• English
  • Business News
Sunday, August 24, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Jaridar ‘NATIONAL ECONOMY’ Za Ta Koma Fita Mako-Mako Daga 29 Ga Agusta

by Khalid Idris Doya
3 years ago
in Labaran Kasuwanci
0
Jaridar ‘NATIONAL ECONOMY’ Za Ta Koma Fita Mako-Mako Daga 29 Ga Agusta
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Jaridar kasuwanci mafi girma a fadin Nijeriya, NATIONAL ECONOMY Newspaper, za ta koma fita mako-mako daga ranar 29 ga watan Agustan 2022.

Jaridar National Economy dai tana karkashin kamfanin buga jaridar LEADERSHIP ne wacce take fita kowace rana tun daga ranar Alhamis na watan Fabrairun 2020 wacce ta maida hankali wajen gudanar da aikin jarida kan harkokin kasuwanci a Nijeriya da gudanar da binciken kwakwaf tare da yin rahotonni kan harkokin kasuwanci da tattalin arziki a cikin shekaru biyu da wata bakwai da ta shafe tana fita kowace rana.

  • Kaso 6 Na Al’umma Ne Kadai Ke Ganin Duniya Za Ta Kasance Karkashin Ikon Amurka
  • Matar Shugaban Kasar Amurka Ta Kamu Da COVID-19 

Jaridar ya bada gudunmawa sosai wajen kyautata harkokin kasuwanci da tattalin arziki ta hanyar nakaltowa daga masana da fasihai domin su yi sharhi kan lamuran da suka shafi kasuwanci da tattalin arziki da ankarar da wadanda suka dace a fannin da ke bukatar gyaran fuska.

Kamar yadda shugaban sashin labaru na jaridar NATIONAL ECONOMY, Mista Bayo Amodu ke cewa, sauyin an yi ne da zimmar ingantawa da kyautata jaridar tare da bunkasa aiki domin masu karanta jaridar da abokan huldar kasuwancinta su kara gamsuwa, ya kuma ce ba za su rage ingancin abubuwan da suke wallafa a jaridar ba illa ma su kara.

Ya ce, jaridar ta na da shafin yanar gizo mafi inganci ta addireshi www.nationaleconomy.com da suke wallafa labaran da suka shafi harkokin kasuwanci a kowani lokaci a kowace rana.

Labarai Masu Nasaba

Tinubu Ya Baro Brazil Bayan Halartar Taron BRICS Na 2025

Kuratan Sojoji 1,196 Aka Yaye A Makarantar Horar Da Sojoji Ta Zariya

Ya ce, “A bisa manufar jaridar tattalin arziki ta National Economy ta kasancewa jaridar wacce ke maida hankali wajen wallafa labarai da mukaloli da batutuwan da suka shafi harkokin kasuwanci da tattalin arziki ga jama’a da kuma kamfanoni, bisa gaskiya da kwarewa hadi da sahihan batutuwa, muna tabbatar wa masu karatu da hulda da mu cewa za mu ci gaba da kara himma wajen hidimta musu.

‘‘Kamar yadda kuka sani, mun karbu sosai mun kuma shahara sosai wajen samar da labaran da suka shafi harkokin kasuwanci da tattalin arziki don mun kai kwaloluwar mataki a fagen yada labaran kasuwanci a Nijeriya.

“Ta hanyar fasahar sadarwar zamani, jaridarmu da muke fitarwa muke kuma yadawa hatta ta hanyar E-paper dubun-dubatan jama’a a cikin lunguna da sakona da kasar nan da kasashen waje ke karanta jaridar duk rana.

‘‘Shafinmu ta yanar gizo, nationaleconomy.com shi ma na samun dubban maziyarta a kowani lokaci. Mun yi amanar cewa komawa mako-mako da za mu yi, zai ba mu dama mu kara azama da kwazo wajen muka hidima fiye da yadda yanzu, ta hanyar fito da muhimman labaran kasuwanci da tattalin arziki, nazari da sharhi.”

Shugaban labarun ya kuma ce shafin nasu na yanar gizo zai cigaba da wallafa labarai a kowani lokaci.

Bayo ya kara da cewa muhimman shafukan da suke cikin jaridar kama daga na mukaloli, sharhi, noma, muhawara, kimiyya, batutuwan kasuwanci, masana’antu da sauransu dukka suna daga cikin ababen da za su gaba da fitowa.

