ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Jerin ‘Yan Wasa Mafi Tsada A Firimiyar Ingila

by Abba Ibrahim Wada
4 years ago
Firimiyar Ingila

Kungiyar kwallon kafa ta Manchester United ta sanar da cimma yarjejeniyar sayan dan wasan kungiyar Ajad dan kasar Brazil, Antony, bayan ta amince za ta biya fam miliyan 80.75 da karin tsarabe-tsaraben fam miliyan 4.25.

Dan wasa Antony ya zama dan wasa na biyu da Manchester United ta dauka mai tsada bayan dan wasa Paul Pogba wanda ya kasance mafi tsada da kungiyar Old Trafford ta saya daga Jubentus kan fam miliyan 89 a shekara ta 2016.

  • Pogba Ya Ce Barayi Suna Yi Masa Barazana
  • Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Keta Ka’idojin Fitar Da Kayayyaki

Antony zai zama dan wasa na biyar da Manchester United ta dauka a bana, bayan dan wasa Lisandro Martinez da Casemiro da Tyrell Malacia da kuma Christian Eriksen wanda kwantiraginsa ya kare a Brentford kuma Antony ya taka rawar gani a Ajad da cin kwallo 47 a dukkan fafatawar da ya yi mata kaka biyu.

ADVERTISEMENT

Dan wasan ya nuna kwarewarsa karkashin kociyan kungiyar na yanzu, Erik ten Hag a Ajad, kuma shi ne kocin ya dauke shi zuwa Manchester United saboda ya san irin salon buga wasansa a baya.

Dan wasan mai shekara 22 a duniya ya zama dan wasa na hudu da aka saya a Premier League da tsada, bayan Paul Pogba da ya koma Manchester United, sai Chelsea da ta dauki Romelu Lukaku da kuma Jack Grealish da Manchester City’ ta dauka.

LABARAI MASU NASABA

Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

Lionel Messi Ya Kafa Tarihin Wanda Yafi Kowa Zura Kwallaye A Tarihin Gasar Cin Kofin Duniya

A ranar 8 ga watan Agustan shekara ta 2016, Manchester United ta kammala daukar Paul Pogba kan fam miliyan 89 kuma dan kwallon tawagar Faransan ya sanar cewar ”lokaci ne ya yi da ya sake komawa kungiyar da ta dace da shi da salon wasansa.

Dan wasa Pogba ya koma kungiyar yana da shekara 23 a lokacin, bayan shekara hudu da ya bar kungiyar zuwa Jubentus kan fam miliyan 1.2 a 2012.

Sannan kudin da aka sayi Pogba ya haura fam miliyan 85 da Real Madrid ta dauki Gareth Bale a shekarar 2013 a matakin mafi tsada a duniya.

Pogba shi ne dan wasa na hudu da Jose Mourinho ya dauka a lokacin, bayan dan wasan tawagar Ibory Coast, Eric Bailly da dan wasan Sweden, Zlatan Ibrahimobic da dan wasan Armenia, Henrikh Mkhitaryan.

Karon farko bayan shekara 20 da wata kungiya a Ingila ta sayi dan wasa a matakin mafi tsada a duniya tun bayan da Newcastle United ta biya fam miliyan 15 kudin Alan Shearer daga Blackburn Robers.

Pogba ya fara zuwa Manchester United daga Le Habre a shekarar 2009 a matakin mai shekara 16, sai dai wasa bakwai kadai ya yi wa kungiyar, sannan ya tafi zuwa Jubentus a 2012, bayan da kwantiraginsa ya kare.

Dan wasan ya yi wasanni 178 a Jubentus da cin kwallo 34 da lashe Champions League a kungiyar ta Italiya a 2015.

