• English
  • Business News
Tuesday, May 13, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Jan Aikin Da Ke Gaban Sababbin Shugabannin Kano Pillars

by Abba Ibrahim Wada
9 months ago
in Wasanni
0
Jan Aikin Da Ke Gaban Sababbin Shugabannin Kano Pillars
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A cikin wannan satin ne gwamnatin Jihar Kano karkashin jagorancin Abba Kabir Yusuf ta bayyana sababbin shugabannin kungiyar kwallon kafa ta Kano Pillars, kwanaki kadan bayan kwamishinan matasa da wasanni, Mustapha Rabiu Kwankwaso, ya soke tsohon shugabancin kungiyar karkashin shugabancin Babangida Little saboda wasu dalilai.

Sai dai masoya kungiyar ta Pillars, wadda ake kira “MASU GIDA” sun ji dadin matakin da gwamnatin ta dauka na rushe wancan jagorancin sakamakon rashin tabuka abin arziki a kakar da aka kammala, inda kungiyar ta kare a mataki na 11 da kuma daukar sabon mai koyarwa, Paul Offor, wanda magoya bayan kungiyar suke ganin bai cancanta ba.

  • Wakilin CMG Ya Zanta Da Shugaban Kasar Timor-Leste
  • Kudurin Jam’iyyar Kwaminis Ta Kasar Sin Ya Shafi Manyan Tsare-Tsare Tare Da Matakai Na Zahiri

Sababbin shugabannin kungiyar, karkashin shugabancin Aliyu Nayara Mai Samba, da mambobinsa da suka hada da Salisu Muhammad Kosawa da Yusuf Danladi Andy Cole da Muhammad Usman da Ahmad Musbahu da Umar Umar Dankura da Rabiu Abdullahi da Nasiru Bello da Muhammad Danjuma Gwarzo da Mustapha Usman Darma da Muhammad Ibrahim (Hassan West) da Injiya Usman K/Naisa su ne za su jagoranci kungiyar sai kuma Abubakar Isa Dandago.

Jami’in yada labarai da kuma Ismail Abba Tangalash, a matsayin mataimakin Jami’in yada labarai.

Wadanne kalubale ne a gaban sababbin shugabannin?

Labarai Masu Nasaba

Abinda Ya Kamata Kusani Akan Wasan El Classico Na Yau

Barin Liverpool Ita Ce Shawara Mafi Wahala Da Na Taɓa Yankewa A Rayuwata -Alexander 

Sabon mai koyarwa

A daren ranar Talata ne sabon shugabancin na Kano Pillars ya tabbatar da korar kociyan kungiyar, Paul Offor, wanda tsohon shugabancin kungiyar ya dauka kwanakin baya, wanda kuma wasu rahotanni sun nuna cewa wannan dalilin na daukar kocin yana daya daga cikin dalilan korar tsohon shugabancin.

Yanzu abin da yake gaban shugabancin kungiyar shi ne tabbatar da ganin an dauki sabon mai koyarwar da zai kawo canji sannan kuma wanda ya cancanta saboda Kano Pillars daya ce daga cikin manyan kungiyoyi a kasar nan, sabode haka suna bukatar kwaarrren mai koyarwa.

Gyara Halayyar Magoya Baya

Wasu suna ganin halayyar magoya bayan kungiyar tana daya daga cikin dalilan da suke sanyawa kungiyar take tsintar kanta a wani halin na rashin kokari saboda rashin hakuri da kuma daukar mataki na jifa ga alkalan wasa da abokan karawa da magoya bayan kungiyar suke yi.

A lokuta da dama an ga yadda kwamitin ladaftarwa na hukumar da ke kula da gasar firimiya ta kasa ke dakatar da magoya baya shiga Kallon wasa ko dauke Kano Pillars din daga Jihar Kano zuwa wata jihar ko kwashe mata maki saboda halayyar magoya baya kuma hakan babbar barazana ce ga kokarin kungiyar.

Sabon shugabancin kungiyar yana bukatar bita domin a nusar da su hakkin magoya baya da kuma rawar da za su iya takawa wajen ganin kungiyar ta samu ci gaba ta hanyar goyon bayan kungiyar ta hanyar da ta da ce.

Sannan akwai bukatar a fitar da wani tsari ga magoya baya wanda wannan alhakin shugabancin magoya bayan kungiyar ne, idan aka samu tsari mai kyau magoya baya kadai za su dinga samar da kudin shiga wanda za a dinga anfani da shi wajen toshe wata matsalar ta kudi.

