• English
  • Business News
Wednesday, May 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Jan Kafar Tinubu Na Cire Harajin Shigo Da Abinci Na Ci Gaba Da Ta’azzara rayuwa

by Sulaiman and Khalid Idris Doya
8 months ago
in Labarai
0
abinci
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnatin tarayya a karkashin Shugaba Bola Ahmed ta ci gaba da jan kafa wajen aiwatar da afuwar harajin shigo da wasu zababbun kayayyakin abinci tun watannin baya da ta sanar da cewa za ta yi hakan.

Kayan abincin da ya kamata a ce an samu damar shigo da su ba tare wani haraji ko haramcin shigo da su ba, sun hada da shinkafa, dawa, masara, alkama, wake, hatsi, gero na tsawon kwanaki 150 daga ranar 15 ga watan Yuli zuwa 31 ga watan Disamban 2024.

  • Jerin Kasurguman ‘Yan Bindiga Da Sojoji Suka Hallaka A Arewa 
  • Jarumai A Masana’antar Kannywood Sun Jajanta Wa Wadanda Ambaliyar Ruwa Ta Shafa A Maiduguri

Ministan kudi, Wale Edun shi ne ya sanar da janye harajin shigo da kayan abincin da dage takunkumin shigo da su a watan Yuni a wani yunkurin gwamnati Tinubu na kawo saukin kayan abinci da rage matsin rayuwa da ake fuskanta.

A watan Yuli na 2024, Kwanturola Janar na Hukumar Kwastam, Bashir Adewale Adeniyi, ya tabbatar da aniyar gwamnati na aiwatar da umarnin janye takunkumin shigo da kayan abincin.

Rahotonni sun ce duk da rahotan hukumar kididdiga (NBS) na watan Yuli da Agusta da suka nuna cewa hauhawar farashin ya kasance daga kaso 39.53 da kaso 37.52 cikin 100, tsadar kayan abinci a kasuwanni na nan a kan tsadarsa sai ma abun da ya karu.

Labarai Masu Nasaba

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Bunƙasa, Amma Farashin Kayayyaki Na Ci Gaba Da Tashi – Bankin Duniya

‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 239, Sun Ƙwato Makamai Da Alburusai A Kogi

A wani ziyarar kasuwanni da aka gudanar a ranar Litinin, ya nuna cewa buhun shinkafar mai nauyin kilogram 50 ya kan kasance daga naira 87,000 zuwa naira 106,000. Buhun wake 50kg kuwa ana sayar da shi ne kan naira 65,000 zuwa naira 100,000. ‘Yan Nijeriya da dama ba su iya samun damar cin abinci sau uku a rana, inda suka rage yawan cin abinci sakamakon tsadar rayuwa duk kuwa da cewa an janye harajin shigo da wasu kayan abinci.

Da yake magana kan wannan lamarin a ranar Litinin, babban daraktan cibiyar inganta harkokin ‘yan kasuwa masu zaman kansu (CPPE), Muda Yusuf, ya ce, babban matsalar da ke janyo tsadar kayan abincin shi ne, jan kafar aiwatar da cire harajin shigo da kayan abincin.

A cewarsa, akwai babbar matsala tsakanin sanar da wani shiri da aiwatar da shiri a wannan gwamnati, wanda kuma bai kamata ake samun irin wannan matsalar ba.

Ya tabbatar da cewa daga kafa ga shigo da kayayyakin abincin bai samu aiwatarwa yadda ya dace ba, don haka ne ake samun karin matsala ga tattalin arziki na kasar.

Yusuf ya bukaci gwamnati ta tashi tsaye ta aiwatar da wannan shirin nata domin a samu saukin matsin rayuwa da tsadar kayayyakin abinci da jama’a ke fuskanta a halin yanzun.

Shi ma nasa bangaren, Olufemi Kayode, mamba a kungiyar samar da lasisi na kwastam a Nijeriya (ANLCA), ya ce, har yanzu babu cikakken tsarin janye harajin shigo da kayayyakin.

