• English
  • Business News
Friday, August 1, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Jega Ya Warware Zare Da Abawa Kan Hanyoyin Tsaftace Zaben Nijeriya

by Sadiq
2 years ago
in Tambarin Dimokuradiyya
0
Jega Ya Warware Zare Da Abawa Kan Hanyoyin Tsaftace Zaben Nijeriya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Tsohon shugaban hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC), Farfesa Attahiru Jega ya bayyana wasu hanyoyin tsaftace zaben NMijeriya cikin sauki.

Jega ya bayyana hanyoyin ne a lokacin da yake gabatar da jawabi a wurin wani taron kwanaki biyu da ya gudana a Jihar Akwa Ibom.

  • Gwamnatin Tarayya Ta Kara Karbo Bashin Dala Biliyan 3.45 Daga Bankin Duniya
  • Shin Wasan Kwaikwayon Na Zaben Kakakin Majalisar Wakilan Amurka Ta Kawo Karshe Ne? 

Ya ce matukar ana bukatar a tsaftace zaben Nijeriya, to dole ne ya kasance ba shugaban kasa ba ne yake nada shugabannin hukumar INEC.

Tsohon shugaban INEC ya yi kira da a yi wa dokar zabe na 2022 garanbawul.

A cewarsa, duk da cewa dokokin zaben Nijeriya na yanzu za a iya cewa su ne mafi kyau a tarihin kasar nan, amma ba su zama cikakku ba, akwai bukatar a kara yin wasu gyare-gyare domin kawar da rudani da fayyafe abubu yadda suke da kuma karfafa wasu bangarorin dokokin.

Labarai Masu Nasaba

ADC Ga Tinubu: Ina Wutar Lantarki Ta Awa 24 Da Ka Yi Wa ‘Yan Nijeriya Alkawari?

Dalilin Da Ya Sa Har Yanzu Obi Da El-Rufai Ba Su Shiga ADC A Hukumance Ba — Kakakin Jam’iyyar 

Ya ce gyare-gyaren su kasance sun tilasta saka sakamakon zabe ta na’ura a zabe mai zuwa na 2027.

Game da shugabancin hukumar INEC, Jega ya jadda cewa kamata ya yi a cire hannun shugaban kasa wajen ikon nada shugaban INEC da kwamishinonin zabe, domin a ceto hukumar daga nuna bangaranci ko bambanci ko kuma taimaka wa wasu.

Ya kara da cewa ya kamata a sake duba dokokin zabe domin tabbatar da cewa an warware duk matsalolin da suka taso wajen gudanar da zabe da yanke hukunci kafin ranar rantsarwa.

Masu ruwa da tsaki da dama sun bayyana damuwarsu kan sashi na 64 na dokar zabe, wanda ya bayyana tsarin yadda za a bayyana sakamakon zabe, inda cikin sauki za a iya yin magudi da kuma kawo rudani.

Jega ya ce ya kamata a fayyace wannan sashe ta tilasta saka sakamakon zabe ta na’ura tun daga rumfunan zabe da har izuwa cibiyoyin tattara sakamakon zabe daban-daban a fadin kasar nan.

“INEC za ta sami isasshen lokacin da za ta shirya domin wannan lamari, idan an yi wa dokar kwaskwarima da wuri kafin zaben da ke tafe, in ji shi.

Haka kuma, Jega ya yi kira ko dai a bullo da wani tsari da zai bayar da damar fara yin zabe da wuri ga ma’aikatan INEC, masu sa ido da direbobinsu da ‘yan jarida, ko kuma wani tsari na musamman da zai ba su damar yin kada kuri’a a ranar zabe, musamman ma a lokacin zaben shugaban kasa.

Tsohon shugaban INEC ya bayar da shawarar barin ‘yan Nijeriya da ke kasashen waje su kada kuri’unsu a kalla zaben shugaban kasa, domin ba su damar yin zabe, musamman wadanda suke aiki a kasashen ketare.

Ya ce akwai bukatar bai wa mata damar tsayawa takara a kowacce jam’iyya na kashi 35, tun daga mukamin shugaban kasa, gwamnoni, ‘yan majalsa, shugaban kananan hukumomi da kansiloli.

haka zalika, ya ce ya kamata a bai wa INEC ikon gudanar da zaben cike gibi da zarar an samu hakan.

A halin da ake ciki kuma, Farfesa Attahiru Jega, ya musanta cewa an yi magudi a zaben 2023.

Wasu rahotanni sun bayyana cewa Jega ya ce an yi magudi a zaben 2023, a wani taro na kwanaki biyu da majalisar dattawa ta shirya a Ikot Ipene na Jihar Akwa Ibom.

“Mun ga a zabukan 2023, illar kawai yadda masu rike da madafun ikon ke samun damar nada makusantarsu a cikin hukumar zabe domin su taimaka musu wajen lashe zabe,” in ji shi.

Sai dai a wata sanarwa da ta fito daga hannun babban mataimakinsa, Princess Hamman-Obels, Jega ya ce rahotannin da suka bayyana cewa ya ce an tafka magudi a zaben 2023 ba daidai ba ne kuma ba su dace da matsayinsa ba.

