• English
  • Business News
Monday, June 2, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Jaridar Business Day Ta Karrama Gwamnan Gombe Kan Hidimta Wa Al’ummarsa

by Khalid Idris Doya
2 years ago
in Labarai
0
Jaridar Business Day Ta Karrama Gwamnan Gombe Kan Hidimta Wa Al’ummarsa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Jaridar ‘Business Day’ ta karrama Gwamnan Jihar Gombe, Muhammadu Inuwa Yahaya, da lambar yabo na gwamna Mafi kwazo a fagen yi wa al’ummar jiharsa hidima. 

 

An gudanar da taron Bada lambar yabon gwarazan na shekarar 2022 ne a ranar Alhamis a Abuja Continental Hotel (Sheraton Hotel and Towers) yayin da mataimakin Gwamnan, Dr. Manassah Daniel Jatau ne ya karɓi kyaututtukan a madadinsa.

  • Tsare-Tsare Ga Ma’aikata: Gwamnonin Bauchi Da Gombe Sun Samu Babbar Lambar Yabo Daga Kungiyar Kwadago Ta TUC

Sauran fitattun mutanen da suka samu lambar yabo a bikin sun hada da Gwamnan Jihar Edo Godwin Obaseki, da Ministan Kwadago da Tallafi Chris Ngige, da Babban Daraktan Hukumar Bunmasa Fasahar Sadarwa ta Kasa NITDA, Kashifu Inuwa da dai sauransu.

 

Labarai Masu Nasaba

Tsohon Minista Ya Fice Daga Jam’iyyar APC A Nasarawa

Sanatocin Arewa Sun Yi Jimamin Rasuwar ‘Yan Wasan Kano

Mawallafi kuma shugaban kamfanin ‘Business Day Media’, Mr Frank Aigbogun, ya ce an shirya taron ne don karfafa gwiwar shugabanni a matakin jihohi su rungumi al’adar aiki tukuru, da samar da ribar demokradiyya ga al’umma.

 

A cewarsa, Gwamna Muhammadu Inuwa Yahaya ya fafata ne da wasu gwamnoni a bangarori daban-daban, kuma jihar sa ta zama zakara wacce tafi kowace jiha a fagen saukaka harkokin kasuwanci, kuma jihar da ta fi inganta yankunan karkara da birane.

 

“An cimma hakan ne bayan da kwamitin bada lambar yabon wanda ya kunshi fitattun mutane ya tattara bayanan da suka dace kai tsaye, da kuma nazarin sauran bayanan da aka tattara daga ɓangarori daban-daban na tattalin arziki da zamantakewa.

Business day

“Mun ga ci gaba sosai a Jihar Gombe tun bayan hawan Gwamna Inuwa Yahaya, mun ji irin nasarorin da ya samu a fannin kiwon lafiya, da samar da ababen more rayuwa, da raya karkara da zuba jari. A ‘yan kwanaki kadan da suka gabata mun ga yadda jihar sa ta samu matsayi na daya a fagen saukala harkokin da harkokin kasuwanci.

 

“Hakan bai zo mana da mamaki ba ganin yadda gwamnan yake ta lashe lambobin yabon da mukan bayar a kai a kai bayan shirya gasa, muna taya mai girma gwamna murna kuma muna kara masa kwarin guiwa kan ya ci gaba da irin wannan kokari nasa”.

 

Da yake karbar lambar yabon a madadin Gwamna Inuwa, Mataimakin nasa Dakta Manassah Daniel Jatau, ya bayyana karramawar a matsayin kalubalen da zai zaburar da shi wajen kara jajircewa kan aikin da ya saba.

 

Sai ya yaba wa kafar yada labaran bisa wannar karramawa ta aiki tukuru da nagarta a harkokin mulki.

 

“Zan fara da yaba wa Mawallafin wannar jarida ta Business Day bisa wannan karramawa da lambar yabo. Wannan wani aiki ne mai matukar muhimmanci da kuka yi. A makon daya gabatan nan muka samu lambar yabo a matsayin jiha mafi fice a fagen saukaka kasuwanci da kuma wani a matsayin gwamnati mafi haba-haba da ma’aikata, daga kungiyar Kwadago ta kasa TUC, kuma a yau ma ga shi muna sake samun wata lambar yabon na gwamnati mafi kwazo a fagen yiwa al’ummar ta hidima”.

 

“A gare mu, samun lambar yabo wani kalubale ne, nauyi ne da kuma tsammanin cewa za mu yi fiye da haka. Bisa tsari na fahimta, babu wanda zai iya yin komai shi kadai. Muna godiya da gudunmawar da kowa ke bayarwa a Jihar Gombe, musamman wadanda suka bada gudunmawa wajen samun wannar lambar yabo. Don haka mun sadaukar da wannar lambar yabo ga dokacin al’ummar jihar bisa irin gudunmawar da suka bayar wajen samun nasarar gwamnatin mu”.

