• English
  • Business News
Sunday, July 27, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Jan Kafar Tinubu Na Cire Harajin Shigo Da Abinci Na Ci Gaba Da Ta’azzara rayuwa

by Sulaiman and Khalid Idris Doya
10 months ago
in Labarai
0
abinci
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnatin tarayya a karkashin Shugaba Bola Ahmed ta ci gaba da jan kafa wajen aiwatar da afuwar harajin shigo da wasu zababbun kayayyakin abinci tun watannin baya da ta sanar da cewa za ta yi hakan.

Kayan abincin da ya kamata a ce an samu damar shigo da su ba tare wani haraji ko haramcin shigo da su ba, sun hada da shinkafa, dawa, masara, alkama, wake, hatsi, gero na tsawon kwanaki 150 daga ranar 15 ga watan Yuli zuwa 31 ga watan Disamban 2024.

  • Jerin Kasurguman ‘Yan Bindiga Da Sojoji Suka Hallaka A Arewa 
  • Jarumai A Masana’antar Kannywood Sun Jajanta Wa Wadanda Ambaliyar Ruwa Ta Shafa A Maiduguri

Ministan kudi, Wale Edun shi ne ya sanar da janye harajin shigo da kayan abincin da dage takunkumin shigo da su a watan Yuni a wani yunkurin gwamnati Tinubu na kawo saukin kayan abinci da rage matsin rayuwa da ake fuskanta.

A watan Yuli na 2024, Kwanturola Janar na Hukumar Kwastam, Bashir Adewale Adeniyi, ya tabbatar da aniyar gwamnati na aiwatar da umarnin janye takunkumin shigo da kayan abincin.

Rahotonni sun ce duk da rahotan hukumar kididdiga (NBS) na watan Yuli da Agusta da suka nuna cewa hauhawar farashin ya kasance daga kaso 39.53 da kaso 37.52 cikin 100, tsadar kayan abinci a kasuwanni na nan a kan tsadarsa sai ma abun da ya karu.

Labarai Masu Nasaba

ADC Ce Za Ta Haɗa Kan Arewa Wajen Kawo Ci Gaba — Mark

Ƴansanda Sun Kama Masu Garkuwa Da Mutane 6 A Kaduna Da Zamfara

A wani ziyarar kasuwanni da aka gudanar a ranar Litinin, ya nuna cewa buhun shinkafar mai nauyin kilogram 50 ya kan kasance daga naira 87,000 zuwa naira 106,000. Buhun wake 50kg kuwa ana sayar da shi ne kan naira 65,000 zuwa naira 100,000. ‘Yan Nijeriya da dama ba su iya samun damar cin abinci sau uku a rana, inda suka rage yawan cin abinci sakamakon tsadar rayuwa duk kuwa da cewa an janye harajin shigo da wasu kayan abinci.

Da yake magana kan wannan lamarin a ranar Litinin, babban daraktan cibiyar inganta harkokin ‘yan kasuwa masu zaman kansu (CPPE), Muda Yusuf, ya ce, babban matsalar da ke janyo tsadar kayan abincin shi ne, jan kafar aiwatar da cire harajin shigo da kayan abincin.

A cewarsa, akwai babbar matsala tsakanin sanar da wani shiri da aiwatar da shiri a wannan gwamnati, wanda kuma bai kamata ake samun irin wannan matsalar ba.

Ya tabbatar da cewa daga kafa ga shigo da kayayyakin abincin bai samu aiwatarwa yadda ya dace ba, don haka ne ake samun karin matsala ga tattalin arziki na kasar.

Yusuf ya bukaci gwamnati ta tashi tsaye ta aiwatar da wannan shirin nata domin a samu saukin matsin rayuwa da tsadar kayayyakin abinci da jama’a ke fuskanta a halin yanzun.

Shi ma nasa bangaren, Olufemi Kayode, mamba a kungiyar samar da lasisi na kwastam a Nijeriya (ANLCA), ya ce, har yanzu babu cikakken tsarin janye harajin shigo da kayayyakin.

