• English
  • Business News
Sunday, September 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Jihar Kebbi Ta Yi Babbar Nasara A Aikin Hajjin Bana – Alhaji Faruk Yaro

by Bello Hamza
1 year ago
in Labarai
0
Jihar Kebbi Ta Yi Babbar Nasara A Aikin Hajjin Bana – Alhaji Faruk Yaro
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A yayin da aka kammala aikin hajjin bana a wannan makon, Shugaban Hukumar Alhazai ta Jihar Kebbi, Alhaji Faruk Yara, Jagaban Gwandu ya bayyana cewa, goyon baya da tallafin da suka samu daga gwamnan jihar, Dakta Nasiru ne ya taimaka musu samun nasarar da suke alfahari da ita.

Faruk ya kuma ce gwamnan ya taimaka musu wajen rashin fuskantar manyan matsaloli tun daga gida Nijeriya har zuwa kasa mai tsarki, gashi kuma cikin ikon Allah an kammala aikin hajji cikin nasara.

  • Hajjin 2024: Wani Alhaji Dan Nijeriya Daga Jihar Kebbi Ya Rasu A Makkah
  • Hajjin Bana: Shettima Zai Kaddamar Da Jirgin Farko Na Maniyyata 430 A Kebbi

Alhaji Faruk ya bayyana haka ne a tattaunawarsa da manema labarai a garin Makkah ranar Laraba. Ya ce, tun da farko sai da Gwamnan ya cika wa kowanne Alhajin jihar Naira Miliyan 1 na kudin ka’ida na aikin hajji lokacin da dala ta yi tashin gwauron zabi, naira kuma ta fadi warwas.

“Gwamnan ya umarci a dinka wa Hajiyoyinmu yunifam kala biyu su kuma maza aka inganta nasu domin su ji dadin zirga-zirga, wani abin shawa’awa kuma shi ne hatta gwamnan shi ma da yunifam din ya shiga kasa mai tsarki da shi kuma ya yi zirga-zirga cikin garin Makkah.

Haka kuma ba mu fuskanci matsala ba a wajen ciyarwa kamar yadda wasu jihohi suka fuskanta, saboda gwamnanmu ya ba mu izinin samar wa da Alhazanmu karin tsarin samar da ingantaccen abinci duk kuwa da wanda NAHCON ta samar a mastayin shirin kota-kwana. Haka kuma a bangaren hadaya, gwamnan ya biya wa dukkan alhazan Kebbi kudin dabbobin da suka yi hadaya da su, wannan kuma wata hadaka ce na kananan hukumomin jihar da iyalan gwamnan.

Labarai Masu Nasaba

Yin Ƙidaya Na Da Muhimmanci Ga Ci Gaban Al’umma – Kwamishina Sa’adatu

Gwamnati Ta Kaddamar Da Sabbin Darussan Karatu A Makarantun Nijeriya

Faruq ya bayyana cewa, a halin yanzu suna nazarin tsare-tsare da hukumar Alhazai ta kasa NAHCON ta fito da shi inda daga nan ne za su fito da nasu tsarin tare da inganta shi domin samun cikakkiyar nasara a dawainiyar aikin hajjin shekara mai zuwa.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Aikin Hajjin 2024HajjiHajjin BanaKebbi
ShareTweetSendShare
Previous Post

Dalilin Da Yasa Muke Kwace Kaddarorin Manyan Dillalan Kwaya – Buba Marwa

Next Post

ASUU Ta Bada Wa’adin Mako 3 Ga Gwamnatin Tarayya, Ta Yi Barazanar Shiga Sabon Yajin aiki

Related

Yin Ƙidaya Na Da Muhimmanci Ga Ci Gaban Al’umma – Kwamishina Sa’adatu
Labarai

Yin Ƙidaya Na Da Muhimmanci Ga Ci Gaban Al’umma – Kwamishina Sa’adatu

2 minutes ago
Gwamnati Ta Kaddamar Da Sabbin Darussan Karatu A Makarantun Nijeriya
Labarai

