ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Jaridar ‘NATIONAL ECONOMY’ Za Ta Koma Fita Mako-Mako Daga 29 Ga Agusta

by Khalid Idris Doya
4 years ago
Jarida

Jaridar kasuwanci mafi girma a fadin Nijeriya, NATIONAL ECONOMY Newspaper, za ta koma fita mako-mako daga ranar 29 ga watan Agustan 2022.

Jaridar National Economy dai tana karkashin kamfanin buga jaridar LEADERSHIP ne wacce take fita kowace rana tun daga ranar Alhamis na watan Fabrairun 2020 wacce ta maida hankali wajen gudanar da aikin jarida kan harkokin kasuwanci a Nijeriya da gudanar da binciken kwakwaf tare da yin rahotonni kan harkokin kasuwanci da tattalin arziki a cikin shekaru biyu da wata bakwai da ta shafe tana fita kowace rana.

  • Kaso 6 Na Al’umma Ne Kadai Ke Ganin Duniya Za Ta Kasance Karkashin Ikon Amurka
  • Matar Shugaban Kasar Amurka Ta Kamu Da COVID-19 

Jaridar ya bada gudunmawa sosai wajen kyautata harkokin kasuwanci da tattalin arziki ta hanyar nakaltowa daga masana da fasihai domin su yi sharhi kan lamuran da suka shafi kasuwanci da tattalin arziki da ankarar da wadanda suka dace a fannin da ke bukatar gyaran fuska.

ADVERTISEMENT

Kamar yadda shugaban sashin labaru na jaridar NATIONAL ECONOMY, Mista Bayo Amodu ke cewa, sauyin an yi ne da zimmar ingantawa da kyautata jaridar tare da bunkasa aiki domin masu karanta jaridar da abokan huldar kasuwancinta su kara gamsuwa, ya kuma ce ba za su rage ingancin abubuwan da suke wallafa a jaridar ba illa ma su kara.

Ya ce, jaridar ta na da shafin yanar gizo mafi inganci ta addireshi www.nationaleconomy.com da suke wallafa labaran da suka shafi harkokin kasuwanci a kowani lokaci a kowace rana.

LABARAI MASU NASABA

Wani Kamfani Ya Tallafa Wa Masu Sana’ar Shayi A Kano

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Ya ce, “A bisa manufar jaridar tattalin arziki ta National Economy ta kasancewa jaridar wacce ke maida hankali wajen wallafa labarai da mukaloli da batutuwan da suka shafi harkokin kasuwanci da tattalin arziki ga jama’a da kuma kamfanoni, bisa gaskiya da kwarewa hadi da sahihan batutuwa, muna tabbatar wa masu karatu da hulda da mu cewa za mu ci gaba da kara himma wajen hidimta musu.

‘‘Kamar yadda kuka sani, mun karbu sosai mun kuma shahara sosai wajen samar da labaran da suka shafi harkokin kasuwanci da tattalin arziki don mun kai kwaloluwar mataki a fagen yada labaran kasuwanci a Nijeriya.

“Ta hanyar fasahar sadarwar zamani, jaridarmu da muke fitarwa muke kuma yadawa hatta ta hanyar E-paper dubun-dubatan jama’a a cikin lunguna da sakona da kasar nan da kasashen waje ke karanta jaridar duk rana.

‘‘Shafinmu ta yanar gizo, nationaleconomy.com shi ma na samun dubban maziyarta a kowani lokaci. Mun yi amanar cewa komawa mako-mako da za mu yi, zai ba mu dama mu kara azama da kwazo wajen muka hidima fiye da yadda yanzu, ta hanyar fito da muhimman labaran kasuwanci da tattalin arziki, nazari da sharhi.”

Shugaban labarun ya kuma ce shafin nasu na yanar gizo zai cigaba da wallafa labarai a kowani lokaci.

Bayo ya kara da cewa muhimman shafukan da suke cikin jaridar kama daga na mukaloli, sharhi, noma, muhawara, kimiyya, batutuwan kasuwanci, masana’antu da sauransu dukka suna daga cikin ababen da za su gaba da fitowa.

Daga bisani ya nuna cewa hukumar gudanarwar jaridar ta nuna godiyarta ga abokan jere musamman masu karanta jaridar duk rana da kuma masu bata talluka tsawon shekarun da ta shafe tana fita duk rana, ya nemi karin hadin kansu kan hakan domin jaridar ta ci gaba da ingantawa.

Jarida
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Yaro Ya Harbe Kansa Har Lahira Bayan Mafarauci Ya Yi Sakaci Da Bindigarsa A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    An Kama Mutane 5 Da Sassan Jikin Ɗan’Adam Za Su Yi Tsafi A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Tsohon Mai Neman Takarar Gwamnan Bauchi, Bala Jibrin, Ya Fice Daga APC Kan Zargin Ɗoki-ɗora
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    ‘Yansanda Sun Cafke Tsoho Mai Shekara 70 Kan Zargin Yi Wa ‘Yar Shekara 8 Fyaɗe A Bauchi

MASU ALAKA

Wani Kamfani Ya Tallafa Wa Masu Sana’ar Shayi A Kano
Labaran Kasuwanci

Wani Kamfani Ya Tallafa Wa Masu Sana’ar Shayi A Kano

August 23, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba
Labaran Kasuwanci

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026
Nijeriya Ta Yi Asarar Biliyoyin Naira Saboda Dakatar Da Shigo Da Motoci Ta Iyakokinta
Labaran Kasuwanci

Nijeriya Ta Yi Asarar Biliyoyin Naira Saboda Dakatar Da Shigo Da Motoci Ta Iyakokinta

May 29, 2026
Next Post
Ministan Harkokin Wajen Sin Ya Gana Da Jakadun Kasashe Masu Tasowa Ta Kafar Bidiyo

Ministan Harkokin Wajen Sin Ya Gana Da Jakadun Kasashe Masu Tasowa Ta Kafar Bidiyo

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.