• English
  • Business News
Friday, May 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Jaridar Business Day Ta Karrama Gwamnan Gombe Kan Hidimta Wa Al’ummarsa

by Khalid Idris Doya
2 years ago
in Labarai
0
Jaridar Business Day Ta Karrama Gwamnan Gombe Kan Hidimta Wa Al’ummarsa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Jaridar ‘Business Day’ ta karrama Gwamnan Jihar Gombe, Muhammadu Inuwa Yahaya, da lambar yabo na gwamna Mafi kwazo a fagen yi wa al’ummar jiharsa hidima. 

 

An gudanar da taron Bada lambar yabon gwarazan na shekarar 2022 ne a ranar Alhamis a Abuja Continental Hotel (Sheraton Hotel and Towers) yayin da mataimakin Gwamnan, Dr. Manassah Daniel Jatau ne ya karɓi kyaututtukan a madadinsa.

  • Tsare-Tsare Ga Ma’aikata: Gwamnonin Bauchi Da Gombe Sun Samu Babbar Lambar Yabo Daga Kungiyar Kwadago Ta TUC

Sauran fitattun mutanen da suka samu lambar yabo a bikin sun hada da Gwamnan Jihar Edo Godwin Obaseki, da Ministan Kwadago da Tallafi Chris Ngige, da Babban Daraktan Hukumar Bunmasa Fasahar Sadarwa ta Kasa NITDA, Kashifu Inuwa da dai sauransu.

 

Labarai Masu Nasaba

Farfaɗo Da Mutuncin Nijeriya Ta Hanyar Buɗe Kofofin Kasuwanci Da Ƙasashen Waje

Hukuncin Tarar Dala Miliyan 220 Da Kotu Ta Ci Kamfanin Meta Ya Yi Daidai

Mawallafi kuma shugaban kamfanin ‘Business Day Media’, Mr Frank Aigbogun, ya ce an shirya taron ne don karfafa gwiwar shugabanni a matakin jihohi su rungumi al’adar aiki tukuru, da samar da ribar demokradiyya ga al’umma.

 

A cewarsa, Gwamna Muhammadu Inuwa Yahaya ya fafata ne da wasu gwamnoni a bangarori daban-daban, kuma jihar sa ta zama zakara wacce tafi kowace jiha a fagen saukaka harkokin kasuwanci, kuma jihar da ta fi inganta yankunan karkara da birane.

 

“An cimma hakan ne bayan da kwamitin bada lambar yabon wanda ya kunshi fitattun mutane ya tattara bayanan da suka dace kai tsaye, da kuma nazarin sauran bayanan da aka tattara daga ɓangarori daban-daban na tattalin arziki da zamantakewa.

Business day

“Mun ga ci gaba sosai a Jihar Gombe tun bayan hawan Gwamna Inuwa Yahaya, mun ji irin nasarorin da ya samu a fannin kiwon lafiya, da samar da ababen more rayuwa, da raya karkara da zuba jari. A ‘yan kwanaki kadan da suka gabata mun ga yadda jihar sa ta samu matsayi na daya a fagen saukala harkokin da harkokin kasuwanci.

 

“Hakan bai zo mana da mamaki ba ganin yadda gwamnan yake ta lashe lambobin yabon da mukan bayar a kai a kai bayan shirya gasa, muna taya mai girma gwamna murna kuma muna kara masa kwarin guiwa kan ya ci gaba da irin wannan kokari nasa”.

 

Da yake karbar lambar yabon a madadin Gwamna Inuwa, Mataimakin nasa Dakta Manassah Daniel Jatau, ya bayyana karramawar a matsayin kalubalen da zai zaburar da shi wajen kara jajircewa kan aikin da ya saba.

 

Sai ya yaba wa kafar yada labaran bisa wannar karramawa ta aiki tukuru da nagarta a harkokin mulki.

 

“Zan fara da yaba wa Mawallafin wannar jarida ta Business Day bisa wannan karramawa da lambar yabo. Wannan wani aiki ne mai matukar muhimmanci da kuka yi. A makon daya gabatan nan muka samu lambar yabo a matsayin jiha mafi fice a fagen saukaka kasuwanci da kuma wani a matsayin gwamnati mafi haba-haba da ma’aikata, daga kungiyar Kwadago ta kasa TUC, kuma a yau ma ga shi muna sake samun wata lambar yabon na gwamnati mafi kwazo a fagen yiwa al’ummar ta hidima”.

 

“A gare mu, samun lambar yabo wani kalubale ne, nauyi ne da kuma tsammanin cewa za mu yi fiye da haka. Bisa tsari na fahimta, babu wanda zai iya yin komai shi kadai. Muna godiya da gudunmawar da kowa ke bayarwa a Jihar Gombe, musamman wadanda suka bada gudunmawa wajen samun wannar lambar yabo. Don haka mun sadaukar da wannar lambar yabo ga dokacin al’ummar jihar bisa irin gudunmawar da suka bayar wajen samun nasarar gwamnatin mu”.