Gwamnati Ta Kaddamar Da Sabbin Darussan Karatu A Makarantun Nijeriya

2 hours ago
Zulum Ya Tabbatar Da Harin Boko Haram Ya Ci Rayukan Mutane 63 
Labarai

Zulum Ya Tabbatar Da Harin Boko Haram Ya Ci Rayukan Mutane 63 

3 hours ago
Mun Tara Kuɗi Sama Da Naira Miliyan 170 Na Fatun Layya – Sheikh Bala Lau 
Manyan Labarai

Mun Tara Kuɗi Sama Da Naira Miliyan 170 Na Fatun Layya – Sheikh Bala Lau 

4 hours ago
An Fara Biyan Ma’aikata Sabon Mafi Ƙarancin Albashin N70,000 A Borno
Manyan Labarai

Boko Haram Ta Hallaka Mutane 61 A Jihar Borno

16 hours ago
‘Yansanda Sun Fara Binciken Yadda Matasa Suka Kone Wata Mata Har Lahira A Neja
Tsaro

‘Yansanda Sun Fara Binciken Yadda Matasa Suka Kone Wata Mata Har Lahira A Neja

19 hours ago
Next Post
ASUU Ta Bada Wa’adin Mako 3 Ga Gwamnatin Tarayya, Ta Yi Barazanar Shiga Sabon Yajin aiki

ASUU Ta Bada Wa'adin Mako 3 Ga Gwamnatin Tarayya, Ta Yi Barazanar Shiga Sabon Yajin aiki

LABARAI MASU NASABA

Yin Ƙidaya Na Da Muhimmanci Ga Ci Gaban Al’umma – Kwamishina Sa’adatu

Yin Ƙidaya Na Da Muhimmanci Ga Ci Gaban Al’umma – Kwamishina Sa’adatu

September 7, 2025
ASUU

Malaman Jami’o’i Sun Zama Abin Tausayi —Kungiyar ASUU

September 7, 2025
Gwamnati Ta Kaddamar Da Sabbin Darussan Karatu A Makarantun Nijeriya

Gwamnati Ta Kaddamar Da Sabbin Darussan Karatu A Makarantun Nijeriya

September 7, 2025
Zulum Ya Tabbatar Da Harin Boko Haram Ya Ci Rayukan Mutane 63 

Zulum Ya Tabbatar Da Harin Boko Haram Ya Ci Rayukan Mutane 63 

September 7, 2025
Mun Tara Kuɗi Sama Da Naira Miliyan 170 Na Fatun Layya – Sheikh Bala Lau 

Mun Tara Kuɗi Sama Da Naira Miliyan 170 Na Fatun Layya – Sheikh Bala Lau 

September 7, 2025
Fyade

Matsalar Ciwon Kwakwalwa A Gidajen Yarin Kasar Nan

September 7, 2025
Kuri’ar Jin Ra’ayoyi Ta CGTN: Sake Maido Da Ma’aikatar Yaki A Amurka Ya Nuna Babu Dakatawa A Yaki Hatta A Wajen Sa Suna 

Kuri’ar Jin Ra’ayoyi Ta CGTN: Sake Maido Da Ma’aikatar Yaki A Amurka Ya Nuna Babu Dakatawa A Yaki Hatta A Wajen Sa Suna 

September 6, 2025
Rikicin NNPP A Kano: Wani Tsagi Ya Soki Korar Abdulmumini Jibrin Kofa

Rikicin NNPP A Kano: Wani Tsagi Ya Soki Korar Abdulmumini Jibrin Kofa

September 6, 2025
Koyo Daga Tarihi Da Kiyaye Zaman Lafiya Za Su Sa Kaimi Ga Zamanantar Da Duk Duniya Baki Daya

Koyo Daga Tarihi Da Kiyaye Zaman Lafiya Za Su Sa Kaimi Ga Zamanantar Da Duk Duniya Baki Daya

September 6, 2025
Neman Gurbin Kofin Duniya: Arokodare Ya Farfaɗo Da Mafarkin Nijeriya A Wasan Rwanda

Neman Gurbin Kofin Duniya: Arokodare Ya Farfaɗo Da Mafarkin Nijeriya A Wasan Rwanda

September 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.