• English
  • Business News
Sunday, September 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Jerin ‘Yan Wasa Mafi Tsada A Firimiyar Ingila

by Abba Ibrahim Wada
3 years ago
in Wasanni
0
Jerin ‘Yan Wasa Mafi Tsada A Firimiyar Ingila
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kungiyar kwallon kafa ta Manchester United ta sanar da cimma yarjejeniyar sayan dan wasan kungiyar Ajad dan kasar Brazil, Antony, bayan ta amince za ta biya fam miliyan 80.75 da karin tsarabe-tsaraben fam miliyan 4.25.

Dan wasa Antony ya zama dan wasa na biyu da Manchester United ta dauka mai tsada bayan dan wasa Paul Pogba wanda ya kasance mafi tsada da kungiyar Old Trafford ta saya daga Jubentus kan fam miliyan 89 a shekara ta 2016.

  • Pogba Ya Ce Barayi Suna Yi Masa Barazana
  • Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Keta Ka’idojin Fitar Da Kayayyaki

Antony zai zama dan wasa na biyar da Manchester United ta dauka a bana, bayan dan wasa Lisandro Martinez da Casemiro da Tyrell Malacia da kuma Christian Eriksen wanda kwantiraginsa ya kare a Brentford kuma Antony ya taka rawar gani a Ajad da cin kwallo 47 a dukkan fafatawar da ya yi mata kaka biyu.

Dan wasan ya nuna kwarewarsa karkashin kociyan kungiyar na yanzu, Erik ten Hag a Ajad, kuma shi ne kocin ya dauke shi zuwa Manchester United saboda ya san irin salon buga wasansa a baya.

Dan wasan mai shekara 22 a duniya ya zama dan wasa na hudu da aka saya a Premier League da tsada, bayan Paul Pogba da ya koma Manchester United, sai Chelsea da ta dauki Romelu Lukaku da kuma Jack Grealish da Manchester City’ ta dauka.

Labarai Masu Nasaba

Neman Gurbin Kofin Duniya: Arokodare Ya Farfaɗo Da Mafarkin Nijeriya A Wasan Rwanda

Spence Na Dab Da Kafa Tarihin Zama Musulmi Na Farko Da Zai Buga Wa Ingila Ƙwallo

A ranar 8 ga watan Agustan shekara ta 2016, Manchester United ta kammala daukar Paul Pogba kan fam miliyan 89 kuma dan kwallon tawagar Faransan ya sanar cewar ”lokaci ne ya yi da ya sake komawa kungiyar da ta dace da shi da salon wasansa.

Dan wasa Pogba ya koma kungiyar yana da shekara 23 a lokacin, bayan shekara hudu da ya bar kungiyar zuwa Jubentus kan fam miliyan 1.2 a 2012.

Sannan kudin da aka sayi Pogba ya haura fam miliyan 85 da Real Madrid ta dauki Gareth Bale a shekarar 2013 a matakin mafi tsada a duniya.

Pogba shi ne dan wasa na hudu da Jose Mourinho ya dauka a lokacin, bayan dan wasan tawagar Ibory Coast, Eric Bailly da dan wasan Sweden, Zlatan Ibrahimobic da dan wasan Armenia, Henrikh Mkhitaryan.

Karon farko bayan shekara 20 da wata kungiya a Ingila ta sayi dan wasa a matakin mafi tsada a duniya tun bayan da Newcastle United ta biya fam miliyan 15 kudin Alan Shearer daga Blackburn Robers.

Pogba ya fara zuwa Manchester United daga Le Habre a shekarar 2009 a matakin mai shekara 16, sai dai wasa bakwai kadai ya yi wa kungiyar, sannan ya tafi zuwa Jubentus a 2012, bayan da kwantiraginsa ya kare.

Dan wasan ya yi wasanni 178 a Jubentus da cin kwallo 34 da lashe Champions League a kungiyar ta Italiya a 2015.

