hadin gwiwar kungiyoyin zai samar da gagarimin sauyi ga kasar nan dama al’ummar Afirka da kuma na duniya baki daya.

Ya ce, “Tabbas na san cewa a duk lokacin da ake kokarin hadin kai, to dole ne a bukaci gina gaskiya a tsakanin juna. Tarihi ya nuna cewa akwai masu bukatar shigowa kasar nan domin zuba jari ko kuma bayar da taimako, amma daga kasarshe sakamakon rashin gaskiya sai abun ya watse.

“Yadda na ga wannan gagarumin taro wanda ya hada mutane wuri guda ba tare da nuna bambancin addini ba, lallai za a samu sauyin da ake bukata. Yana da matukar muhimmanci mu wanzar da gaskiya a tsakaninmu, saboda mu kasance jakadu na kwarai. Domin ta haka ne kadai za mu iya gudanar da abubuwa yadda ake bukata.

Labarai Masu Nasaba

Sarkakiyar Da Ke Tattare Da Zaben 2027 Da Yadda Za Ta Kaya

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

“Mun san cewa a wasu daga cikinmu sun fi wasu, amma mun kasance tare ne domin masu karfi su tallafa wa masu rauni ta yadda za a samu al’umma nagari.

Talaka na bukatar kiwon lafiya, abinci da sauran abubuwa masu yawa wanda idan har bai same su ba, to ba zai taba samun natsuwa ba. Mun dai samu mummunar tarihi ne na bullowar muyagun laifuka kamar irin sun kungiyoyi masu tayar da kayar baya da da ‘yan bindiga da dai sauran muyagun laifukan da mu taba ganin irinsu ba a cikin kasar nan sakamakon rashin tallafa wa al’umma.

“Dole ne mu fahimci abubuwan da suke faruwa domin mu cimma burikanmu na taimakon al’umma. Mun hadu ne a nan saboda mu yi aiki kafada da kafada cikin gaskiya da rikon amana domin kanmu. A bangaren wannan kungiya, za mu ci gaba da yin aiki domin tantance yankunan da suka fi bukatar taimako. Za mu tabbatar da cewa duk abin da muka tattara zai kai ga mutanen da ake bukata, domin za a dunga daukan bayanen abubuwan da muka yi ta yadda duniya za ta ga abun da muka yi.

Haka kuma ya ce duk da matsalolin al’umma suna da yawan gaske, amma za a fara bayar da tallafin ne ta bangaren kiwon lafiya, saboda yana yin muhallin da al’umma ke raywa a ciki.

Tun da farko, mataimakin sakataren kungiyar JAMAAT na kasa, Murtala Abdul-Rahman ya kawo tarihin kungiyar a takaice. Ya ce kungiya ce da take gudanar da ayyukanta a dukkan fadin duniya wanda take da rassa a kasarshe daban-daban da ke fadin duniya.
Ya ce jagoran Darikan Tijjaniyya, Sheik Ibrahim Inyass ne ya kirkiro kungiyar domin inganta rayuwar al’umma da ke rayuwa a ban kasa.

Mataimakin sakataren ya ce kungiyar tana kokarin habaka kowani fanni, amma tafi mayar da hankali ne wajen ilmantar da al’umma, sai kuma bangaren kiwon lafiya ta yadda take taimakawo ciki har da gina asibitoci da samar da kayayyakin aiki a bangaren kiwon lafiya da kuma bayar da tallafi ga bangaren.

A cewarsa, kungiyar tana kokarin kawar da talauci a cikin al’umma ta hanyar bayar da taimakon tallafin kudaden sana’a da samar da cibiyoyin koyon sana’o’i.

Ya ce kungiyar tana taimaka wa wadanda ibtila’i ya rutsa da su kamar na ambaliyar ruwa ko ‘yan gudun hijira, wanda take samar musu da abinci da kiwon lafiya da dai sauransu.

Mataimakin sakataren ya ce kungiyar tana tallafa wa mata wajen ganin sun dogara da kansu, wanda ya hada da tallafa musu wajen koyon sana’o’in hannu da kuma kare hakkinsu.

Ya ce kungiyar tana karfafa zumunci a tsakanin Musulmai da wadanda ba Musulmai ba domin samun fahimtar juna da zai kawo ci gaban al’umma, wanda take daukan nauyin shirya taron kara wa juna sani a tsakanin addinai a nan cikin gina Nijeriya da kuma kasashen ketare.

A cewarsa, kungiyar tana mayar da hankali kan habaka rayuwar matasa, wanda take samar da horo a tsakanin matasa domin inganta rayuwarsu. Ya ce kungiyar tana kai ziyara a gidagen yari domin tallafa wa dauraru, sannan tana shirya taron ciyarwa ga al’umma da kuma shirya gasa iri-iri a tsakanin matasa.

Da take mayar da jawabi a wurin taron hadin gwiwar, daya daga cikin ‘ya’yan kungiyar Rayuwa Da Zurfi, Iyabo Samuel ta bayyana cewa idan Allah ya yarda za a cimma abin ake bukata. Ta ce suna aiki ne kafada da kafada da sauran kungiyoyi da ke Dubai da Amurka wajen tallafa wa al’umma.

