ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 5, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Jaridar ‘NATIONAL ECONOMY’ Za Ta Koma Fita Mako-Mako Daga 29 Ga Agusta

by Khalid Idris Doya
4 years ago
Jarida

Jaridar kasuwanci mafi girma a fadin Nijeriya, NATIONAL ECONOMY Newspaper, za ta koma fita mako-mako daga ranar 29 ga watan Agustan 2022.

Jaridar National Economy dai tana karkashin kamfanin buga jaridar LEADERSHIP ne wacce take fita kowace rana tun daga ranar Alhamis na watan Fabrairun 2020 wacce ta maida hankali wajen gudanar da aikin jarida kan harkokin kasuwanci a Nijeriya da gudanar da binciken kwakwaf tare da yin rahotonni kan harkokin kasuwanci da tattalin arziki a cikin shekaru biyu da wata bakwai da ta shafe tana fita kowace rana.

  • Kaso 6 Na Al’umma Ne Kadai Ke Ganin Duniya Za Ta Kasance Karkashin Ikon Amurka
  • Matar Shugaban Kasar Amurka Ta Kamu Da COVID-19 

Jaridar ya bada gudunmawa sosai wajen kyautata harkokin kasuwanci da tattalin arziki ta hanyar nakaltowa daga masana da fasihai domin su yi sharhi kan lamuran da suka shafi kasuwanci da tattalin arziki da ankarar da wadanda suka dace a fannin da ke bukatar gyaran fuska.

ADVERTISEMENT

Kamar yadda shugaban sashin labaru na jaridar NATIONAL ECONOMY, Mista Bayo Amodu ke cewa, sauyin an yi ne da zimmar ingantawa da kyautata jaridar tare da bunkasa aiki domin masu karanta jaridar da abokan huldar kasuwancinta su kara gamsuwa, ya kuma ce ba za su rage ingancin abubuwan da suke wallafa a jaridar ba illa ma su kara.

Ya ce, jaridar ta na da shafin yanar gizo mafi inganci ta addireshi www.nationaleconomy.com da suke wallafa labaran da suka shafi harkokin kasuwanci a kowani lokaci a kowace rana.

LABARAI MASU NASABA

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Nijeriya Ta Yi Asarar Biliyoyin Naira Saboda Dakatar Da Shigo Da Motoci Ta Iyakokinta

Ya ce, “A bisa manufar jaridar tattalin arziki ta National Economy ta kasancewa jaridar wacce ke maida hankali wajen wallafa labarai da mukaloli da batutuwan da suka shafi harkokin kasuwanci da tattalin arziki ga jama’a da kuma kamfanoni, bisa gaskiya da kwarewa hadi da sahihan batutuwa, muna tabbatar wa masu karatu da hulda da mu cewa za mu ci gaba da kara himma wajen hidimta musu.

‘‘Kamar yadda kuka sani, mun karbu sosai mun kuma shahara sosai wajen samar da labaran da suka shafi harkokin kasuwanci da tattalin arziki don mun kai kwaloluwar mataki a fagen yada labaran kasuwanci a Nijeriya.

“Ta hanyar fasahar sadarwar zamani, jaridarmu da muke fitarwa muke kuma yadawa hatta ta hanyar E-paper dubun-dubatan jama’a a cikin lunguna da sakona da kasar nan da kasashen waje ke karanta jaridar duk rana.

‘‘Shafinmu ta yanar gizo, nationaleconomy.com shi ma na samun dubban maziyarta a kowani lokaci. Mun yi amanar cewa komawa mako-mako da za mu yi, zai ba mu dama mu kara azama da kwazo wajen muka hidima fiye da yadda yanzu, ta hanyar fito da muhimman labaran kasuwanci da tattalin arziki, nazari da sharhi.”

Shugaban labarun ya kuma ce shafin nasu na yanar gizo zai cigaba da wallafa labarai a kowani lokaci.

Bayo ya kara da cewa muhimman shafukan da suke cikin jaridar kama daga na mukaloli, sharhi, noma, muhawara, kimiyya, batutuwan kasuwanci, masana’antu da sauransu dukka suna daga cikin ababen da za su gaba da fitowa.

Daga bisani ya nuna cewa hukumar gudanarwar jaridar ta nuna godiyarta ga abokan jere musamman masu karanta jaridar duk rana da kuma masu bata talluka tsawon shekarun da ta shafe tana fita duk rana, ya nemi karin hadin kansu kan hakan domin jaridar ta ci gaba da ingantawa.

Jarida
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Zaɓen Fidda Gwani Na Gwamna: Ba Za Mu Lamunci Kaƙaba Mana Ɗan Takara A Bauchi Ba – Mambobin APC
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Sanata Buba Ya Janye Daga Takarar Fidda Gwani Ta Gwamnan APC A Bauchi, Ya Zargi Cewa ‘Ɗauki Ɗaura Ake Yi Ba Zaɓe Ba”

MASU ALAKA

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba
Labaran Kasuwanci

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026
Nijeriya Ta Yi Asarar Biliyoyin Naira Saboda Dakatar Da Shigo Da Motoci Ta Iyakokinta
Labaran Kasuwanci

Nijeriya Ta Yi Asarar Biliyoyin Naira Saboda Dakatar Da Shigo Da Motoci Ta Iyakokinta

May 29, 2026
Farashin Siminti Zai Ragu Idan Farashin Kayan Aiki Ya Sauka – BUA
Labaran Kasuwanci

Farashin Siminti Zai Ragu Idan Farashin Kayan Aiki Ya Sauka – BUA

May 21, 2026
Next Post
Ministan Harkokin Wajen Sin Ya Gana Da Jakadun Kasashe Masu Tasowa Ta Kafar Bidiyo

Ministan Harkokin Wajen Sin Ya Gana Da Jakadun Kasashe Masu Tasowa Ta Kafar Bidiyo

LABARAI MASU NASABA

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

June 4, 2026
Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.