ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Akwai Raɗaɗi Da Zafi Kan Cire Tallafin Man Fetur Amma Ya Zama Dole – Tinubu Ga masu Zanga-zangar 

by Sulaiman
2 years ago
Tinubu

LABARAI MASU NASABA

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

Sabanin bukatun masu zanga-zangar #EndBadGovernance da ke ci gaba da gudana, Shugaba Bola Tinubu ya ce, ba zai yi wu ba a maido da biyan tallafin man fetur.
Shugaban kasar a wani jawabi da ya yi wa ‘yan Nijeriya a safiyar ranar Lahadi, ya bayyana cewa, duk da cewa matakin cire tallafin man fetur ya haifar da tsanani da kuncin rayuwa, amma hakan ya zama dole domin biyan tallafin ba ya haifar da alkairi ga tattalin arzikin kasarmu sai dai kawo cikas ga ci gaban tattalin arzikinmu da ci gabanmu.”
  • Jan Aikin Da Ke Gaban Sababbin Shugabannin Kano Pillars
  • Mummunan Tasirin Da Kuncin Rayuwa Ke Yi Ga Al’umma Wajen Bin Addini
Shugaban ya kuma shaida wa masu zanga-zangar cewa, jami’an tsaro za su ci gaba da tabbatar da cikakken tsaron rayuka da dukiyoyin ‘yan kasa ta hanyar da ta dace, inda ya kara da cewa, “Dimokuradiyyarmu tana ci gaba ne idan aka mutunta da kuma kare hakkokin da tsarin mulki ya ba kowane dan Nijeriya.
Shugaba Tinubu ya bayyana cewa, “Manufar da nake da ita game da kasarmu, ita ce, a samu kasa mai adalci da wadata, inda kowane mutum zai ci moriyar zaman lafiya, ’yanci, da rayuwa mai arha wacce ba tsada wanda shugabanci nagari na dimokuradiyya ne kadai zai iya samar da ita – shugabanci irin na Dimokuradiyya a bayyane yake, da gaskiya da rikon amana ga al’ummar Nijeriya.
“Tsawon shekaru da yawa, tattalin arzikinmu ya kasance mai rauni, kuma mara karsashi, saboda rashin daidaituwa da yawa da suka kawo cikas ga ci gabanmu. Sama da shekara guda da ta wuce, kasarmu Nijeriya, ta kai matsayin da ba za mu iya ci gaba da yin amfani da hanyoyin magance matsalolin wucin gadi don magance matsalolin da dole mu kawo karshensu ba, domin kanmu da kuma zuriyarmu masu zuwa daga baya.
“Saboda haka na dauki matsaya mai raɗaɗi wacce ta zama dole na cire tallafin man fetur da kuma kawar da tsarin musayar kuɗi da yawa wacce ke haifar da rudani da cikas ga ci gaban tattalin arzikinmu da ci gabanmu.”

“Wadannan shawarwarin da na yanke sun zama dole idan har muna so mu ceto tattalin arzikin kasarmu daga durkushewa. Eh, na yarda, kuɗin kasa yana tsayawa akan teburi na. Amma ina tabbatar muku cewa, na mayar da hankali sosai wajen jagoranci nagari ga jama’a” In ji Tinubu

Tinubu
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi
  • Sulaiman
    Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara
  • Sulaiman
    Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5
  • Sulaiman
    Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana
ADVERTISEMENT

MASU ALAKA

Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja
Labarai

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji
Manyan Labarai

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
'Yan Bindiga
Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Next Post
Yaki A Hukumance Da Matatar Dangote Da `Yan Nijeriya

Yaki A Hukumance Da Matatar Dangote Da `Yan Nijeriya

LABARAI MASU NASABA

Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.