Daga bisani ya nuna cewa hukumar gudanarwar jaridar ta nuna godiyarta ga abokan jere musamman masu karanta jaridar duk rana da kuma masu bata talluka tsawon shekarun da ta shafe tana fita duk rana, ya nemi karin hadin kansu kan hakan domin jaridar ta ci gaba da ingantawa.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AgustaJaridar KasuwanciLEADERSHIPMako-Mako
ShareTweetSendShare
Previous Post

Matar Shugaban Kasar Amurka, Jill Biden Ta Kamu Da COVID-19 

Next Post

Ministan Harkokin Wajen Sin Ya Gana Da Jakadun Kasashe Masu Tasowa Ta Kafar Bidiyo

Related

Tinubu Ya Baro Brazil Bayan Halartar Taron BRICS Na 2025
Labaran Kasuwanci

Tinubu Ya Baro Brazil Bayan Halartar Taron BRICS Na 2025

1 month ago
Kuratan Sojoji 1,196 Aka Yaye A Makarantar Horar Da Sojoji Ta Zariya
Labaran Kasuwanci

Kuratan Sojoji 1,196 Aka Yaye A Makarantar Horar Da Sojoji Ta Zariya

2 months ago
Za Mu Tabbatar Da Samun Kyakkyawar Alaka Da Gwamnati Don Ci Gaban Kasuwar Kofar Ruwa – ‘Yanleman
Labaran Kasuwanci

Za Mu Tabbatar Da Samun Kyakkyawar Alaka Da Gwamnati Don Ci Gaban Kasuwar Kofar Ruwa – ‘Yanleman

7 months ago
Alternative Bank Shi Ne Mafi Inganci Da Baya Amfani Da Kuɗin Ruwa Da Zuwa Da Fasaha A 2024
Labarai

Alternative Bank Shi Ne Mafi Inganci Da Baya Amfani Da Kuɗin Ruwa Da Zuwa Da Fasaha A 2024

9 months ago
Kamfanin NNPCL Zai Cefanar Da Matatun Mai Na Kaduna Da Warri
Labarai

Kamfanin NNPCL Zai Cefanar Da Matatun Mai Na Kaduna Da Warri

12 months ago
Ministan Ma’adanai Ya Bukaci Masu Harkar Ma’adanai A Jihar Nasarawa Su Zauna Lafiya
Labaran Kasuwanci

Ministan Ma’adanai Ya Bukaci Masu Harkar Ma’adanai A Jihar Nasarawa Su Zauna Lafiya

12 months ago
Next Post
Ministan Harkokin Wajen Sin Ya Gana Da Jakadun Kasashe Masu Tasowa Ta Kafar Bidiyo

Ministan Harkokin Wajen Sin Ya Gana Da Jakadun Kasashe Masu Tasowa Ta Kafar Bidiyo

LABARAI MASU NASABA

NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru

NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru

August 23, 2025
Amfani Da Rashin Amfanin Auren Jari

Amfani Da Rashin Amfanin Auren Jari

August 23, 2025
CMG Ya Yi Bikin Cudanyar Al’adu Mai Taken “Sautin Zaman Lafiya” A Hadaddiyar Daular Larabawa Da Koriya Ta Kudu

CMG Ya Yi Bikin Cudanyar Al’adu Mai Taken “Sautin Zaman Lafiya” A Hadaddiyar Daular Larabawa Da Koriya Ta Kudu

August 23, 2025
Yadda Ake Alale

Yadda Ake Alale

August 23, 2025
Babban Sakataren SCO: Sin Na Taka Rawar Gani A Matsayin Kasar Da Ke Shugabancin SCO

Babban Sakataren SCO: Sin Na Taka Rawar Gani A Matsayin Kasar Da Ke Shugabancin SCO

August 23, 2025
Matsalar Al’ada Da Ciwon Mara Ga Mata

Matsalar Al’ada Da Ciwon Mara Ga Mata

August 23, 2025
CMG Ya Kaddamar Da Gangamin Tattara Fina-Finai Da Talabijin Da Aka Samar Bisa AI A Los Angeles

CMG Ya Kaddamar Da Gangamin Tattara Fina-Finai Da Talabijin Da Aka Samar Bisa AI A Los Angeles

August 23, 2025
Taron Kare Hakkin Dan Adam Na Sin Da Afirka Na Farko Ya Nemi Hada Karfi Don Tabbatar Da ‘Yancin Samun Ci Gaba

Taron Kare Hakkin Dan Adam Na Sin Da Afirka Na Farko Ya Nemi Hada Karfi Don Tabbatar Da ‘Yancin Samun Ci Gaba

August 23, 2025
Bangaren Kasuwancin “E-Commerce” Na Kasar Sin Ya Karu Sosai A Watanni 7 Na Farkon Bana

Bangaren Kasuwancin “E-Commerce” Na Kasar Sin Ya Karu Sosai A Watanni 7 Na Farkon Bana

August 23, 2025
Yajin Aiki: Kungiyar ASUP Ta Ba Gwamntin Tarayya Wa’adin Kwana 21 Ta Biya Masu Bukatu

Yajin Aiki: Kungiyar ASUP Ta Ba Gwamntin Tarayya Wa’adin Kwana 21 Ta Biya Masu Bukatu

August 23, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.