ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, July 10, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Akwai Raɗaɗi Da Zafi Kan Cire Tallafin Man Fetur Amma Ya Zama Dole – Tinubu Ga masu Zanga-zangar 

by Sulaiman
2 years ago
Tinubu

LABARAI MASU NASABA

An Ceto Dukkanin Ɗalibai Da Malaman Da Aka Sace A Jihar Oyo — Fadar Shugaban Ƙasa

Xi Ya Zanta Da Shugabar Namibia

Sabanin bukatun masu zanga-zangar #EndBadGovernance da ke ci gaba da gudana, Shugaba Bola Tinubu ya ce, ba zai yi wu ba a maido da biyan tallafin man fetur.
Shugaban kasar a wani jawabi da ya yi wa ‘yan Nijeriya a safiyar ranar Lahadi, ya bayyana cewa, duk da cewa matakin cire tallafin man fetur ya haifar da tsanani da kuncin rayuwa, amma hakan ya zama dole domin biyan tallafin ba ya haifar da alkairi ga tattalin arzikin kasarmu sai dai kawo cikas ga ci gaban tattalin arzikinmu da ci gabanmu.”
  • Jan Aikin Da Ke Gaban Sababbin Shugabannin Kano Pillars
  • Mummunan Tasirin Da Kuncin Rayuwa Ke Yi Ga Al’umma Wajen Bin Addini
Shugaban ya kuma shaida wa masu zanga-zangar cewa, jami’an tsaro za su ci gaba da tabbatar da cikakken tsaron rayuka da dukiyoyin ‘yan kasa ta hanyar da ta dace, inda ya kara da cewa, “Dimokuradiyyarmu tana ci gaba ne idan aka mutunta da kuma kare hakkokin da tsarin mulki ya ba kowane dan Nijeriya.
Shugaba Tinubu ya bayyana cewa, “Manufar da nake da ita game da kasarmu, ita ce, a samu kasa mai adalci da wadata, inda kowane mutum zai ci moriyar zaman lafiya, ’yanci, da rayuwa mai arha wacce ba tsada wanda shugabanci nagari na dimokuradiyya ne kadai zai iya samar da ita – shugabanci irin na Dimokuradiyya a bayyane yake, da gaskiya da rikon amana ga al’ummar Nijeriya.
“Tsawon shekaru da yawa, tattalin arzikinmu ya kasance mai rauni, kuma mara karsashi, saboda rashin daidaituwa da yawa da suka kawo cikas ga ci gabanmu. Sama da shekara guda da ta wuce, kasarmu Nijeriya, ta kai matsayin da ba za mu iya ci gaba da yin amfani da hanyoyin magance matsalolin wucin gadi don magance matsalolin da dole mu kawo karshensu ba, domin kanmu da kuma zuriyarmu masu zuwa daga baya.
“Saboda haka na dauki matsaya mai raɗaɗi wacce ta zama dole na cire tallafin man fetur da kuma kawar da tsarin musayar kuɗi da yawa wacce ke haifar da rudani da cikas ga ci gaban tattalin arzikinmu da ci gabanmu.”

“Wadannan shawarwarin da na yanke sun zama dole idan har muna so mu ceto tattalin arzikin kasarmu daga durkushewa. Eh, na yarda, kuɗin kasa yana tsayawa akan teburi na. Amma ina tabbatar muku cewa, na mayar da hankali sosai wajen jagoranci nagari ga jama’a” In ji Tinubu

Tinubu
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Xi Ya Zanta Da Shugabar Namibia
  • Sulaiman
    “Kashin Baya” Na Sin Ya Zama Abun Dogara Ga Kasashen Afirka
  • Sulaiman
    Shugaba Xi Ya Gana Da Firaministan Koriya Ta Arewa A Beijing
  • Sulaiman
    Shugaban Miyetti Allah, Bodejo Ya Karyata Zargin Halatta Kudin Haram A Zaman Kotu
ADVERTISEMENT

MASU ALAKA

An Ceto Dukkanin Ɗalibai Da Malaman Da Aka Sace A Jihar Oyo — Fadar Shugaban Ƙasa
Manyan Labarai

An Ceto Dukkanin Ɗalibai Da Malaman Da Aka Sace A Jihar Oyo — Fadar Shugaban Ƙasa

July 10, 2026
Xi Ya Zanta Da Shugabar Namibia
Labarai

Xi Ya Zanta Da Shugabar Namibia

July 10, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya
Labarai

Ko Ka San Dalilin Da Ya Sa Chana Da Indiya Ba Sa Buga Kofin Duniya?

July 10, 2026
Next Post
Yaki A Hukumance Da Matatar Dangote Da `Yan Nijeriya

Yaki A Hukumance Da Matatar Dangote Da `Yan Nijeriya

LABARAI MASU NASABA

An Ceto Dukkanin Ɗalibai Da Malaman Da Aka Sace A Jihar Oyo — Fadar Shugaban Ƙasa

An Ceto Dukkanin Ɗalibai Da Malaman Da Aka Sace A Jihar Oyo — Fadar Shugaban Ƙasa

July 10, 2026
Xi Ya Zanta Da Shugabar Namibia

Xi Ya Zanta Da Shugabar Namibia

July 10, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya

Ko Ka San Dalilin Da Ya Sa Chana Da Indiya Ba Sa Buga Kofin Duniya?

July 10, 2026
“Kashin Baya” Na Sin Ya Zama Abun Dogara Ga Kasashen Afirka

“Kashin Baya” Na Sin Ya Zama Abun Dogara Ga Kasashen Afirka

July 10, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya

Sana’ar Ɗinki: Yadda Telolin Zariya Suka Yi Fice A Sassan Afirka

July 10, 2026
Shugaba Xi Ya Gana Da Firaministan Koriya Ta Arewa A Beijing

Shugaba Xi Ya Gana Da Firaministan Koriya Ta Arewa A Beijing

July 10, 2026
Kofin Duniya: Na fi Son Faransa Ta Kara Da Argentina A Wasan Ƙarshe A Kan Ingila — Vieira

Kofin Duniya: Na fi Son Faransa Ta Kara Da Argentina A Wasan Ƙarshe A Kan Ingila — Vieira

July 10, 2026
Sojoji Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga A Wani Ƙauyen Katsina

Sojoji Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga A Wani Ƙauyen Katsina

July 10, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya

Ibrahim Aliyu Na Ci Gaba Da Rasa Tasiri A Harkar Fili Da Gidaje A Yankin Abuja

July 10, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya

Fafutukar Neman Sabon Sakataren Majalisar Ɗinkin Duniya

July 10, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.