Sai kuma ranar 12 ga watan Agustan shekara ta 2021, dan wasa Romelu Lukaku ya sake komawa Chelsea daga Inter Milan kan fam miliyan 97.5 kuma dan wasan mai shekara 28 a lokacin da dan kwallon kasar Belgium ya sake komawa Chelsea kan yarjejeniyar kakar wasa biyar, bayan da ya koma Eberton daga kungiyar kan fam miliyan 28 a 2014.

Kadan ya rage kudin da aka sayo Lukaku ya kai iri daya da wanda Manchester City ta dauki Jack Grealish daga Aston Billa kan fam miliyan 100 sannan Lukaku shi ne mafi tsada da wata kungiya a Italiya ta sayar, tun farko ya zama na uku mafi tsada da aka dauka a Italiya a 2019 da Inter Milan ta saya daga Manchester United kan fam miliyan 74.

Tun farko kungiyar Chelsea ta bai wa Eberton aron Lukaku a shekarar 2013, daga baya ta sayar mata da shi a Yulin 2014 kan fam miliyan 24 a matakin dan wasan da ta saya da tsada a tarihin Eberton.

Har ila yau a ranar 5 ga watan Agustan shekara ta 2021, Manchester City ta sanar da daukar dan wasa Jack Grealish kan yarjejeniyar kakar wasa shida da za ta kare zuwa shekarar 2027 sannan Manchester City ta sayi Grealish daga Aston Billa kan fam miliyan 100.

Dan wasan mai shekara 25 ya karbi riga mai lamba 10, wadda Sergio Aguero ya yi amfani da ita a kungiyar, sannan kudin da Manchester City ta sayi dan kwallon ya haura fam miliyan 89 da Manchester United ta dauki Paul Pogba daga Jubentus a 2016.

Bugu da kari kwana bakwai tsakani da Manchester City ta sayi Grealish, Chelsea ta sake daukar Lukaku daga Inter Milan kan fam miliyan 97.5 wanda hakan ne ya sa Grealish kan gaba a matakin wanda aka dauka mafi tsada a tarihin gasar Premier Legue kuma Lukaku ne na biyu, sai Pogba na uku, sannan Antony na hudu.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: 'Yan WasaFirimiyar IngilaKwanllon KafaManchester UnitedPogba
ShareTweetSendShare
Previous Post

Cika Shekara 20 Kan Karaga: Kyakkyawan Shugabancin Mai Martaba Sarkin Hadeja, Dakta Adamu Abubakar Maje

Next Post

Wasu ‘Yan Siyasa Na Daukar Zaben 2023 Na Ko A Mutu, Ko A Yi Rai –INEC

Related

Neman Gurbin Kofin Duniya: Arokodare Ya Farfaɗo Da Mafarkin Nijeriya A Wasan Rwanda
Wasanni

Neman Gurbin Kofin Duniya: Arokodare Ya Farfaɗo Da Mafarkin Nijeriya A Wasan Rwanda

5 hours ago
Spence Na Dab Da Kafa Tarihin Zama Musulmi Na Farko Da Zai Buga Wa Ingila Ƙwallo
Wasanni

Spence Na Dab Da Kafa Tarihin Zama Musulmi Na Farko Da Zai Buga Wa Ingila Ƙwallo

2 days ago
Lookman
Wasanni

Kofin Duniya: Lookman Da Dessers Sun Isa Sansanin Super Eagles A Uyo

3 days ago
Tottenham Ta Dauki Aron Kolo Muani Daga PSG
Wasanni

Tottenham Ta Dauki Aron Kolo Muani Daga PSG

5 days ago
Isak Na Dab Da Zama Ɗan Wasa Mafi Tsada A Tarihin Firimiya
Wasanni

Isak Na Dab Da Zama Ɗan Wasa Mafi Tsada A Tarihin Firimiya

6 days ago
Yadda Kungiyoyin Firimiyar Ingila Suka Shirya Wa Kakar Bana
Wasanni

Yadda Kungiyoyin Firimiyar Ingila Suka Shirya Wa Kakar Bana

7 days ago
Next Post
Wasu ‘Yan Siyasa Na Daukar Zaben 2023 Na Ko A Mutu, Ko A Yi Rai –INEC