Sai kuma ranar 12 ga watan Agustan shekara ta 2021, dan wasa Romelu Lukaku ya sake komawa Chelsea daga Inter Milan kan fam miliyan 97.5 kuma dan wasan mai shekara 28 a lokacin da dan kwallon kasar Belgium ya sake komawa Chelsea kan yarjejeniyar kakar wasa biyar, bayan da ya koma Eberton daga kungiyar kan fam miliyan 28 a 2014.

Kadan ya rage kudin da aka sayo Lukaku ya kai iri daya da wanda Manchester City ta dauki Jack Grealish daga Aston Billa kan fam miliyan 100 sannan Lukaku shi ne mafi tsada da wata kungiya a Italiya ta sayar, tun farko ya zama na uku mafi tsada da aka dauka a Italiya a 2019 da Inter Milan ta saya daga Manchester United kan fam miliyan 74.

Tun farko kungiyar Chelsea ta bai wa Eberton aron Lukaku a shekarar 2013, daga baya ta sayar mata da shi a Yulin 2014 kan fam miliyan 24 a matakin dan wasan da ta saya da tsada a tarihin Eberton.

Har ila yau a ranar 5 ga watan Agustan shekara ta 2021, Manchester City ta sanar da daukar dan wasa Jack Grealish kan yarjejeniyar kakar wasa shida da za ta kare zuwa shekarar 2027 sannan Manchester City ta sayi Grealish daga Aston Billa kan fam miliyan 100.

Dan wasan mai shekara 25 ya karbi riga mai lamba 10, wadda Sergio Aguero ya yi amfani da ita a kungiyar, sannan kudin da Manchester City ta sayi dan kwallon ya haura fam miliyan 89 da Manchester United ta dauki Paul Pogba daga Jubentus a 2016.

Bugu da kari kwana bakwai tsakani da Manchester City ta sayi Grealish, Chelsea ta sake daukar Lukaku daga Inter Milan kan fam miliyan 97.5 wanda hakan ne ya sa Grealish kan gaba a matakin wanda aka dauka mafi tsada a tarihin gasar Premier Legue kuma Lukaku ne na biyu, sai Pogba na uku, sannan Antony na hudu.

Firimiyar Ingila
Abba Ibrahim Wada
+ postsBio
  • Abba Ibrahim Wada
    https://hausa.leadership.ng/author/abba-ibrahim-wada/
    Har Yanzu Nijeriya Tana Fatan Zuwa Kofin Duniya Na 2026
  • Abba Ibrahim Wada
    https://hausa.leadership.ng/author/abba-ibrahim-wada/
    Mece Ce Matsalar Real Madrid? 
  • Abba Ibrahim Wada
    https://hausa.leadership.ng/author/abba-ibrahim-wada/
    Waye Zai Lashe Ƙyautar Gwarzon Ɗan Wasan Afrika Na 2025?
  • Abba Ibrahim Wada
    https://hausa.leadership.ng/author/abba-ibrahim-wada/
    Ko Ka San Dalilin Da Zai Bai Wa Nijeriya Damar Zuwa Gasar Cin Kofin Duniya?

MASU ALAKA

Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino
Wasanni

Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

June 24, 2026
Lionel Messi Ya Kafa Tarihin Wanda Yafi Kowa Zura Kwallaye A Tarihin Gasar Cin Kofin Duniya
Wasanni

Lionel Messi Ya Kafa Tarihin Wanda Yafi Kowa Zura Kwallaye A Tarihin Gasar Cin Kofin Duniya

June 22, 2026
Ɗanwasa Thomas Partey Ya Yi Rashin Nasara A Kotun Canada
Wasanni

Ɗanwasa Thomas Partey Ya Yi Rashin Nasara A Kotun Canada

June 21, 2026
Next Post
Wasu ‘Yan Siyasa Na Daukar Zaben 2023 Na Ko A Mutu, Ko A Yi Rai –INEC

Wasu ‘Yan Siyasa Na Daukar Zaben 2023 Na Ko A Mutu, Ko A Yi Rai –INEC

LABARAI MASU NASABA

Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa’ — Atiku

June 25, 2026
Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.