 

“Ina gayyatar ku zuwa Jihar Gombe don ku ganewa idon ku cibiyar masana’antu ta Muhammadu Buhari mai girman kadada 1000, inda muka samar da duk abin da ake bukata da suka hada da wutar lantarki daga madatsar ruwa ta Dadinkowa, da ayyukan more rayuwa na zamani da abubuwan jin dadin jama’a da kuma zaman lafiya domin kasuwanci ya bunkasa. Ina kuma gayyatar ku da ku zo ku zuba jari a Jihar Gombe, muna da kyakkyawan yanayi na kasuwanci”.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

FIFA Ta Yi Barazanar Kin Haska Kofin Duniya Na Mata A Wasu Kasashen

Next Post

Shugaban Kasar Sin Da Uwargidansa Sun Taya Sarki Charles Na III Da Sarauniya Camilla Murnar Nadin Da Aka Yi Musu A Hukumance

Related

Farfaɗo Da Mutuncin Nijeriya Ta Hanyar Buɗe Kofofin Kasuwanci Da Ƙasashen Waje
Manyan Labarai

Farfaɗo Da Mutuncin Nijeriya Ta Hanyar Buɗe Kofofin Kasuwanci Da Ƙasashen Waje

26 minutes ago
Hukuncin Tarar Dala Miliyan 220 Da Kotu Ta Ci Kamfanin Meta Ya Yi Daidai
Manyan Labarai

Hukuncin Tarar Dala Miliyan 220 Da Kotu Ta Ci Kamfanin Meta Ya Yi Daidai

1 hour ago
Man Utd Ta Lallasa Bilbao, Ta Kai Wasan Ƙarshe Na Gasar Europa
Manyan Labarai

Man Utd Ta Lallasa Bilbao, Ta Kai Wasan Ƙarshe Na Gasar Europa

10 hours ago
Me Ya Sa ‘Yan Kasuwar Kasashen Afirka Rungumar Kudin RMB?
Ra'ayi Riga

Me Ya Sa ‘Yan Kasuwar Kasashen Afirka Rungumar Kudin RMB?

13 hours ago
Robert Prevost Ya Zama Ba’amurke Na Farko Da Ya Zama Fafaroma
Da ɗumi-ɗuminsa

Robert Prevost Ya Zama Ba’amurke Na Farko Da Ya Zama Fafaroma

14 hours ago
Sojoji Sun Kama Ƙasurgumin Ɗan Bindiga, Sun Kashe Shugaban IPOB
Manyan Labarai

Sojoji Sun Kama Ƙasurgumin Ɗan Bindiga, Sun Kashe Shugaban IPOB

14 hours ago
Next Post
Shugaban Kasar Sin Da Uwargidansa Sun Taya Sarki Charles Na III Da Sarauniya Camilla Murnar Nadin Da Aka Yi Musu A Hukumance

Shugaban Kasar Sin Da Uwargidansa Sun Taya Sarki Charles Na III Da Sarauniya Camilla Murnar Nadin Da Aka Yi Musu A Hukumance

LABARAI MASU NASABA

Farfaɗo Da Mutuncin Nijeriya Ta Hanyar Buɗe Kofofin Kasuwanci Da Ƙasashen Waje

Farfaɗo Da Mutuncin Nijeriya Ta Hanyar Buɗe Kofofin Kasuwanci Da Ƙasashen Waje

May 9, 2025
Hukuncin Tarar Dala Miliyan 220 Da Kotu Ta Ci Kamfanin Meta Ya Yi Daidai

Hukuncin Tarar Dala Miliyan 220 Da Kotu Ta Ci Kamfanin Meta Ya Yi Daidai

May 9, 2025
Xi Da Putin Sun Gana Da Manema Labarai Tare

Xi Da Putin Sun Gana Da Manema Labarai Tare

May 8, 2025
Man Utd Ta Lallasa Bilbao, Ta Kai Wasan Ƙarshe Na Gasar Europa

Man Utd Ta Lallasa Bilbao, Ta Kai Wasan Ƙarshe Na Gasar Europa

May 8, 2025
Xi: Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Rasha Na Samar Da Daidaito Ga Duniya Mai Cike Da Tashin Hankali

Xi: Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Rasha Na Samar Da Daidaito Ga Duniya Mai Cike Da Tashin Hankali

May 8, 2025
Xi Da Putin Sun Rattaba Hannu Kan Sanarwar Hadin Gwiwa A Sabon Zamani

Xi Da Putin Sun Rattaba Hannu Kan Sanarwar Hadin Gwiwa A Sabon Zamani

May 8, 2025
Waiwaye Game Da Gudummawar Shawarar BRI Ga Duniya

Waiwaye Game Da Gudummawar Shawarar BRI Ga Duniya

May 8, 2025
Me Ya Sa ‘Yan Kasuwar Kasashen Afirka Rungumar Kudin RMB?

Me Ya Sa ‘Yan Kasuwar Kasashen Afirka Rungumar Kudin RMB?

May 8, 2025
Bisa Rokon Bangaren Amurka Ne Manyan Jami’In Kasar Sin Zai Tattauna Da Takwaransa Na Gwamnatin Amurka Kan Batun Ciniki Da Tattalin Arziki

Bisa Rokon Bangaren Amurka Ne Manyan Jami’In Kasar Sin Zai Tattauna Da Takwaransa Na Gwamnatin Amurka Kan Batun Ciniki Da Tattalin Arziki

May 8, 2025
Robert Prevost Ya Zama Ba’amurke Na Farko Da Ya Zama Fafaroma

Robert Prevost Ya Zama Ba’amurke Na Farko Da Ya Zama Fafaroma

May 8, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.