ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 5, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Jam’iyyatu Ansaariddeen Attajjaniyya Ta Hada Hannu Da Kungiyoyin Waje Domin Ci Gaban Al’umma

by Sulaiman
3 years ago
Ansaariddeen

Kungiyar Jam’iyyatu Ansaariddeen Attajjaniyya (JAMAAT) ta yi hadin gwiwa da kungiyoyin kasashen waje domin ciyar da al’ummar Nijeriya dama na duniya baki daya gaba.

Kungiyar JAMAAT ta gudanar da taron hadin gwiwar ne shalkwatanta da ke 4th Abenue a Gwarinpa cikin garin Abuja, wanda ya sama halartar manyan baki ciki da wajen Nijeriya,
Da yake jawabi a wurin taron hadin gwiwar, Babban Sakataren Kungiyar JAMAAT na kasa, Alhaji Alkasim Yahaya ya bayyana cewa an gudanar da wannan taron hadin gwiwa ne domin lalubo hanyar da za a hada hannu da karfe wajen ciyar da al’ummar kasar nan gaba.

  • Kyawawan Abubuwa Da Allah Ya Yi Wa Manzon Allah (SAW) Na Girmamawa

Ya kara da cewa ya tabbatar da cewa hadin gwiwar kungiyoyin zai samar da gagarimin sauyi ga kasar nan dama al’ummar Afirka da kuma na duniya baki daya.

ADVERTISEMENT

Ya ce, “Tabbas na san cewa a duk lokacin da ake kokarin hadin kai, to dole ne a bukaci gina gaskiya a tsakanin juna. Tarihi ya nuna cewa akwai masu bukatar shigowa kasar nan domin zuba jari ko kuma bayar da taimako, amma daga kasarshe sakamakon rashin gaskiya sai abun ya watse.

“Yadda na ga wannan gagarumin taro wanda ya hada mutane wuri guda ba tare da nuna bambancin addini ba, lallai za a samu sauyin da ake bukata. Yana da matukar muhimmanci mu wanzar da gaskiya a tsakaninmu, saboda mu kasance jakadu na kwarai. Domin ta haka ne kadai za mu iya gudanar da abubuwa yadda ake bukata.

LABARAI MASU NASABA

Ko Yakin Iran Zai Kawo Karshen Kawancen Amurka Da Kasashen Larabawa?

Yadda Sauya Shekar ‘Yan Siyasa Ta Sauya Fasalin Majalisar Dokokin Kasa

“Mun san cewa a wasu daga cikinmu sun fi wasu, amma mun kasance tare ne domin masu karfi su tallafa wa masu rauni ta yadda za a samu al’umma nagari.

Talaka na bukatar kiwon lafiya, abinci da sauran abubuwa masu yawa wanda idan har bai same su ba, to ba zai taba samun natsuwa ba. Mun dai samu mummunar tarihi ne na bullowar muyagun laifuka kamar irin sun kungiyoyi masu tayar da kayar baya da da ‘yan bindiga da dai sauran muyagun laifukan da mu taba ganin irinsu ba a cikin kasar nan sakamakon rashin tallafa wa al’umma.

“Dole ne mu fahimci abubuwan da suke faruwa domin mu cimma burikanmu na taimakon al’umma. Mun hadu ne a nan saboda mu yi aiki kafada da kafada cikin gaskiya da rikon amana domin kanmu. A bangaren wannan kungiya, za mu ci gaba da yin aiki domin tantance yankunan da suka fi bukatar taimako. Za mu tabbatar da cewa duk abin da muka tattara zai kai ga mutanen da ake bukata, domin za a dunga daukan bayanen abubuwan da muka yi ta yadda duniya za ta ga abun da muka yi.

Haka kuma ya ce duk da matsalolin al’umma suna da yawan gaske, amma za a fara bayar da tallafin ne ta bangaren kiwon lafiya, saboda yana yin muhallin da al’umma ke raywa a ciki.

Tun da farko, mataimakin sakataren kungiyar JAMAAT na kasa, Murtala Abdul-Rahman ya kawo tarihin kungiyar a takaice. Ya ce kungiya ce da take gudanar da ayyukanta a dukkan fadin duniya wanda take da rassa a kasarshe daban-daban da ke fadin duniya.
Ya ce jagoran Darikan Tijjaniyya, Sheik Ibrahim Inyass ne ya kirkiro kungiyar domin inganta rayuwar al’umma da ke rayuwa a ban kasa.

Mataimakin sakataren ya ce kungiyar tana kokarin habaka kowani fanni, amma tafi mayar da hankali ne wajen ilmantar da al’umma, sai kuma bangaren kiwon lafiya ta yadda take taimakawo ciki har da gina asibitoci da samar da kayayyakin aiki a bangaren kiwon lafiya da kuma bayar da tallafi ga bangaren.

A cewarsa, kungiyar tana kokarin kawar da talauci a cikin al’umma ta hanyar bayar da taimakon tallafin kudaden sana’a da samar da cibiyoyin koyon sana’o’i.

Ya ce kungiyar tana taimaka wa wadanda ibtila’i ya rutsa da su kamar na ambaliyar ruwa ko ‘yan gudun hijira, wanda take samar musu da abinci da kiwon lafiya da dai sauransu.

Mataimakin sakataren ya ce kungiyar tana tallafa wa mata wajen ganin sun dogara da kansu, wanda ya hada da tallafa musu wajen koyon sana’o’in hannu da kuma kare hakkinsu.

