ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Tuesday, July 14, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Hajjin Bana: Shettima Zai Kaddamar Da Jirgin Farko Na Maniyyata 430 A Kebbi

by Umar Faruk
2 years ago
Hajjin Bana

Mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima ya isa filin jirgin saman Sir Ahmadu Bello na Jihar Kebbi, domin kaddamar da jirgin farko na aikin hajjin 2024.

Maniyyata 430 ne dai aka shirya yin jigilar su ta farko zuwa kasar Saudiyya.

  • Emefiele Ya Ki Amincewa Da Tuhumar Da Ake Masa A Kotu
  • An Kashe Kasurgumin Dan Bindiga Modi Da Yaransa 4 A Katsina

Haka Kuma jimillar maniyyata 65,500 da suka yi rajista a fadin kasar nan da hukumar jin dadin alhazai da kuma masu gudanar da yawon bude ido da ake sa ran za su yi aikin hajjin bana.

ADVERTISEMENT

A yayin da Shettima ya sauka a filin jirgin sama na Sir Ahmadu Bello da ke Birnin Kebbi ya samu tarba daga Gwamna Nasir Idris na jihar da Mai Alfarma Sarkin Musulmi Alhaji Sa’ad Abubakar III da Shugaban Hukumar Alhazai ta Kasa (NAHCON), Malam Jalal Arabi.

Sauran sun hada da Sanata Ali Ndume, tsohon Gwamna Sa’idu Dakingari na Kebbi, wanda shi ne Amirul Hajji na jihar, Sanata Abubakar Sani, Sanata Bala Ibn Na’Allah, Ministan Ilimi, Alhaji Yusuf Sununu da dai sauransu.

LABARAI MASU NASABA

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

Tuni dai kamfanin Flynas na kasar Saudiyya da aka tanada, kuma daya daga cikin jiragen sama guda uku da aka zaba domin gudanar da jigilar alhazai na 2024, ya kasance a filin jirgin saman, yana shirin fara jigilar maniyyatan.

Arabi, ya sauka ne domin duba jirgin tare da Kwamishinonin dindindin guda uku da Kwamishinansa da ke wakiltar Arewa maso Yamma.

Haka kuma a cikin tawagar akwai ‘yan kadan daga cikin ma’aikatan hukumar NAHCON.

Tawagar FlyNas a wajen ziyarar ta samu jagorancin Malam Umar Kaila, wakilin FlyNas a Nijeriya.

Arabi, ya shawarci masu kula da filin jirgin da su samar da karin matakalar hawa zuwa kofar bayan jirgin domin saukaka shiga cikin gaggawa.

Jirgin na flynas, jirgin zamani mai dauke da kujeru 436, an shirya zai tashi daga filin jirgin ne tsakanin karfe 12 na dare zuwa 1 na rana.

Jirage uku ne aka shirya tashi daga Nijeriya zuwa Saudiyya a ranar Laraba, Air Peace zai tashi daga Abuja tare da alhazan birnin tarayya 310 da jami’ai biyar.

Hajjin Bana
Umar Faruk
+ postsBio
  • Umar Faruk
    https://hausa.leadership.ng/author/umar-faruk-2/
    Nijeriya Da Jamhuriyar Benin Za Su Sassauta Tsanantawa A Kan Iyakokinsu Ga ‘Yan Kasuwa
  • Umar Faruk
    https://hausa.leadership.ng/author/umar-faruk-2/
    Jami’an Tsaro sun Ceto Mata Biyu da aka Yi Garkuwa da Su A Kebbi
  • Umar Faruk
    https://hausa.leadership.ng/author/umar-faruk-2/
    Majalisar Dokokin Kebbi Ta Dakatar Da Dan Majalisa Mai Wakiltar Birnin Kebbi Ta Arewa
  • Umar Faruk
    https://hausa.leadership.ng/author/umar-faruk-2/
    Sakon Sallah: Gwamna Nasir Ya Yi Kira Da Hadin Kai Don Gina Jihar Kebbi

MASU ALAKA

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu
Labarai

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga
Manyan Labarai

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi
Labarai

Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

July 14, 2026
Next Post
Hajjin Bana: Saudiyya Ta Kaddamar Da Kundayen Wayar Da Kai Ga Mahajjata Cikin Harsuna 16 Har Da Hausa

Hajjin Bana: Saudiyya Ta Kaddamar Da Kundayen Wayar Da Kai Ga Mahajjata Cikin Harsuna 16 Har Da Hausa

LABARAI MASU NASABA

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

July 14, 2026
Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

July 14, 2026
Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

July 14, 2026
CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

July 14, 2026
Tsohon Sanatan Gombe, Bayero Nafada, Ya Fice Daga PDP Bayan Ganawa da Shugabannin APC

Tsohon Sanatan Gombe, Bayero Nafada, Ya Fice Daga PDP Bayan Ganawa da Shugabannin APC

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.