Gyara Yadda Ake Daukar ‘Yan Wasa

Abu ne sananne a kungiyar kwallon kafa ta Kano Pillars, salon yadda ake daukar ‘yan wasa a kungiyar yana bukatar gyara da kuma sanya ido tare da nuna kwarewa. Kamar yadda rahotanni suka bayyana, da yawa daga cikin ‘yan wasan kungiyar da suka buga kakar wasan da ta gabata sun tafi, sun koma wasu daga cikin abokan hamayyar Kano Pillars wanda hakan yana nufin akwai bukatar a kawo wasu domin cike gurbinsu.

Sai dai ba kawai kawo wasu ‘yan wasan ba ne mafita, akwai bukatar yin tsari wajen daukar ‘yan wasan kamar yadda yake a tsare kuma zai kasance kungiyar za ta samu riba idan har an tashi sayar da dan wasa zuwa wata kungiyar a nan gida Nigeria ko kuma kasashen waje.

Tsarin daukar dan wasa ta hannun wakilinsa, wato (Agent) a turance yana da illa sosai domin dan wasa yana iya barin kungiya a duk lokacin da ya ga wata dama ta zo masa saboda ba kwantiragi aka shiga da shi ba kamar

yadda yake a tsare.

Da yawa daga cikin wakilan ‘yan wasa sun yi amfani da Kano Pillars wajen tallata ‘yan wasansu a gasar firimiya da ma kasashen waje kuma idan dama ta samu sai su dauke ‘yan wasan su tafi tun da babu wata yarjejeniya da aka kulla ta adadin wasu shekaru ko watanni.

Aikin da yake gaban sabon shugabancin Kano Pillars a yanzu a kan maganar daukar sababbin ‘yan wasa shi ne dole ne a kaucewa hanyar dodorido da yin ungulu da kan zabo ga kungiyar domin samun ci gaban da ake abukata.

Biyan ‘yan wasa hakkokinsu

Hakkokin ‘yan wasa su ne muhimman abubuwan da shugabancin ya kamata ya kalla, domin biyan dan wasa albashi da ragowar hakkokinsa yana daya daga cikin abubuwan da suke karawa ‘yan wasa kwarin gwiwa domin su dage su yi abin da ya kamata.

Sai dai tuni gwamnatin Kano ta yi alkawarin biyan ‘yan wasan hakkokinsu wanda hakan yake nufin nan gaba kadan abubuwa za su gyaru a kungiyar.

Hanyoyin Samun Kudin Shiga

Kano Pillars kungiya ce da ta karkashin gwamnatin jiha kuma ana biyansu albashi ne kamar yadda gwamnati take biyan albashi ga ma’aikatanta, kasancewar wasan kwallon kafa yana da farin jini da kuma kasancewar kungiyar a Jihar Kano take, akwai bukatar sabon shugabancin ya samar da wani tsari wanda zai kawo hanyoyin shigowar kudi kungiyar ta hanyar neman kwararru su samar da yanayin da za a samu kudin shiga da

kuma kafa kwamiti mai karfi wajen neman talla ta hanyar tuntubar ‘yan kasuwa da kamfanoni.

Yada labarai

Wannan shi ne bangaren da za a iya cewa tuni ya fara aiki kai tsaye kuma aka fara gani da ido daga fara aikin sabon shugabancin kungiyar, duk da cewa ba abin mamaki bane kasancewar wadanda suke da alhakin wannan fanni na yada labarai daman kwararru ne a bangaren.

Abubakar Isa Dandago da Isma’il Abba Tangalashi sun yi suna wajen bayar da labaran wasanni, sannan ba iya bayar da labarin ba, salon bayar da labarin da kwarewar da suke da ita ce ya sa suka kasance cikin kunshin shugabancin Kano Pillars. Tuni bangaren yada labarai ya fara aikinsa ta hanyar fitar da sanarwa irin yadda manyan kungiyoyi suke yi tare kuma da bude shafukan sada zumunta domin isar da sako da magoya bayan kungiyar kai tsaye, hakan kuma zai taimaka wajen wayar da kan magoya baya a nan gaba domin ta kafar yada labarai ne kawai magoya baya za su dinga sanin halin da kungiyar take ciki da kuma rawar da suma za su dinga takawa wajen ba wa kungiyar goyon baya a tsare ba tare da kaucewa doka ba.