Wasu ‘Yan Siyasa Na Daukar Zaben 2023 Na Ko A Mutu, Ko A Yi Rai –INEC

LABARAI MASU NASABA

Kuri’ar Jin Ra’ayoyi Ta CGTN: Sake Maido Da Ma’aikatar Yaki A Amurka Ya Nuna Babu Dakatawa A Yaki Hatta A Wajen Sa Suna 

Kuri’ar Jin Ra’ayoyi Ta CGTN: Sake Maido Da Ma’aikatar Yaki A Amurka Ya Nuna Babu Dakatawa A Yaki Hatta A Wajen Sa Suna 

September 6, 2025
Rikicin NNPP A Kano: Wani Tsagi Ya Soki Korar Abdulmumini Jibrin Kofa

Rikicin NNPP A Kano: Wani Tsagi Ya Soki Korar Abdulmumini Jibrin Kofa

September 6, 2025
Koyo Daga Tarihi Da Kiyaye Zaman Lafiya Za Su Sa Kaimi Ga Zamanantar Da Duk Duniya Baki Daya

Koyo Daga Tarihi Da Kiyaye Zaman Lafiya Za Su Sa Kaimi Ga Zamanantar Da Duk Duniya Baki Daya

September 6, 2025
Neman Gurbin Kofin Duniya: Arokodare Ya Farfaɗo Da Mafarkin Nijeriya A Wasan Rwanda

Neman Gurbin Kofin Duniya: Arokodare Ya Farfaɗo Da Mafarkin Nijeriya A Wasan Rwanda

September 6, 2025
Babban Taron MDD Ya Zartas Da Kudurin Hadin Gwiwar MDD Da SCO

Babban Taron MDD Ya Zartas Da Kudurin Hadin Gwiwar MDD Da SCO

September 6, 2025
Dorad Da Zuba Jari A Sashen Bincike Da Samarwa Da Kare Ikon Mallaka Sun Taimaka Wa Sin Zama Kan Gaba A Duniya Ta Fuskar Kirkire-kirkire

Dorad Da Zuba Jari A Sashen Bincike Da Samarwa Da Kare Ikon Mallaka Sun Taimaka Wa Sin Zama Kan Gaba A Duniya Ta Fuskar Kirkire-kirkire

September 6, 2025
An Fara Biyan Ma’aikata Sabon Mafi Ƙarancin Albashin N70,000 A Borno

Boko Haram Ta Hallaka Mutane 61 A Jihar Borno

September 6, 2025
Jami’ar IMF Ta Yaba Da Kwararan Bayanan Tattalin Arziki Da Manufofin Kasafin Kudi Na Kasar Sin 

Jami’ar IMF Ta Yaba Da Kwararan Bayanan Tattalin Arziki Da Manufofin Kasafin Kudi Na Kasar Sin 

September 6, 2025
Xi Ya Mika Sakon Taya Murna Ga Zaman Kwamitin Sada Zumunta Da Zaman Lafiya Da Ci Gaba Tsakanin Sin Da Rasha

Xi Ya Mika Sakon Taya Murna Ga Zaman Kwamitin Sada Zumunta Da Zaman Lafiya Da Ci Gaba Tsakanin Sin Da Rasha

September 6, 2025
‘Yansanda Sun Fara Binciken Yadda Matasa Suka Kone Wata Mata Har Lahira A Neja

‘Yansanda Sun Fara Binciken Yadda Matasa Suka Kone Wata Mata Har Lahira A Neja

September 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.