A cewarta, a kowani lokaci daga yanzu za su kawo na’urorir duba lafiyar mutane guda 37 da za a rarraba a dukkan jihohin Nijeriya ciki har da Abuja, sannan kuma kungiyar Rayuwa da Zurfi ne za ta ci gaba da kulawa da na’urorin.

Ta ce za su yi aiki kafada da kafada da kungiyar JAMAAT wajen taimakon al’umma, sannan suna bukatar hadin kai kowa da kowa domin inganta rayuwar al’ummar Nijeriya. Ta ce Allah ya albarkaci Nijeriya da arziki mai yawa, amma babu jagoranci mai kyau wanda hakan ne ya je fa al’ummar kasar cikin mawuyacin halai. Ta ce wannan ne ya sa suka mayar da hankali kan sake gina rayuwar mutane a Nijeriya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Darikar TijjaniyyaTijjaniyya
ShareTweetSendShare
Previous Post

Karancin Masara: Sana’ar Kiwon Kaji Ta Fiye Da Dala Biliyan 4 Na Cikin Garari

Next Post

Munakisar Turawan Yamma A Juyin Mulkin Nijar –Farfesa Dikwa

Related

jam'iyyu
Rahotonni

Sarkakiyar Da Ke Tattare Da Zaben 2027 Da Yadda Za Ta Kaya

3 weeks ago
Ansaariddeen
Rahotonni

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

3 weeks ago
Tsadar Rayuwa: Yadda Al’umma Suka Yi Sallah Cikin Kunci
Rahotonni

Tsadar Rayuwa: Yadda Al’umma Suka Yi Sallah Cikin Kunci

4 weeks ago
Ana Fargabar Boko Haram Ta Kara Mamaye Wasu Kananan Hukumomi A Borno
Rahotonni

Ana Fargabar Boko Haram Ta Kara Mamaye Wasu Kananan Hukumomi A Borno

1 month ago
Kokarin Minista Tuggar Na Mayar Da Hijirar Masana Daga Nijeriya Zuwa Kasashen Waje Alhairi
Rahotonni

Kokarin Minista Tuggar Na Mayar Da Hijirar Masana Daga Nijeriya Zuwa Kasashen Waje Alhairi

1 month ago
Faduwar Jarrabawar JAMB Ta Tayar Da Bukatar Neman Sake Fasalin Hukumar
Rahotonni

Faduwar Jarrabawar JAMB Ta Tayar Da Bukatar Neman Sake Fasalin Hukumar

1 month ago
Next Post
Munakisar Turawan Yamma A Juyin Mulkin Nijar –Farfesa Dikwa

Munakisar Turawan Yamma A Juyin Mulkin Nijar –Farfesa Dikwa

LABARAI MASU NASABA

An Dakatar Da Shugaban APC Na Jihar Nasarawa

An Dakatar Da Shugaban APC Na Jihar Nasarawa

July 1, 2025
Tawagar Gwamnatin Tarayya Da Ɗangote Sun Halarci Jana’izar Aminu Ɗantata A Saudiyya

Tawagar Gwamnatin Tarayya Da Ɗangote Sun Halarci Jana’izar Aminu Ɗantata A Saudiyya

July 1, 2025
An Gudanar Da Bikin Daga Tuta Da Bikin Murnar Cika Shekaru 28 Da Dawowar Yankin HK Karkashin Kasar Sin

An Gudanar Da Bikin Daga Tuta Da Bikin Murnar Cika Shekaru 28 Da Dawowar Yankin HK Karkashin Kasar Sin

July 1, 2025
Ɗantata: Majalisar Dattawa Ta Ɗage Taron Jin Ra’ayin Jama’a A Arewa maso Yamma

Ɗantata: Majalisar Dattawa Ta Ɗage Taron Jin Ra’ayin Jama’a A Arewa maso Yamma

July 1, 2025
Kayan Aro Baya Rufe Katara

Kayan Aro Baya Rufe Katara

July 1, 2025
Gwamnatin Zamfara Ta Tabbatar Da Kashe Manyan Mayakan Bello Turji Fiye Da 100

Askarawan Zamfara Sun Kashe Riƙaƙƙen Ɗan Bindiga, Kacalla Ɗanbokolo Ubangidan Turji

July 1, 2025
Tawagar Likitoci Ta Sin Ta Ba Da Horon Fasahar Likitancin Gargajiya Ta Sin A Nijar

Tawagar Likitoci Ta Sin Ta Ba Da Horon Fasahar Likitancin Gargajiya Ta Sin A Nijar

July 1, 2025
Farfesa Haruna Musa Ya Lashe Zaɓen Shugabancin Jami’ar Bayero Ta Kano

Farfesa Haruna Musa Ya Lashe Zaɓen Shugabancin Jami’ar Bayero Ta Kano

July 1, 2025
Fahimtar Sabon Tunani: Yadda Sin Ta Samu Bunkasa A Tarihi Ta Hanyar Juyin Juya Halin Da Take Yi Wa Kanta 

Fahimtar Sabon Tunani: Yadda Sin Ta Samu Bunkasa A Tarihi Ta Hanyar Juyin Juya Halin Da Take Yi Wa Kanta 

July 1, 2025
An Yi Bikin Kade-Kade Don Taya Murnar Cika Shekaru 104 Da Kafuwar JKS

An Yi Bikin Kade-Kade Don Taya Murnar Cika Shekaru 104 Da Kafuwar JKS

July 1, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.