Tuni dai aka fara ganin canji a fannin yada labarai kuma hakan yana nufin nan gaba kadan kungiyar za ta fara samun kudin shiga ta hanyar shafukan sada zumunta. Idan har bangaren yada labarai za su dage wajen samar da labarai na hoto da bidiyo da sauran hanyoyin yadda manyan kungiyoyi na duniya suke yi na mayar da hankali a kan kafofin yada labarai na zamani ana sakawa a shafukan sada zumuntar kungiyar hakan zai kawo canji sosai kuma za a tabbatar da cewa an saka kwarya a gurbinta.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AikiGyarakanoKungiyaKwalloPillars
ShareTweetSendShare
Previous Post

Mummunan Tasirin Da Kuncin Rayuwa Ke Yi Ga Al’umma Wajen Bin Addini

Next Post

Akwai Raɗaɗi Da Zafi Kan Cire Tallafin Man Fetur Amma Ya Zama Dole – Tinubu Ga masu Zanga-zangar 

Related

Abinda Ya Kamata Kusani Akan Wasan El Classico Na Yau
Wasanni

Abinda Ya Kamata Kusani Akan Wasan El Classico Na Yau

2 days ago
Barin Liverpool Ita Ce Shawara Mafi Wahala Da Na Taɓa Yankewa A Rayuwata -Alexander 
Wasanni

Barin Liverpool Ita Ce Shawara Mafi Wahala Da Na Taɓa Yankewa A Rayuwata -Alexander 

2 days ago
Man Utd Ta Lallasa Bilbao, Ta Kai Wasan Ƙarshe Na Gasar Europa
Manyan Labarai

Man Utd Ta Lallasa Bilbao, Ta Kai Wasan Ƙarshe Na Gasar Europa

5 days ago
Zamalek Ta Sallami Tsohon Kocin Super Eagles, Peseiro
Wasanni

Zamalek Ta Sallami Tsohon Kocin Super Eagles, Peseiro

5 days ago
PSG Ta Yi Waje Rod Da Arsenal A Gasar Zakarun Turai 
Wasanni

PSG Ta Yi Waje Rod Da Arsenal A Gasar Zakarun Turai 

6 days ago
UEFA: Inter Milan Ta Yi Wa Barcelona Kancal
Wasanni

UEFA: An Kai Ruwa Rana Yayin Da Inter Ta Koro Barcelona Gida

7 days ago
Next Post
Akwai Raɗaɗi Da Zafi Kan Cire Tallafin Man Fetur Amma Ya Zama Dole – Tinubu Ga masu Zanga-zangar 

Akwai Raɗaɗi Da Zafi Kan Cire Tallafin Man Fetur Amma Ya Zama Dole - Tinubu Ga masu Zanga-zangar 

LABARAI MASU NASABA

An Nuna Fasahar Waken Pingtan Na Kasar Sin A Najeriya

An Nuna Fasahar Waken Pingtan Na Kasar Sin A Najeriya

May 13, 2025
Gwamna Zamfara Ya Raba Katin ATM Ga Mutane 400,000 Da Suka Ci Gajiyar Shirin ‘Cash Transfer’ A Jihar

Gwamna Zamfara Ya Raba Katin ATM Ga Mutane 400,000 Da Suka Ci Gajiyar Shirin ‘Cash Transfer’ A Jihar

May 13, 2025
Xi Jinping Ya Halarci Bikin Bude Taro Na 4 Na Ministocin Dandalin CCF 

Xi Jinping Ya Halarci Bikin Bude Taro Na 4 Na Ministocin Dandalin CCF 

May 13, 2025
Kasar Sin Ta Fitar Da Tambarin Cika Shekaru 80 Da Samun Nasarar Murkushe Harin Japan

Kasar Sin Ta Fitar Da Tambarin Cika Shekaru 80 Da Samun Nasarar Murkushe Harin Japan

May 13, 2025
Wata Mata Ta Kashe Dan Hayar Da Ke Gidanta A Ondo

‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban APC A Ondo, Sun Nemi N100m

May 13, 2025
Rikicin Ribas: Fubara Ya Ce Ya San Yadda Zai Magance Matsalar, Ya Gargaɗi Magoya Bayansa

Rikicin Ribas: Fubara Ya Ce Ya San Yadda Zai Magance Matsalar, Ya Gargaɗi Magoya Bayansa

May 13, 2025
Jami’ar Maryam Abacha Ta Rufe Ɗakunan Kwanan Ɗalibai Saboda Aikata Rashin Ɗa’a A Kano

Jami’ar Maryam Abacha Ta Rufe Ɗakunan Kwanan Ɗalibai Saboda Aikata Rashin Ɗa’a A Kano

May 13, 2025
China Da Amurka Sun Yarda Da Rage Harajin Kayayyakinsu Domin Sasanta Rikicin Kasuwanci

China Da Amurka Sun Yarda Da Rage Harajin Kayayyakinsu Domin Sasanta Rikicin Kasuwanci

May 13, 2025
Boko Haram Sun Kashe Mutum 12 A Wani Sabon Hari A Borno

Bam Ya Hallaka Ma’aikatan Hukumar Ilimi 2 A Hanyar Damboa-Maiduguri

May 13, 2025
Wike Ya Gargaɗi PDP Kan Bai Wa Ɗan Arewa Takara A 2027

Wike Ya Gargaɗi PDP Kan Bai Wa Ɗan Arewa Takara A 2027

May 13, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.