Sanarwar ta kara da cewa, “Hankalin Farfesa Attahiru Jega ya karkata ne ga wani rahoto na yaudara da aka buga a jaridu da dama na intanet, inda ya ce an yi magudi a zaben 2023.

“Rahoton da aka yi ba daidai ba ne kuma ba dace da matsayin Farfesa Jega ba, lallai ya musanta yin wannan kalamai game da zaben 2023.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Abinda Ya Kamata Ku Sani Akan Wasan El Classico

Next Post

Duk Da Narka Fiye Da Biliyan 200, Gwamnati Ta Yi Gum A Kan Kidaya

Related

2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC
Tambarin Dimokuradiyya

ADC Ga Tinubu: Ina Wutar Lantarki Ta Awa 24 Da Ka Yi Wa ‘Yan Nijeriya Alkawari?

7 days ago
Dalilin Da Ya Sa Har Yanzu Obi Da El-Rufai Ba Su Shiga ADC A Hukumance Ba — Kakakin Jam’iyyar 
Tambarin Dimokuradiyya

Dalilin Da Ya Sa Har Yanzu Obi Da El-Rufai Ba Su Shiga ADC A Hukumance Ba — Kakakin Jam’iyyar 

1 week ago
Jam’iyyar PDP Ta Janye Daga Shiga ZaÉ“en Ƙananan Hukumomi A Kebbi
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Masu Neman Takarar Shugaban Kasa A PDP Sun Kara Matsa Kaimi Bayan Ficewar Atiku

1 week ago
2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC

2 weeks ago
majalisar kasa
Tambarin Dimokuradiyya

Kirkirar Sabbin Jihohi Da Kananan Hukumomi Sun Dabaibaye Sauraron Jin Ra’ayoyin Gyaran Tsarin Mulki

2 weeks ago
Ko Yanzu Tinubu Ya Yi Rawar Gani, Kuma Yana Ƙoƙari Sosai – Buhari
Rahotonni

Muhimman Abubuwa 10 Da Kowa Zai So Ya Sani Game Da Marigayi Shugaban Ƙasa Buhari

3 weeks ago
Next Post
Duk Da Narka Fiye Da Biliyan 200, Gwamnati Ta Yi Gum A Kan Kidaya

Duk Da Narka Fiye Da Biliyan 200, Gwamnati Ta Yi Gum A Kan Kidaya

LABARAI MASU NASABA

Abin Da Ya Sa NPA Da Kwalejin MAN Oron Suka Yi HaÉ—in Gwiwa

Abin Da Ya Sa NPA Da Kwalejin MAN Oron Suka Yi HaÉ—in Gwiwa

August 1, 2025
Kasar Sin Ta Yi Watsi Da Zargin Amurka Dangane Da Batun Ukraine

Kasar Sin Ta Yi Watsi Da Zargin Amurka Dangane Da Batun Ukraine

August 1, 2025
2027: APC Da ADC Na Gwagwarmayar Neman Samun Goyon Bayan Mutanen Arewa

2027: APC Da ADC Na Gwagwarmayar Neman Samun Goyon Bayan Mutanen Arewa

August 1, 2025
Sin Ta Kadu Da Takunkumin Da Amurka Ta Kakaba Wa Hukumomi Da Jami’an Falasdinu

Sin Ta Kadu Da Takunkumin Da Amurka Ta Kakaba Wa Hukumomi Da Jami’an Falasdinu

August 1, 2025
Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto DimokuraÉ—iyyar Nijeriya Daga Rugujewa

Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto DimokuraÉ—iyyar Nijeriya Daga Rugujewa

August 1, 2025
Sin Ta Samu Bunkasar Tafiye-Tafiye Cikin Gida Da Kashi 20.6% A Rabin Farko Na Bana

Sin Ta Samu Bunkasar Tafiye-Tafiye Cikin Gida Da Kashi 20.6% A Rabin Farko Na Bana

August 1, 2025
Tinubu Ya Sauke Gawuna A Matsayin Shugaban Kwamitin Gudanarwar BUK, Ya Maye Gurbinsa Da Kaita 

Tinubu Ya Sauke Gawuna A Matsayin Shugaban Kwamitin Gudanarwar BUK, Ya Maye Gurbinsa Da Kaita 

August 1, 2025
Majalisar Dokokin Sokoto Ta Aike Wa  Kwamishina Sammaci, Duba Dalili

Majalisar Dokokin Sokoto Ta Aike Wa  Kwamishina Sammaci, Duba Dalili

August 1, 2025
Ministan Tsaron Kasar Sin Ya Nanata Shan Damarar PLA A Kan Sake Hadewar Kasar

Ministan Tsaron Kasar Sin Ya Nanata Shan Damarar PLA A Kan Sake Hadewar Kasar

August 1, 2025
An Bude Atisayen “Hadin Gwiwa Na Teku Na 2025″ Tsakanin Sin Da Rasha

An Bude Atisayen “Hadin Gwiwa Na Teku Na 2025″ Tsakanin Sin Da Rasha

August 1, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.