• English
  • Business News
Monday, October 20, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Jaridar ‘NATIONAL ECONOMY’ Za Ta Koma Fita Mako-Mako Daga 29 Ga Agusta

by Khalid Idris Doya
3 years ago
Jarida

Jaridar kasuwanci mafi girma a fadin Nijeriya, NATIONAL ECONOMY Newspaper, za ta koma fita mako-mako daga ranar 29 ga watan Agustan 2022.

Jaridar National Economy dai tana karkashin kamfanin buga jaridar LEADERSHIP ne wacce take fita kowace rana tun daga ranar Alhamis na watan Fabrairun 2020 wacce ta maida hankali wajen gudanar da aikin jarida kan harkokin kasuwanci a Nijeriya da gudanar da binciken kwakwaf tare da yin rahotonni kan harkokin kasuwanci da tattalin arziki a cikin shekaru biyu da wata bakwai da ta shafe tana fita kowace rana.

  • Kaso 6 Na Al’umma Ne Kadai Ke Ganin Duniya Za Ta Kasance Karkashin Ikon Amurka
  • Matar Shugaban Kasar Amurka Ta Kamu Da COVID-19 

Jaridar ya bada gudunmawa sosai wajen kyautata harkokin kasuwanci da tattalin arziki ta hanyar nakaltowa daga masana da fasihai domin su yi sharhi kan lamuran da suka shafi kasuwanci da tattalin arziki da ankarar da wadanda suka dace a fannin da ke bukatar gyaran fuska.

Kamar yadda shugaban sashin labaru na jaridar NATIONAL ECONOMY, Mista Bayo Amodu ke cewa, sauyin an yi ne da zimmar ingantawa da kyautata jaridar tare da bunkasa aiki domin masu karanta jaridar da abokan huldar kasuwancinta su kara gamsuwa, ya kuma ce ba za su rage ingancin abubuwan da suke wallafa a jaridar ba illa ma su kara.

Ya ce, jaridar ta na da shafin yanar gizo mafi inganci ta addireshi www.nationaleconomy.com da suke wallafa labaran da suka shafi harkokin kasuwanci a kowani lokaci a kowace rana.

LABARAI MASU NASABA

Tinubu Ya Baro Brazil Bayan Halartar Taron BRICS Na 2025

Kuratan Sojoji 1,196 Aka Yaye A Makarantar Horar Da Sojoji Ta Zariya

Ya ce, “A bisa manufar jaridar tattalin arziki ta National Economy ta kasancewa jaridar wacce ke maida hankali wajen wallafa labarai da mukaloli da batutuwan da suka shafi harkokin kasuwanci da tattalin arziki ga jama’a da kuma kamfanoni, bisa gaskiya da kwarewa hadi da sahihan batutuwa, muna tabbatar wa masu karatu da hulda da mu cewa za mu ci gaba da kara himma wajen hidimta musu.

‘‘Kamar yadda kuka sani, mun karbu sosai mun kuma shahara sosai wajen samar da labaran da suka shafi harkokin kasuwanci da tattalin arziki don mun kai kwaloluwar mataki a fagen yada labaran kasuwanci a Nijeriya.

“Ta hanyar fasahar sadarwar zamani, jaridarmu da muke fitarwa muke kuma yadawa hatta ta hanyar E-paper dubun-dubatan jama’a a cikin lunguna da sakona da kasar nan da kasashen waje ke karanta jaridar duk rana.

‘‘Shafinmu ta yanar gizo, nationaleconomy.com shi ma na samun dubban maziyarta a kowani lokaci. Mun yi amanar cewa komawa mako-mako da za mu yi, zai ba mu dama mu kara azama da kwazo wajen muka hidima fiye da yadda yanzu, ta hanyar fito da muhimman labaran kasuwanci da tattalin arziki, nazari da sharhi.”

Shugaban labarun ya kuma ce shafin nasu na yanar gizo zai cigaba da wallafa labarai a kowani lokaci.

Bayo ya kara da cewa muhimman shafukan da suke cikin jaridar kama daga na mukaloli, sharhi, noma, muhawara, kimiyya, batutuwan kasuwanci, masana’antu da sauransu dukka suna daga cikin ababen da za su gaba da fitowa.