Ya ce kungiyar tana karfafa zumunci a tsakanin Musulmai da wadanda ba Musulmai ba domin samun fahimtar juna da zai kawo ci gaban al’umma, wanda take daukan nauyin shirya taron kara wa juna sani a tsakanin addinai a nan cikin gina Nijeriya da kuma kasashen ketare.

A cewarsa, kungiyar tana mayar da hankali kan habaka rayuwar matasa, wanda take samar da horo a tsakanin matasa domin inganta rayuwarsu. Ya ce kungiyar tana kai ziyara a gidagen yari domin tallafa wa dauraru, sannan tana shirya taron ciyarwa ga al’umma da kuma shirya gasa iri-iri a tsakanin matasa.

Da take mayar da jawabi a wurin taron hadin gwiwar, daya daga cikin ‘ya’yan kungiyar Rayuwa Da Zurfi, Iyabo Samuel ta bayyana cewa idan Allah ya yarda za a cimma abin ake bukata. Ta ce suna aiki ne kafada da kafada da sauran kungiyoyi da ke Dubai da Amurka wajen tallafa wa al’umma.

A cewarta, a kowani lokaci daga yanzu za su kawo na’urorir duba lafiyar mutane guda 37 da za a rarraba a dukkan jihohin Nijeriya ciki har da Abuja, sannan kuma kungiyar Rayuwa da Zurfi ne za ta ci gaba da kulawa da na’urorin.

Ta ce za su yi aiki kafada da kafada da kungiyar JAMAAT wajen taimakon al’umma, sannan suna bukatar hadin kai kowa da kowa domin inganta rayuwar al’ummar Nijeriya. Ta ce Allah ya albarkaci Nijeriya da arziki mai yawa, amma babu jagoranci mai kyau wanda hakan ne ya je fa al’ummar kasar cikin mawuyacin halai. Ta ce wannan ne ya sa suka mayar da hankali kan sake gina rayuwar mutane a Nijeriya.

Ansaariddeen
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya
  • Sulaiman
    Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina
  • Sulaiman
    Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026
  • Sulaiman
    Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

MASU ALAKA

Ansaariddeen
Rahotonni

Ko Yakin Iran Zai Kawo Karshen Kawancen Amurka Da Kasashen Larabawa?

May 17, 2026
Ansaariddeen
Rahotonni

Yadda Sauya Shekar ‘Yan Siyasa Ta Sauya Fasalin Majalisar Dokokin Kasa

May 16, 2026
Abincin Da Ya Kamata Ku Ci Lokacin Al’ada
Rahotonni

Almajiranci:Matsala Ko Maslaha

May 10, 2026
Next Post
Munakisar Turawan Yamma A Juyin Mulkin Nijar –Farfesa Dikwa

Munakisar Turawan Yamma A Juyin Mulkin Nijar –Farfesa Dikwa

LABARAI MASU NASABA

An Cafke Motocin Dako 50 Makare Da Abinci Za Su Shiga Nijar A Zamfara

Shekara 3 Da Shirin Ceto Jihar Zamfara: Jinjina Ta Musamman Ga Gwamna Dauda Lawal

June 5, 2026
Jami’an Tsaro Sun Cafke Masu Garkuwa Da Mutane 4, Sun Ceto Uwa Da Ɗanta A Bauchi

Jami’an Tsaro Sun Cafke Masu Garkuwa Da Mutane 4, Sun Ceto Uwa Da Ɗanta A Bauchi

June 5, 2026
An Yi Tir Da ‘Yan Takarar Da Suka Fice Daga APC Saboda Faduwa Zabe

An Yi Tir Da ‘Yan Takarar Da Suka Fice Daga APC Saboda Faduwa Zabe

June 5, 2026
Ƴansanda Sun Daƙile Yunƙurin Garkuwa Da Wasu Ma’aurata A Abuja

Ƴansanda Sun Daƙile Yunƙurin Garkuwa Da Wasu Ma’aurata A Abuja

June 5, 2026
Kotu Ta Yi Gwanjon Kaddarorin Sani Sha’aban Bisa Taurin Bashi

Kotu Ta Yi Gwanjon Kaddarorin Sani Sha’aban Bisa Taurin Bashi

June 5, 2026
An Yi Suka Kan Mayar Da Nijeriya Jujin Jibge Kwantaina Da Ake Shigowa Da Su

An Yi Suka Kan Mayar Da Nijeriya Jujin Jibge Kwantaina Da Ake Shigowa Da Su

June 5, 2026
Dorewar Tattalin Arzikin Duniya Ya Dogara Ne Kan Ayyukan Tashoshin Jiragen Ruwa Na Afrika Ta Tsakiya, Cewar Dantsoho

Dorewar Tattalin Arzikin Duniya Ya Dogara Ne Kan Ayyukan Tashoshin Jiragen Ruwa Na Afrika Ta Tsakiya, Cewar Dantsoho

June 5, 2026
Sabon Rikicin Manoma Da Makiyaya yayi Ajalin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Sabon Rikicin Manoma Da Makiyaya yayi Ajalin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 5, 2026
Babu Wani Shiri Na Kwaso ‘Yan Nijeriya Daga Falasdin Ko Isra’ila –Gwamnatin Tarayya

Mulkin Tinubu A Shekara 3:Ina Aka Fito? Ina Aka Dosa?

June 5, 2026
Hajji 2026: Mahajjata 1,905 Sun Dawo Nijeriya Daga Saudiyya

Hajji 2026: Mahajjata 1,905 Sun Dawo Nijeriya Daga Saudiyya

June 5, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.