 

“Ina gayyatar ku zuwa Jihar Gombe don ku ganewa idon ku cibiyar masana’antu ta Muhammadu Buhari mai girman kadada 1000, inda muka samar da duk abin da ake bukata da suka hada da wutar lantarki daga madatsar ruwa ta Dadinkowa, da ayyukan more rayuwa na zamani da abubuwan jin dadin jama’a da kuma zaman lafiya domin kasuwanci ya bunkasa. Ina kuma gayyatar ku da ku zo ku zuba jari a Jihar Gombe, muna da kyakkyawan yanayi na kasuwanci”.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

FIFA Ta Yi Barazanar Kin Haska Kofin Duniya Na Mata A Wasu Kasashen

Next Post

Shugaban Kasar Sin Da Uwargidansa Sun Taya Sarki Charles Na III Da Sarauniya Camilla Murnar Nadin Da Aka Yi Musu A Hukumance

Related

Tsohon Minista Ya Fice Daga Jam’iyyar APC A Nasarawa
Labarai

Tsohon Minista Ya Fice Daga Jam’iyyar APC A Nasarawa

2 hours ago
Sanatocin Arewa Sun Yi Jimamin Rasuwar ‘Yan Wasan Kano
Labarai

Sanatocin Arewa Sun Yi Jimamin Rasuwar ‘Yan Wasan Kano

6 hours ago
Gwamnatin Kano Ta Ba Da Hutun Makaranta Domin Bukukuwan Sallah
Ilimi

Gwamnatin Kano Ta Ba Da Hutun Makaranta Domin Bukukuwan Sallah

7 hours ago
bakin wake
Labarai

Bam Ya Kashe Mutane 9 A Wata Tashar Motoci Da Ke Borno 

9 hours ago
NDLEA Ta Cafke Masu Tura Alhazai Saudiyya Domin Safarar Hodar Iblis Zuwa Kasar
Labarai

NDLEA Ta Cafke Masu Tura Alhazai Saudiyya Domin Safarar Hodar Iblis Zuwa Kasar

12 hours ago
Gwamnan kano
Manyan Labarai

Gwamna Yusuf Ya Bada Hutu A Ranar Litinin Domin Addu’o’i Ga ‘Yan Wasan Kano 22

13 hours ago
Next Post
Shugaban Kasar Sin Da Uwargidansa Sun Taya Sarki Charles Na III Da Sarauniya Camilla Murnar Nadin Da Aka Yi Musu A Hukumance

Shugaban Kasar Sin Da Uwargidansa Sun Taya Sarki Charles Na III Da Sarauniya Camilla Murnar Nadin Da Aka Yi Musu A Hukumance

LABARAI MASU NASABA

Ma’aikatar Tsaron Kasar Sin Ta Maida Martani Game Da Munanan Kalaman Sakataren Tsaron Amurka Kan Kasar Sin

Ma’aikatar Tsaron Kasar Sin Ta Maida Martani Game Da Munanan Kalaman Sakataren Tsaron Amurka Kan Kasar Sin

June 1, 2025
Tsohon Minista Ya Fice Daga Jam’iyyar APC A Nasarawa

Tsohon Minista Ya Fice Daga Jam’iyyar APC A Nasarawa

June 1, 2025
Ranar Yara Ta Duniya: Yadda Shugaba Xi Ya Kasance Tare Da Yara

Ranar Yara Ta Duniya: Yadda Shugaba Xi Ya Kasance Tare Da Yara

June 1, 2025
Sin Na Matukar Adawa Da Munanan Kalaman Sakataren Tsaron Amurka

Sin Na Matukar Adawa Da Munanan Kalaman Sakataren Tsaron Amurka

June 1, 2025
Sanatocin Arewa Sun Yi Jimamin Rasuwar ‘Yan Wasan Kano

Sanatocin Arewa Sun Yi Jimamin Rasuwar ‘Yan Wasan Kano

June 1, 2025
Binciken CGTN Ya Nuna Kaso Kusan 90 Bisa Dari Na Masu Bayyana Ra’ayoyi Na Kokawa Da Makomar “Mafarkin Amurka”

Binciken CGTN Ya Nuna Kaso Kusan 90 Bisa Dari Na Masu Bayyana Ra’ayoyi Na Kokawa Da Makomar “Mafarkin Amurka”

June 1, 2025
Gwamnatin Kano Ta Ba Da Hutun Makaranta Domin Bukukuwan Sallah

Gwamnatin Kano Ta Ba Da Hutun Makaranta Domin Bukukuwan Sallah

June 1, 2025
bakin wake

Bam Ya Kashe Mutane 9 A Wata Tashar Motoci Da Ke Borno 

June 1, 2025
‘Yan Wasan Da Tauraruwar Ronaldo Da Messi Ta Hana Su Haskawa

‘Yan Wasan Da Tauraruwar Ronaldo Da Messi Ta Hana Su Haskawa

June 1, 2025
NDLEA Ta Cafke Masu Tura Alhazai Saudiyya Domin Safarar Hodar Iblis Zuwa Kasar

NDLEA Ta Cafke Masu Tura Alhazai Saudiyya Domin Safarar Hodar Iblis Zuwa Kasar

June 1, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.