Ya nuna cewa akwai matsala a tsakanin tsarin sanarwar janyewar da kuma manufar aiwatar da shirin daga wajen kwastam. Don haka ne ya nuna cewa akwai bukatar daga ma’aikatar kudi da kwastam da su samar da manufa ta yadda za a aiwatar da janye harajin domin shigo da kayayyakin ba tare da wani kalubale ba.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Kamshin Jiki Da Cikar Hankalin Manzon Allah (SAW)

Next Post

Nijeriya Na Bukatar Kujeran Dindindin A Kwamitin Tsaro Na MDD – Ministan Tsaro

Related

ADC Ce Za Ta Haɗa Kan Arewa Wajen Kawo Ci Gaba — Mark
Labarai

ADC Ce Za Ta Haɗa Kan Arewa Wajen Kawo Ci Gaba — Mark

47 minutes ago
Ƴansanda Sun Kama Masu Garkuwa Da Mutane 6 A Kaduna Da Zamfara
Labarai

Ƴansanda Sun Kama Masu Garkuwa Da Mutane 6 A Kaduna Da Zamfara

4 hours ago
VON Zai Fara Watsa Shirye-Shirye Da Harshen Sinanci — Ndace
Labarai

VON Zai Fara Watsa Shirye-Shirye Da Harshen Sinanci — Ndace

5 hours ago
Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 
Wasanni

Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 

15 hours ago
Kasar Sin Na Tir Da Harin Isra’ila Kan Makarantu A Gaza Tare Da Kira Da A Dakatar Da Bude Wuta
Labarai

Isra’ila Na Sanya Alamar Rusau A Dubban Gidajen Fararen Hula A Gaza

17 hours ago
Duk Da Ni Ɗan Adawa Ne Buhari Ya Hana A Murɗe Min Zaɓe — Dickson
Siyasa

Duk Da Ni Ɗan Adawa Ne Buhari Ya Hana A Murɗe Min Zaɓe — Dickson

19 hours ago
Next Post
Ministan Tsaro

Nijeriya Na Bukatar Kujeran Dindindin A Kwamitin Tsaro Na MDD – Ministan Tsaro

LABARAI MASU NASABA

Super Falcons Zasu Samu Kyakkyawar Tarɓa Daga Gare Ni A Abuja — Tinubu

Super Falcons Zasu Samu Kyakkyawar Tarɓa Daga Gare Ni A Abuja — Tinubu

July 27, 2025
ADC Ce Za Ta Haɗa Kan Arewa Wajen Kawo Ci Gaba — Mark

ADC Ce Za Ta Haɗa Kan Arewa Wajen Kawo Ci Gaba — Mark

July 27, 2025
Hanyoyin Da Za A Bi A Rage Yawan Zawarawa

Hanyoyin Da Za A Bi A Rage Yawan Zawarawa

July 27, 2025
Ƴansanda Sun Kama Masu Garkuwa Da Mutane 6 A Kaduna Da Zamfara

Ƴansanda Sun Kama Masu Garkuwa Da Mutane 6 A Kaduna Da Zamfara

July 27, 2025
aure

Ko Kin San… Matsalolin Mahaifa Da Suke Hana Haihuwa 

July 27, 2025
VON Zai Fara Watsa Shirye-Shirye Da Harshen Sinanci — Ndace

VON Zai Fara Watsa Shirye-Shirye Da Harshen Sinanci — Ndace

July 27, 2025
Yadda Ake Faten Acca

Yadda Ake Faten Acca

July 27, 2025
Hanyoyin Gyaran Gashi

Hanyoyin Gyaran Gashi

July 27, 2025
Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 

Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 

July 26, 2025
Musuluntar Wata Ce Ya Ja Hankalina Shiga Fim – Sailuba Dadin Kowa

Musuluntar Wata Ce Ya Ja Hankalina Shiga Fim – Sailuba Dadin Kowa

July 26, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.