Daga bisani ya nuna cewa hukumar gudanarwar jaridar ta nuna godiyarta ga abokan jere musamman masu karanta jaridar duk rana da kuma masu bata talluka tsawon shekarun da ta shafe tana fita duk rana, ya nemi karin hadin kansu kan hakan domin jaridar ta ci gaba da ingantawa.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Tinubu Ya Baro Brazil Bayan Halartar Taron BRICS Na 2025
Labaran Kasuwanci

Tinubu Ya Baro Brazil Bayan Halartar Taron BRICS Na 2025

July 12, 2025
Kuratan Sojoji 1,196 Aka Yaye A Makarantar Horar Da Sojoji Ta Zariya
Labaran Kasuwanci

Kuratan Sojoji 1,196 Aka Yaye A Makarantar Horar Da Sojoji Ta Zariya

June 21, 2025
Za Mu Tabbatar Da Samun Kyakkyawar Alaka Da Gwamnati Don Ci Gaban Kasuwar Kofar Ruwa – ‘Yanleman
Labaran Kasuwanci

Za Mu Tabbatar Da Samun Kyakkyawar Alaka Da Gwamnati Don Ci Gaban Kasuwar Kofar Ruwa – ‘Yanleman

January 11, 2025
Next Post
Ministan Harkokin Wajen Sin Ya Gana Da Jakadun Kasashe Masu Tasowa Ta Kafar Bidiyo

Ministan Harkokin Wajen Sin Ya Gana Da Jakadun Kasashe Masu Tasowa Ta Kafar Bidiyo

LABARAI MASU NASABA

Kano Derby: Barau FC Ta Doke Kano Pillars A Karon Farko A Tarihin Gamuwarsu

Kano Derby: Barau FC Ta Doke Kano Pillars A Karon Farko A Tarihin Gamuwarsu

October 19, 2025
Binciken CGTN: An Fitar Da Sakamakon Jin Ra’ayin Jama’a Dangane Da Cikakken Zama Na 4 Na Kwamitin Kolin JKS Na 20

Binciken CGTN: An Fitar Da Sakamakon Jin Ra’ayin Jama’a Dangane Da Cikakken Zama Na 4 Na Kwamitin Kolin JKS Na 20

October 19, 2025
Arewa Ta Samu Kashi 56% Na Muƙaman Gwamnatin Tinubu — Shugaban FCC

Arewa Ta Samu Kashi 56% Na Muƙaman Gwamnatin Tinubu — Shugaban FCC

October 19, 2025
Xi Jinping Ya Mika Sakon Taya Cheng Li-wun Murnar Zama Shugabar Jam’iyyar KMT Ta Kasar Sin

Xi Jinping Ya Mika Sakon Taya Cheng Li-wun Murnar Zama Shugabar Jam’iyyar KMT Ta Kasar Sin

October 19, 2025
Ɗan Jarida Ibrahim Ɗan’uwa Rano Ya Shaƙi Iskar Ƴanci Bayan Tsare Shi

Ɗan Jarida Ibrahim Ɗan’uwa Rano Ya Shaƙi Iskar Ƴanci Bayan Tsare Shi

October 19, 2025
Tie Ning Ta Halarci Bikin Bude Taron Karawa Juna Sani Na ‘Yan Majalisun Dokokin Kasashen Afirka

Tie Ning Ta Halarci Bikin Bude Taron Karawa Juna Sani Na ‘Yan Majalisun Dokokin Kasashen Afirka

October 19, 2025
Ƴansanda Sun Kama Ɗan Jarida A Kano Bisa Zargin Ɓata Suna

Ƴansanda Sun Kama Ɗan Jarida A Kano Bisa Zargin Ɓata Suna

October 19, 2025
Amfanin Yawan Shan Ruwa Da Kuma Illolin Rashin Yawan Sha

Amfanin Yawan Shan Ruwa Da Kuma Illolin Rashin Yawan Sha

October 19, 2025
Xinjiang Ta Janyo Karin Jari A Rubu’i Uku Na Farkon Shekarar Nan

Xinjiang Ta Janyo Karin Jari A Rubu’i Uku Na Farkon Shekarar Nan

October 19, 2025
Yadda Shagwaɓa Kananan Yara Da Kudi Ke Shafar Tarbiyyarsu

Yadda Shagwaɓa Kananan Yara Da Kudi Ke Shafar Tarbiyyarsu

October 19, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.