Ya nuna cewa akwai matsala a tsakanin tsarin sanarwar janyewar da kuma manufar aiwatar da shirin daga wajen kwastam. Don haka ne ya nuna cewa akwai bukatar daga ma’aikatar kudi da kwastam da su samar da manufa ta yadda za a aiwatar da janye harajin domin shigo da kayayyakin ba tare da wani kalubale ba.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Kamshin Jiki Da Cikar Hankalin Manzon Allah (SAW)

Next Post

Nijeriya Na Bukatar Kujeran Dindindin A Kwamitin Tsaro Na MDD – Ministan Tsaro

Related

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Bunƙasa, Amma Farashin Kayayyaki Na Ci Gaba Da Tashi – Bankin Duniya
Manyan Labarai

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Bunƙasa, Amma Farashin Kayayyaki Na Ci Gaba Da Tashi – Bankin Duniya

1 hour ago
‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 239, Sun Ƙwato Makamai Da Alburusai A Kogi
Labarai

‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 239, Sun Ƙwato Makamai Da Alburusai A Kogi

3 hours ago
Dakarun Soji Sun Daƙile Wani Sabon Harin ISWAP A Dikwa
Labarai

Dakarun Soji Sun Daƙile Wani Sabon Harin ISWAP A Dikwa

4 hours ago
Sojoji 20 Sun Ɓace Bayan Harin Da ISWAP Suka Kai Marte
Manyan Labarai

Sojoji 20 Sun Ɓace Bayan Harin Da ISWAP Suka Kai Marte

5 hours ago
Ko Kanawa Za Su Yafe Wa Ganduje?
Manyan Labarai

Kotu Ta Ce Za A Ci Gaba Da Shari’ar Ganduje Kan Zargin Aikata Rashawa A Kano

6 hours ago
Tsaro: Gwamna Lawal Ya Raba Motoci 140 Ga Jami’an Tsaro A Zamfara 
Labarai

Tsaro: Gwamna Lawal Ya Raba Motoci 140 Ga Jami’an Tsaro A Zamfara 

15 hours ago
Next Post
Ministan Tsaro

Nijeriya Na Bukatar Kujeran Dindindin A Kwamitin Tsaro Na MDD – Ministan Tsaro

LABARAI MASU NASABA

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Bunƙasa, Amma Farashin Kayayyaki Na Ci Gaba Da Tashi – Bankin Duniya

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Bunƙasa, Amma Farashin Kayayyaki Na Ci Gaba Da Tashi – Bankin Duniya

May 14, 2025
Sin Ta Daidaita Harajin Fito Kan Hajojin Amurka Da Ake Shigarwa Kasar

Sin Ta Daidaita Harajin Fito Kan Hajojin Amurka Da Ake Shigarwa Kasar

May 14, 2025
Amurka Da Saudiyya Sun Ƙulla Yarjejeniyar Dala Biliyan 600 Kan Tsaro, Makamashi Da Fasaha

Amurka Da Saudiyya Sun Ƙulla Yarjejeniyar Dala Biliyan 600 Kan Tsaro, Makamashi Da Fasaha

May 14, 2025
Peng Liyuan Da Uwar Gidan Shugaban Kasar Brazil Sun Ziyarci Babban Zauren Nuna Fasahohin Nishadantarwa Ta Kasar Sin

Peng Liyuan Da Uwar Gidan Shugaban Kasar Brazil Sun Ziyarci Babban Zauren Nuna Fasahohin Nishadantarwa Ta Kasar Sin

May 14, 2025
‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 239, Sun Ƙwato Makamai Da Alburusai A Kogi

‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 239, Sun Ƙwato Makamai Da Alburusai A Kogi

May 14, 2025
Dakarun Soji Sun Daƙile Wani Sabon Harin ISWAP A Dikwa

Dakarun Soji Sun Daƙile Wani Sabon Harin ISWAP A Dikwa

May 14, 2025
Sojoji 20 Sun Ɓace Bayan Harin Da ISWAP Suka Kai Marte

Sojoji 20 Sun Ɓace Bayan Harin Da ISWAP Suka Kai Marte

May 14, 2025
Ko Kanawa Za Su Yafe Wa Ganduje?

Kotu Ta Ce Za A Ci Gaba Da Shari’ar Ganduje Kan Zargin Aikata Rashawa A Kano

May 14, 2025
Binciken Jin Ra’ayoyi Na CGTN: Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ta Ce Harajin Fentanyl Ya Gurgunta Hadin Gwiwar Amurka Da Sin Kuma Fiye Da Kashi 90% Na Jama’a Sun Koka Da “Jarabar” Amurka Ta Cin Zarafi

Binciken Jin Ra’ayoyi Na CGTN: Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ta Ce Harajin Fentanyl Ya Gurgunta Hadin Gwiwar Amurka Da Sin Kuma Fiye Da Kashi 90% Na Jama’a Sun Koka Da “Jarabar” Amurka Ta Cin Zarafi

May 13, 2025
Tsaro: Gwamna Lawal Ya Raba Motoci 140 Ga Jami’an Tsaro A Zamfara 

Tsaro: Gwamna Lawal Ya Raba Motoci 140 Ga Jami’an Tsaro A Zamfara 

May 13, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.